< Ezekiyel 27 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying:
2 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin Taya.
Thou therefore, O son of man, take up a lamentation for Tyre:
3 Ka ce wa Taya, wadda take zaune a hanyar shiga zuwa teku, kasuwar masu yawa mutane a bakin teku, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kin ce, ya Taya, “Ni kyakkyawa ce cikakkiya.”
And say to Tyre that dwelleth at the entry of the sea, being the mart of the people for many islands: Thus saith the Lord God: O Tyre, thou hast said: I am of perfect beauty,
4 Manyan tekuna ne wurin zamanki; maginanki sun sa kyanki ya zama cikakke.
And situate in the heart of the sea. Thy neighbours, that built thee, have perfected thy beauty:
5 Sun yi dukan katakanki daga itatuwan fir daga Senir; sun kwaso itatuwan al’ul daga Lebanon don su yi miki jigon jirgin ruwa.
With fir trees of Sanir they have built thee with all sea planks: they have taken cedars from Libanus to make thee masts.
6 Da oak daga Bashan suka yi sandunan tuƙan jirgin ruwa da itatuwan kasharina daga bakin tekun Saifurus suka yi daɓe jirgin ruwanki, suka kuma manne masa hauren giwa.
They have cut thy oars out of the oaks of Basan: and they have made thee benches of Indian ivory and cabins with things brought from the islands of Italy.
7 Lilin mai kyau mai ado daga Masar ne filafilan jirgin ruwanki suka kuma zama tutarki; an yi tutarki da shuɗi da shunayya daga bakin tekun Elisha.
Fine broidered linen from Egypt was woven for thy sail, to be spread on thy mast: blue and purple from the islands of Elisa, were made thy covering.
8 Mutanen Sidon da Arfad su ne matuƙan jirgin ruwanki; gwanayenki, ya Taya, suna ciki a matsayi matuƙan jiragen ruwa.
The inhabitants of Sidon, and the Arabians were thy rowers: thy wise men, O Tyre, were thy pilots.
9 Masu hikima na Gebal suna ciki a matsayin masu tattoshe mahaɗan katakon jirginki. Dukan jiragen ruwa da matuƙansu sukan zo wurinki don kasuwanci.
The ancients of Gebal, and the wise men thereof furnished mariners for the service of thy various furniture: all the ships of the sea, and their mariners were thy factors.
10 “‘Mutanen Farisa, Lidiya da Fut su ne suka zama sojoji a cikin mayaƙanki. Sun rataye garkuwoyinsu da hulunan kwano a katangarki, suna kawo miki daraja.
The Persians, and Lydians, and the Libyans were thy soldiers in thy army: they hung up the buckler and the helmet in thee for thy ornament.
11 Mutanen Arfad da Helek sun yi tsaron katangar a kowace gefe; mutanen Gammad su ne a hasumiyoyinki. Sun rataye garkuwoyinsu kewaye da katangarki; sun sa kyanki ya zama cikakke.
The men of Arad were with thy army upon thy walls round about: the Pygmeans also that were in thy towers, hung up their quivers on thy walls round about: they perfected thy beauty.
12 “‘Tarshish ta yi ciniki da ke saboda yawan wadatar kayayyakinki; sun sayi kayan cinikinki da azurfa, ƙarfe, kuza da dalma.
The Carthaginians thy merchants supplied thy fairs with a multitude of all kinds of riches, with silver, iron, tin, and lead.
13 “‘Girka, Tubal da Meshek sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki suka biya da bayi da kuma abubuwan da aka yi da tagulla.
Greece, Thubal, and Mosoch, they were thy merchants: they brought to thy people slaves and vessels of brass.
14 “‘Mutanen Bet Togarma sun sayi kayan cinikinki da dawakai, dawakan yaƙi da alfadarai.
From the house of Thogorma they brought horses, and horsemen, and mules to thy market.
15 “‘Mutanen Dedan sun yi kasuwanci da ke, bakin teku masu yawa abokan cinikinki ne; sun biya ki da hauren giwa da katakon kanya.
The men of Dedan were thy merchants: many islands were the traffic of thy hand, they exchanged for thy price teeth of ivory and ebony.
16 “‘Mutanen Aram sun yi ciniki da ke saboda yawan kayanki; suka sayi kayan cinikinki da zumurrudu, da shunayya, da kayan ado, da lilin mai taushi, da murjani, da yakutu.
The Syrian was thy merchant: by reason of the multitude of thy works, they set forth precious stones, and purple, and broidered works, and fine linen, and silk, and chodchod in thy market.
17 “‘Yahuda da Isra’ila sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki da alkama da Minnit da alawa, da zuma, da mai, da ganyaye masu ƙanshi.
Juda and the land of Israel, they were thy merchants with the best corn: they set forth balm, and honey, and oil, and rosin in thy fairs.
