< Ezekiyel 27 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And there is a word of Jehovah unto me, saying:
2 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin Taya.
'And thou, son of man, lift up concerning Tyre a lamentation, and thou hast said to Tyre:
3 Ka ce wa Taya, wadda take zaune a hanyar shiga zuwa teku, kasuwar masu yawa mutane a bakin teku, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kin ce, ya Taya, “Ni kyakkyawa ce cikakkiya.”
O dweller on the entrances of the sea, Merchant of the peoples unto many isles, Thus said the Lord Jehovah: O Tyre, thou — thou hast said: I [am] the perfection of beauty.
4 Manyan tekuna ne wurin zamanki; maginanki sun sa kyanki ya zama cikakke.
In the heart of the seas [are] thy borders, Thy builders have perfected thy beauty.
5 Sun yi dukan katakanki daga itatuwan fir daga Senir; sun kwaso itatuwan al’ul daga Lebanon don su yi miki jigon jirgin ruwa.
Of firs of Senir they have built to thee all thy double-boarded ships, Of cedars of Lebanon they have taken to make a mast for thee,
6 Da oak daga Bashan suka yi sandunan tuƙan jirgin ruwa da itatuwan kasharina daga bakin tekun Saifurus suka yi daɓe jirgin ruwanki, suka kuma manne masa hauren giwa.
Of oaks of Bashan they made thine oars, Thy bench they have made of ivory, A branch of Ashurim from isles of Chittim.
7 Lilin mai kyau mai ado daga Masar ne filafilan jirgin ruwanki suka kuma zama tutarki; an yi tutarki da shuɗi da shunayya daga bakin tekun Elisha.
Of fine linen with embroidery from Egypt hath been thy sail, To be to thee for an ensign, Of blue and purple from isles of Elishah hath been thy covering.
8 Mutanen Sidon da Arfad su ne matuƙan jirgin ruwanki; gwanayenki, ya Taya, suna ciki a matsayi matuƙan jiragen ruwa.
Inhabitants of Zidon and Arvad have been rowers to thee, Thy wise men, O Tyre, have been in thee, They [are] thy pilots.
9 Masu hikima na Gebal suna ciki a matsayin masu tattoshe mahaɗan katakon jirginki. Dukan jiragen ruwa da matuƙansu sukan zo wurinki don kasuwanci.
Elders of Gebal and its wise men have been in thee, Strengthening thy breach; All ships of the sea and their mariners, Have been in thee, to trade [with] thy merchandise.
10 “‘Mutanen Farisa, Lidiya da Fut su ne suka zama sojoji a cikin mayaƙanki. Sun rataye garkuwoyinsu da hulunan kwano a katangarki, suna kawo miki daraja.
Persian and Lud and Phut Have been in thy forces — thy men of war. Shield and helmet they hung up in thee, They — they have given out thine honour.
11 Mutanen Arfad da Helek sun yi tsaron katangar a kowace gefe; mutanen Gammad su ne a hasumiyoyinki. Sun rataye garkuwoyinsu kewaye da katangarki; sun sa kyanki ya zama cikakke.
The sons of Arvad, and thy force, [Are] on thy walls round about, And short swordsmen in thy towers have been, Their shields they have hung up on thy walls round about, They — they have perfected thy beauty.
12 “‘Tarshish ta yi ciniki da ke saboda yawan wadatar kayayyakinki; sun sayi kayan cinikinki da azurfa, ƙarfe, kuza da dalma.
Tarshish [is] thy merchant, Because of the abundance of all wealth, For silver, iron, tin, and lead, They have given out thy remnants.
13 “‘Girka, Tubal da Meshek sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki suka biya da bayi da kuma abubuwan da aka yi da tagulla.
Javan, Tubal, and Meshech — they [are] thy merchants, For persons of men, and vessels of brass, They have given out thy merchandise.
14 “‘Mutanen Bet Togarma sun sayi kayan cinikinki da dawakai, dawakan yaƙi da alfadarai.
They of the house of Togarmah, [For] horses, and riding steeds, and mules, They have given out thy remnants.
15 “‘Mutanen Dedan sun yi kasuwanci da ke, bakin teku masu yawa abokan cinikinki ne; sun biya ki da hauren giwa da katakon kanya.
Sons of Dedan [are] thy merchants, Many isles [are] the mart of thy hand, Horns of ivory and ebony they sent back thy reward.
16 “‘Mutanen Aram sun yi ciniki da ke saboda yawan kayanki; suka sayi kayan cinikinki da zumurrudu, da shunayya, da kayan ado, da lilin mai taushi, da murjani, da yakutu.
Aram [is] thy merchant, Because of the abundance of thy works, For emerald, purple, and embroidery, And fine linen, and coral, and agate, They have given out thy remnants.
17 “‘Yahuda da Isra’ila sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki da alkama da Minnit da alawa, da zuma, da mai, da ganyaye masu ƙanshi.
Judah and the land of Israel — they [are] thy merchants, For wheat of Minnith, and Pannag, And honey, and oil, and balm, They have given out thy merchandise.
18 “‘Mutanen Damaskus sun ga abin da za ki iya bayarwa sai suka yi ciniki da ke, ta sayi kayanki da ruwan inabi daga Helbon, da ulu daga Zahar.
Damascus [is] thy merchant, For the abundance of thy works, Because of the abundance of all wealth, For wine of Helbon, and white wool.
