< Ezekiyel 27 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
2 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin Taya.
Toi donc, fils d’un homme, fais entendre sur Tyr des lamentations;
3 Ka ce wa Taya, wadda take zaune a hanyar shiga zuwa teku, kasuwar masu yawa mutane a bakin teku, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kin ce, ya Taya, “Ni kyakkyawa ce cikakkiya.”
Et tu diras à Tyr, qui habite à l’entrée de la mer, au siège du commerce des peuples pour des îles nombreuses: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Ô Tyr, tu as dit, je suis d’une parfaite beauté,
4 Manyan tekuna ne wurin zamanki; maginanki sun sa kyanki ya zama cikakke.
Et située au milieu de la mer.: Tes voisins qui t’ont bâtie ont mis le comble à ta beauté,
5 Sun yi dukan katakanki daga itatuwan fir daga Senir; sun kwaso itatuwan al’ul daga Lebanon don su yi miki jigon jirgin ruwa.
C’est avec les sapins du Sanir qu’ils t’ont construite ainsi que tous tes étages qui plongent dans la mer; ils ont pris un cèdre du Liban pour te faire un mât.
6 Da oak daga Bashan suka yi sandunan tuƙan jirgin ruwa da itatuwan kasharina daga bakin tekun Saifurus suka yi daɓe jirgin ruwanki, suka kuma manne masa hauren giwa.
Ils ont poli des chênes de Basan pour tes rames; et ils ont fait tes bancs avec l’ivoire des Indes, et les prétorioles avec le bois des îles d’Italie.
7 Lilin mai kyau mai ado daga Masar ne filafilan jirgin ruwanki suka kuma zama tutarki; an yi tutarki da shuɗi da shunayya daga bakin tekun Elisha.
Le byssus varié d’Egypte a été tissu en forme de voile pour être mis sur ton mât; l’hyacinthe et la pourpre des îles d’Elisa sont devenues ta couverture.
8 Mutanen Sidon da Arfad su ne matuƙan jirgin ruwanki; gwanayenki, ya Taya, suna ciki a matsayi matuƙan jiragen ruwa.
Les habitants de Sidon et d’Arad ont été tes rameurs; tes sages, ô Tyr, sont devenus tes pilotes.
9 Masu hikima na Gebal suna ciki a matsayin masu tattoshe mahaɗan katakon jirginki. Dukan jiragen ruwa da matuƙansu sukan zo wurinki don kasuwanci.
Les vieillards de Gébal et ses hommes habiles ont eu des nautoniers pour le service de tout ton équipage; tous les vaisseaux de la mer et leurs nautoniers ont été engagés dans ton commerce.
10 “‘Mutanen Farisa, Lidiya da Fut su ne suka zama sojoji a cikin mayaƙanki. Sun rataye garkuwoyinsu da hulunan kwano a katangarki, suna kawo miki daraja.
Les Perses, et les Lydiens, et les Lybiens étaient dans ton armée, tes hommes de guerre; ils ont suspendu chez toi la cuirasse et le bouclier pour ton ornement.
11 Mutanen Arfad da Helek sun yi tsaron katangar a kowace gefe; mutanen Gammad su ne a hasumiyoyinki. Sun rataye garkuwoyinsu kewaye da katangarki; sun sa kyanki ya zama cikakke.
Les fils d’Arad, et ton armée, étaient sur tes murs tout autour; et aussi les Pygmées qui étaient sur tes tours ont suspendu leurs carquois à tes murs tout autour; ils ont mis eux-mêmes le comble à ta beauté.
12 “‘Tarshish ta yi ciniki da ke saboda yawan wadatar kayayyakinki; sun sayi kayan cinikinki da azurfa, ƙarfe, kuza da dalma.
Les Carthaginois qui négociaient avec toi par l’abondance de toutes les richesses, ont rempli tes foires d’argent, de fer, d’étain, et de plomb.
13 “‘Girka, Tubal da Meshek sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki suka biya da bayi da kuma abubuwan da aka yi da tagulla.
