< Ezekiyel 27 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Yahweh said this to me:
2 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin Taya.
“You human, sing a funeral song about Tyre.
3 Ka ce wa Taya, wadda take zaune a hanyar shiga zuwa teku, kasuwar masu yawa mutane a bakin teku, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kin ce, ya Taya, “Ni kyakkyawa ce cikakkiya.”
[The city of] is located [on an island] at the edge of the sea, and their merchants (traded/bought and sold goods) with people-groups [who live] along many seacoasts. This is what [I], Yahweh the Lord, say [that you should tell them]: ‘You [people of] Tyre said that your [city] was very beautiful.
4 Manyan tekuna ne wurin zamanki; maginanki sun sa kyanki ya zama cikakke.
You controlled what was bought and sold by people who lived along the sea. Those who built your [city] caused it to become very beautiful.
5 Sun yi dukan katakanki daga itatuwan fir daga Senir; sun kwaso itatuwan al’ul daga Lebanon don su yi miki jigon jirgin ruwa.
You were like [SIM] a huge ship that was built from the from pine/cypress [trees] on Hermon [Mountain]. Then they took cedar [wood] from Lebanon to make a mast for the ship.
6 Da oak daga Bashan suka yi sandunan tuƙan jirgin ruwa da itatuwan kasharina daga bakin tekun Saifurus suka yi daɓe jirgin ruwanki, suka kuma manne masa hauren giwa.
They carved your oars from oak trees from the Bashan [region]. They made the deck from cypress/pine wood from Cyprus [island], and they covered [the decks] with ivory.
7 Lilin mai kyau mai ado daga Masar ne filafilan jirgin ruwanki suka kuma zama tutarki; an yi tutarki da shuɗi da shunayya daga bakin tekun Elisha.
The sails for the ship were made from fine embroidered linen from Egypt, and those sails were like flags that people could see [far away]. For shade they [hung pieces of] blue and purple cloth [brought] from [people living on] Cyprus [island].
8 Mutanen Sidon da Arfad su ne matuƙan jirgin ruwanki; gwanayenki, ya Taya, suna ciki a matsayi matuƙan jiragen ruwa.
Men from Sidon and Arvad [cities] pulled the oars; the men who steered the boat were skilled men from Tyre.
9 Masu hikima na Gebal suna ciki a matsayin masu tattoshe mahaɗan katakon jirginki. Dukan jiragen ruwa da matuƙansu sukan zo wurinki don kasuwanci.
Experienced craftsmen from Byblos [city on the coast] (did the caulking/filled the spaces between the planks in the sides) of the ship. Sailors from many countries came in their ships to buy and sell goods there.
10 “‘Mutanen Farisa, Lidiya da Fut su ne suka zama sojoji a cikin mayaƙanki. Sun rataye garkuwoyinsu da hulunan kwano a katangarki, suna kawo miki daraja.
Men from [as far away as] Persia, Lydia, and Libya were [soldiers] in your army. They hung their shields and helmets on [the walls of] your [city], and that caused people to admire your city.
11 Mutanen Arfad da Helek sun yi tsaron katangar a kowace gefe; mutanen Gammad su ne a hasumiyoyinki. Sun rataye garkuwoyinsu kewaye da katangarki; sun sa kyanki ya zama cikakke.
Men from Arvad and Helech [cities were watchmen] on the walls [of your city]; men from Gammad [town] were in your towers. They [also] hung their shields on your walls; they also caused your [city] to be very beautiful.
12 “‘Tarshish ta yi ciniki da ke saboda yawan wadatar kayayyakinki; sun sayi kayan cinikinki da azurfa, ƙarfe, kuza da dalma.
Because of the many things that you had [to trade], men from Tarshish [in Spain] sent merchants who brought silver, iron, tin, and lead to trade for things that you had.
13 “‘Girka, Tubal da Meshek sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki suka biya da bayi da kuma abubuwan da aka yi da tagulla.
[Merchants from] Greece, Tubal, and Meshech brought slaves and things made from bronze to trade for things that you had.
14 “‘Mutanen Bet Togarma sun sayi kayan cinikinki da dawakai, dawakan yaƙi da alfadarai.
[Men from] Beth-Togarmah [in Armenia] brought work horses, war horses, and mules to trade for things that you had.
15 “‘Mutanen Dedan sun yi kasuwanci da ke, bakin teku masu yawa abokan cinikinki ne; sun biya ki da hauren giwa da katakon kanya.
Merchants came to you from Rhodes [island]. [People from] nations along the coast traded with you; they brought (ivory/elephant tusks) and [valuable black] ebony [wood] to trade for things that you had.
16 “‘Mutanen Aram sun yi ciniki da ke saboda yawan kayanki; suka sayi kayan cinikinki da zumurrudu, da shunayya, da kayan ado, da lilin mai taushi, da murjani, da yakutu.
Because you had very many things [to trade], people from Syria brought to you valuable turquoise stones, purple [cloth], embroidered [cloth], fine linen [cloth], and [jewelry made from] coral and rubies to trade for your things.
17 “‘Yahuda da Isra’ila sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki da alkama da Minnit da alawa, da zuma, da mai, da ganyaye masu ƙanshi.
Men from Judah and Israel brought wheat from Minnith [city in Ammon], and figs, honey, [olive] oil, and ointment to trade for your things.
18 “‘Mutanen Damaskus sun ga abin da za ki iya bayarwa sai suka yi ciniki da ke, ta sayi kayanki da ruwan inabi daga Helbon, da ulu daga Zahar.
Because you had very many things [to trade], men from Damascus brought wine from Helbon [town] and white wool from the Zahar [area] to trade for many things that you had.