19 Wedan da Yaban kusa da Uzal, suka sayi kayanki; wato gyararren ƙarfe da kayan yaji.
Vedan and Javan go about with thy remnants, They have given shining iron, cassia, and cane, In thy merchandise it hath been.
20 “‘Mutanen Dedan sun sayi kayanki da sirdin zama a kan dawakai.
Dedan [is] thy merchant, For clothes of freedom for riding.
21 “‘Mutanen Arabiya da dukan sarakunan Kedar abokan cinikinki ne; sun yi ciniki da ke suka sayi kayanki da’yan raguna, da raguna, da awaki.
Arabia, and all princes of Kedar, They [are] the traders of thy hand, For lambs, and rams, and he-goats, In these thy merchants.
22 “‘’Yan kasuwan Sheba da Ra’ama sun yi ciniki da ke; suka sayi kayanki da kayan yaji mafi kyau iri-iri, da duwatsu masu daraja iri-iri, da zinariya.
Merchants of Sheba and Raamah — they [are] thy merchants, For the chief of all spices, And for every precious stone, and gold, They have given out thy remnants.
23 “‘Haran, Kanne da Eden da kuma’yan kasuwan Sheba, Assuriya da Kilmad sun yi ciniki da ke.
Haran, and Canneh, and Eden, merchants of Sheba, Asshur — Chilmad — [are] thy merchants,
24 A kasuwarki sun yi ciniki da ke suka sayar miki tufafi masu tsada, da na shuɗi, da masu ado, da dardumai masu ƙyalƙyali da kirtani, da igiyoyi waɗanda aka tuƙa da kyau.
They [are] thy merchants for perfect things, For wrappings of blue, and embroidery, And for treasuries of rich apparel, With cords bound and girded, for thy merchandise,
25 “‘Jiragen ruwan Tarshish sun zama masu jigilar kayanki. Kin cika da kaya masu nauyi a tsakiyar teku.
Ships of Tarshish [are] thy double walls of thy merchandise, And thou art filled and honoured greatly, In the heart of the seas.
26 Matuƙan jiragenki sun kai ki can cikin manyan tekuna. Amma iskar gabas za tă farfasa ki kucu-kucu a tsakiyar teku.
Into great waters have they brought thee, Those rowing thee, The east wind hath broken thee in the heart of the seas.
27 Dukiyarki, cinikinki da kayan kasuwarki, ma’aikatanki na jirgi, matuƙan jiragenki da masu tattoshe mahaɗan katakan jiragenki,’yan kasuwarki da dukan sojojinki, da kuma kowa da yake cikin jirgi zai nutsa a tsakiyar teku a ranar da jirginki zai nutse.
Thy wealth and thy remnants, Thy merchandise, thy mariners, And thy pilots, strengtheners of thy breach, And the traders of thy merchandise, And all thy men of war, who [are] in thee, And in all thine assembly that [is] in thy midst, Fall into the heart of the seas in the day of thy fall,
28 Ƙasashen bakin teku za su girgiza sa’ad da matuƙan jirginki suka yi kuka.
At the voice of the cry of thy pilots shake do the suburbs.
29 Dukan waɗanda suke riƙe da matuƙi za su ƙyale jiragensu; ma’aikatan jirage da dukan matuƙan jirage za su tsaya a bakin teku.
And come down from their ships have all handling an oar, Mariners, all the pilots of the sea, on the land they stand,
30 Za su tā da muryarsu su yi kuka mai zafi a kanki; za su yayyafa ƙura a kawunansu, su yi ta birgima a cikin toka.
And have sounded for thee with their voice, And cry bitterly, and cause dust to go up on their heads, In ashes they do roll themselves.
31 Za su aske kawunansu saboda ke za su kuma sa tufafin makoki. Za su yi kuka dominki su yi ɓacin rai da kuma kuka mai zafi.
And they have made for thee baldness, And they have girded on sackcloth, And they have wept for thee, In bitterness of soul — a bitter mourning.
32 Yayinda suke kuka a kanki kuwa, za su yi makoki dominki suna cewa, “Wa ya taɓa yin shiru kamar Taya, kewaye da teku?”
And lifted up for thee have their sons a lamentation, And they have lamented over thee, who [is] as Tyre? As the cut-off one in the midst of the sea?
33 Sa’ad da kayan cinikinki suka tafi ƙasashen hayi, kin gamsar da al’ummai masu yawa; da dukiyarki masu yawa da kuma kayan cinikinki kin azurtar da sarakunan duniya.
With the outgoing of thy remnants from the seas, Thou hast filled many peoples, With the abundance of thy riches, and thy merchandise, Thou hast made rich things of earth.
34 Yanzu teku ta farfashe ki cikin zurfafan ruwaye; kayan cinikinki da dukan kamfaninki sun nutse tare da ke.
The time of [thy] being broken by the seas in the depths of the waters, Thy merchandise and all thy assembly in thy midst have fallen.
35 Dukan mazaunan bakin teku sun giggice saboda masifarki; sarakunansu sun tsorata ƙwarai fuskokinsu kuwa sun yamutse don tsoro.
All inhabitants of the isles have been astonished at thee, And their kings have been sore afraid, They have been troubled in countenance.
36 ’Yan kasuwa a cikin al’ummai suna yin miki tsaki; kin zo ga mummunar ƙarshe ba za ki ƙara kasancewa ba har abada.’”
Merchants among the peoples have shrieked for thee, Wastes thou hast been, and thou art not — to the age!'

< Ezekiyel 27 >