La Grèce, Thubal et Mosoch étaient tes courtiers; ils ont amené des esclaves et des vases d’airain à ton peuple.
14 “‘Mutanen Bet Togarma sun sayi kayan cinikinki da dawakai, dawakan yaƙi da alfadarai.
De la maison de Thogorma on amenait des chevaux, des cavaliers et des mulets à ton marché.
15 “‘Mutanen Dedan sun yi kasuwanci da ke, bakin teku masu yawa abokan cinikinki ne; sun biya ki da hauren giwa da katakon kanya.
Les fils de Dédan ont négocié avec toi; beaucoup d’îles ont négocié par tes mains; elles t’ont donné des dents d’ivoire et de l’ébène en échange de tes marchandises.
16 “‘Mutanen Aram sun yi ciniki da ke saboda yawan kayanki; suka sayi kayan cinikinki da zumurrudu, da shunayya, da kayan ado, da lilin mai taushi, da murjani, da yakutu.
Le Syrien qui négociait avec toi à cause de la multitude de tes ouvrages, a exposé dans ton marché des pierreries et de la pourpre, et des vêtements de tricot, et du byssus, et de la soie, et du chodchod.
17 “‘Yahuda da Isra’ila sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki da alkama da Minnit da alawa, da zuma, da mai, da ganyaye masu ƙanshi.
Juda et la terre d’Israël étaient aussi tes courtiers; ils ont exposé dans tes foires du froment de première qualité, du baume, du miel, de l’huile et de la résine.
18 “‘Mutanen Damaskus sun ga abin da za ki iya bayarwa sai suka yi ciniki da ke, ta sayi kayanki da ruwan inabi daga Helbon, da ulu daga Zahar.
Damas, qui négociait avec toi, te donnait pour la multitude de tes ouvrages une multitude de différentes richesses, du vin généreux, des laines de la couleur la plus belle.
19 Wedan da Yaban kusa da Uzal, suka sayi kayanki; wato gyararren ƙarfe da kayan yaji.
Dan, et la Grèce et Mosel dans tes foires ont exposé du fer travaillé; il y avait du stacté et de la canne dans ton commerce.
20 “‘Mutanen Dedan sun sayi kayanki da sirdin zama a kan dawakai.
Dédan était ton courtier pour les tapis à s’asseoir.
21 “‘Mutanen Arabiya da dukan sarakunan Kedar abokan cinikinki ne; sun yi ciniki da ke suka sayi kayanki da’yan raguna, da raguna, da awaki.
L’Arabie et tous les princes de Cédar ont négocié par tes mains; avec des agneaux, et des béliers, et des boucs, ils sont venus vers toi étant en commerce avec toi.
22 “‘’Yan kasuwan Sheba da Ra’ama sun yi ciniki da ke; suka sayi kayanki da kayan yaji mafi kyau iri-iri, da duwatsu masu daraja iri-iri, da zinariya.
Les marchands de Saba et de Réema eux-mêmes ont négocié avec toi en toutes sortes d’excellents aromates, en pierres précieuses, et en or qu’ils ont exposé dans ton marché.
23 “‘Haran, Kanne da Eden da kuma’yan kasuwan Sheba, Assuriya da Kilmad sun yi ciniki da ke.
Haran, et Chené, et Eden ont négocié avec toi; Saba, Assur et Chelmad t’ont vendu leurs marchandises.
24 A kasuwarki sun yi ciniki da ke suka sayar miki tufafi masu tsada, da na shuɗi, da masu ado, da dardumai masu ƙyalƙyali da kirtani, da igiyoyi waɗanda aka tuƙa da kyau.
Eux aussi trafiquaient avec toi de bien des manières pour des balles d’hyacinthe, de tissus de diverses couleurs et de trésors précieux qui étaient enveloppés et attachés avec des cordes; ils avaient encore des cèdres dans leurs trafics avec toi.
25 “‘Jiragen ruwan Tarshish sun zama masu jigilar kayanki. Kin cika da kaya masu nauyi a tsakiyar teku.