19 Wedan da Yaban kusa da Uzal, suka sayi kayanki; wato gyararren ƙarfe da kayan yaji.
Greek men from the Uzal [area] brought things made of iron, and cassia [spice], and [fragrant] calamus [seeds] to trade for things that you had.
20 “‘Mutanen Dedan sun sayi kayanki da sirdin zama a kan dawakai.
[Merchants came from] Dedan [in southern Edom] bringing saddle blankets to trade for things that you had.
21 “‘Mutanen Arabiya da dukan sarakunan Kedar abokan cinikinki ne; sun yi ciniki da ke suka sayi kayanki da’yan raguna, da raguna, da awaki.
Men from Arabia and all the rulers of the Kedar [region] sent merchants to trade lambs and rams and male goats for things that you had.
22 “‘’Yan kasuwan Sheba da Ra’ama sun yi ciniki da ke; suka sayi kayanki da kayan yaji mafi kyau iri-iri, da duwatsu masu daraja iri-iri, da zinariya.
Merchants from Sheba and Raamah [in Arabia] brought many kinds of very good spices and jewels and gold to exchange for things that you had.
23 “‘Haran, Kanne da Eden da kuma’yan kasuwan Sheba, Assuriya da Kilmad sun yi ciniki da ke.
[Men came from] Haran, Canneh, Eden, Sheba, Asshur and Kilmad [in Mesopotamia] with their goods.
24 A kasuwarki sun yi ciniki da ke suka sayar miki tufafi masu tsada, da na shuɗi, da masu ado, da dardumai masu ƙyalƙyali da kirtani, da igiyoyi waɗanda aka tuƙa da kyau.
They brought pretty things to trade: Blue cloth, embroidered cloth, and rugs of [many] colors that were [rolled up and] tied with ropes.
25 “‘Jiragen ruwan Tarshish sun zama masu jigilar kayanki. Kin cika da kaya masu nauyi a tsakiyar teku.
Cargo ships from Tarshish carried [all] those things that you traded; and the warehouses on your island were full of all those things.’”
26 Matuƙan jiragenki sun kai ki can cikin manyan tekuna. Amma iskar gabas za tă farfasa ki kucu-kucu a tsakiyar teku.
“‘The men who row your boats took [the ships full of] cargo out on the stormy seas. But the strong east wind wrecked those cargo boats.
27 Dukiyarki, cinikinki da kayan kasuwarki, ma’aikatanki na jirgi, matuƙan jiragenki da masu tattoshe mahaɗan katakan jiragenki,’yan kasuwarki da dukan sojojinki, da kuma kowa da yake cikin jirgi zai nutsa a tsakiyar teku a ranar da jirginki zai nutse.
Everything in the boats (was lost/sank to the bottom of the sea)— all the valuable cargo [DOU] and [many of] [HYP] the sailors and ship pilots, the ship workers and merchants and soldiers. On the day that the ships were wrecked, many of those on the ships sank to the bottom of the sea.
28 Ƙasashen bakin teku za su girgiza sa’ad da matuƙan jirginki suka yi kuka.
[The people in cities along] the coast trembled when they heard your ship pilots cry out.
29 Dukan waɗanda suke riƙe da matuƙi za su ƙyale jiragensu; ma’aikatan jirage da dukan matuƙan jirage za su tsaya a bakin teku.
All the men who remained who pulled the oars left the ships; the sailors and pilots [go to the shore and] stand on the beach.
30 Za su tā da muryarsu su yi kuka mai zafi a kanki; za su yayyafa ƙura a kawunansu, su yi ta birgima a cikin toka.
They cry aloud because of [what has happened to] your [wealth], and they weep bitterly. They throw dirt on their heads and roll around in ashes.
31 Za su aske kawunansu saboda ke za su kuma sa tufafin makoki. Za su yi kuka dominki su yi ɓacin rai da kuma kuka mai zafi.
They shave their heads to show that they are very sad because of [what has happened to] you, and they put on rough sackcloth. They weep for you very bitterly and mourn for you.
32 Yayinda suke kuka a kanki kuwa, za su yi makoki dominki suna cewa, “Wa ya taɓa yin shiru kamar Taya, kewaye da teku?”
While they wail and mourn because of what has happened to you, they sing this sad funeral song: “There was certainly never [RHQ] a city like Tyre that now is silent, covered by the waves of the sea.”
33 Sa’ad da kayan cinikinki suka tafi ƙasashen hayi, kin gamsar da al’ummai masu yawa; da dukiyarki masu yawa da kuma kayan cinikinki kin azurtar da sarakunan duniya.
The goods that your merchants traded were things that pleased the people of many countries. Kings in very distant places became rich from the wealth that they obtained from trading with you.
34 Yanzu teku ta farfashe ki cikin zurfafan ruwaye; kayan cinikinki da dukan kamfaninki sun nutse tare da ke.
But now your city is like a ship [MET] that is wrecked in the sea, and everything that was in it is broken, at the bottom of the sea. All of your cargo and your sailors have sunk to the bottom of the sea along with the ships.
35 Dukan mazaunan bakin teku sun giggice saboda masifarki; sarakunansu sun tsorata ƙwarai fuskokinsu kuwa sun yamutse don tsoro.
All the people who live along the seacoast are appalled/horrified because of what has happened to you. Their kings are very horrified, [causing] their faces to be twisted [as they watch].
36 ’Yan kasuwa a cikin al’ummai suna yin miki tsaki; kin zo ga mummunar ƙarshe ba za ki ƙara kasancewa ba har abada.’”
The merchants of the [other] nations shake their heads [because it is difficult for them to believe what has happened]; your city has disappeared, and it will not exist any more.’”

< Ezekiyel 27 >