Les vaisseaux de la mer étaient tes princes dans ton commerce; tu as été comblée de richesses et extrêmement glorifiée au milieu de la mer.
26 Matuƙan jiragenki sun kai ki can cikin manyan tekuna. Amma iskar gabas za tă farfasa ki kucu-kucu a tsakiyar teku.
Tes rameurs t’ont conduite sur les grandes eaux; mais le vent du midi t’a brisée au fond de la mer.
27 Dukiyarki, cinikinki da kayan kasuwarki, ma’aikatanki na jirgi, matuƙan jiragenki da masu tattoshe mahaɗan katakan jiragenki,’yan kasuwarki da dukan sojojinki, da kuma kowa da yake cikin jirgi zai nutsa a tsakiyar teku a ranar da jirginki zai nutse.
Tes richesses, et tes trésors, et ton nombreux équipage, tes nautoniers, tes pilotes qui avaient en garde les objets à ton usage et commandaient à tes gens; et aussi tous les hommes de guerre qui étaient en toi, avec toute la multitude qui se trouve au milieu de toi, tomberont au fond de la mer au jour de ta ruine.
28 Ƙasashen bakin teku za su girgiza sa’ad da matuƙan jirginki suka yi kuka.
Au bruit de la clameur de tes pilotes, les flots seront troublés;
29 Dukan waɗanda suke riƙe da matuƙi za su ƙyale jiragensu; ma’aikatan jirage da dukan matuƙan jirage za su tsaya a bakin teku.
Et ils descendront de leurs vaisseaux, tous ceux qui tenaient la rame; les nautoniers et tous les pilotes de la mer se tiendront sur la terre.
30 Za su tā da muryarsu su yi kuka mai zafi a kanki; za su yayyafa ƙura a kawunansu, su yi ta birgima a cikin toka.
Ils se lamenteront sur toi à haute voix, et pousseront des cris amers; et ils jetteront de la poussière sur leurs têtes et se couvriront de cendre.
31 Za su aske kawunansu saboda ke za su kuma sa tufafin makoki. Za su yi kuka dominki su yi ɓacin rai da kuma kuka mai zafi.
Et ils raseront à cause de toi leur chevelure et se ceindront de cilices; et ils te pleureront dans l’amertume de l’âme d’un pleur très amer.
32 Yayinda suke kuka a kanki kuwa, za su yi makoki dominki suna cewa, “Wa ya taɓa yin shiru kamar Taya, kewaye da teku?”
Et ils entonneront sur toi un chant lugubre, et se désoleront à ton sujet, disant: Quelle ville est comme Tyr, et quelle ville est devenue muette au milieu de la mer?
33 Sa’ad da kayan cinikinki suka tafi ƙasashen hayi, kin gamsar da al’ummai masu yawa; da dukiyarki masu yawa da kuma kayan cinikinki kin azurtar da sarakunan duniya.
Toi qui, en faisant sortir tes marchandises de la mer, as comblé de biens des peuples nombreux, qui, par la multitude de tes richesses et de tes peuples, as enrichi des rois de la terre;
34 Yanzu teku ta farfashe ki cikin zurfafan ruwaye; kayan cinikinki da dukan kamfaninki sun nutse tare da ke.
Maintenant tu as été brisée par la mer; tes richesses et toute la multitude qui était au milieu de toi sont tombées au profond des eaux.
35 Dukan mazaunan bakin teku sun giggice saboda masifarki; sarakunansu sun tsorata ƙwarai fuskokinsu kuwa sun yamutse don tsoro.
Tous les habitants des îles seront frappés de stupeur sur loi; et tous leurs rois battus par cette tempête ont changé de visage.
36 ’Yan kasuwa a cikin al’ummai suna yin miki tsaki; kin zo ga mummunar ƙarshe ba za ki ƙara kasancewa ba har abada.’”
Les marchands de tous les peuples ont sifflé sur toi: tu as été réduite au néant, et tu ne seras plus à jamais.