18 “‘Mutanen Damaskus sun ga abin da za ki iya bayarwa sai suka yi ciniki da ke, ta sayi kayanki da ruwan inabi daga Helbon, da ulu daga Zahar.
The men of Damascus were thy merchants in the multitude of thy works, in the multitude of divers riches, in rich wine, in wool of the best colour.
19 Wedan da Yaban kusa da Uzal, suka sayi kayanki; wato gyararren ƙarfe da kayan yaji.
Dan, and Greece, and Mosel have set forth in thy marts wrought iron: stacte, and calamus were in thy market.
20 “‘Mutanen Dedan sun sayi kayanki da sirdin zama a kan dawakai.
The men of Dedan were thy merchants in tapestry for seats.
21 “‘Mutanen Arabiya da dukan sarakunan Kedar abokan cinikinki ne; sun yi ciniki da ke suka sayi kayanki da’yan raguna, da raguna, da awaki.
Arabia, and all the princes of Cedar, they were the merchants of thy hand: thy merchants came to thee with lambs, and rants, and kids.
22 “‘’Yan kasuwan Sheba da Ra’ama sun yi ciniki da ke; suka sayi kayanki da kayan yaji mafi kyau iri-iri, da duwatsu masu daraja iri-iri, da zinariya.
The sellers of Saba, and Reema, they were thy merchants: with all the best spices, and precious stones, and gold, which they set forth in thy market.
23 “‘Haran, Kanne da Eden da kuma’yan kasuwan Sheba, Assuriya da Kilmad sun yi ciniki da ke.
Haran, and Chene, and Eden were thy merchants; Saba, Assur, and Chelmad sold to thee.
24 A kasuwarki sun yi ciniki da ke suka sayar miki tufafi masu tsada, da na shuɗi, da masu ado, da dardumai masu ƙyalƙyali da kirtani, da igiyoyi waɗanda aka tuƙa da kyau.
They were thy merchants in divers manners, with bales of blue cloth, and of embroidered work, and of precious riches, which were wrapped up and bound with cords: they had cedars also in thy merchandise.
25 “‘Jiragen ruwan Tarshish sun zama masu jigilar kayanki. Kin cika da kaya masu nauyi a tsakiyar teku.
The ships of the sea, were thy chief in thy merchandise: and thou wast replenished, and glorified exceedingly in the heart of the sea.
26 Matuƙan jiragenki sun kai ki can cikin manyan tekuna. Amma iskar gabas za tă farfasa ki kucu-kucu a tsakiyar teku.
Thy rowers have brought thee into great waters: the south wind hath broken thee in the heart of the sea.
27 Dukiyarki, cinikinki da kayan kasuwarki, ma’aikatanki na jirgi, matuƙan jiragenki da masu tattoshe mahaɗan katakan jiragenki,’yan kasuwarki da dukan sojojinki, da kuma kowa da yake cikin jirgi zai nutsa a tsakiyar teku a ranar da jirginki zai nutse.
Thy riches, and thy treasures, and thy manifold furniture, thy mariners, and thy pilots, who kept thy goods, and were chief over thy people: thy men of war also, that were in thee, with all thy multitude that is in the midst of thee: shall fall in the heart of the sea in the day of thy ruin.
28 Ƙasashen bakin teku za su girgiza sa’ad da matuƙan jirginki suka yi kuka.
Thy fleets shall be troubled at the sound of the cry of thy pilots.
29 Dukan waɗanda suke riƙe da matuƙi za su ƙyale jiragensu; ma’aikatan jirage da dukan matuƙan jirage za su tsaya a bakin teku.
And all that handled the oar shall come down from their ships: the mariners, and all the pilots of the sea shall stand upon the land:
30 Za su tā da muryarsu su yi kuka mai zafi a kanki; za su yayyafa ƙura a kawunansu, su yi ta birgima a cikin toka.
And they shall mourn over thee with a loud voice, and shall cry bitterly: and they shall cast up dust upon their heads, and shall be sprinkled with ashes.
31 Za su aske kawunansu saboda ke za su kuma sa tufafin makoki. Za su yi kuka dominki su yi ɓacin rai da kuma kuka mai zafi.
And they shall shave themselves bald for thee, and shall be girded with haircloth: and they shall weep for thee with bitterness of soul, with most bitter weeping.
32 Yayinda suke kuka a kanki kuwa, za su yi makoki dominki suna cewa, “Wa ya taɓa yin shiru kamar Taya, kewaye da teku?”
And they shall take up a mournful song for thee, and snail lament thee: What city is like Tyre, which is become silent in the midst of the sea?
33 Sa’ad da kayan cinikinki suka tafi ƙasashen hayi, kin gamsar da al’ummai masu yawa; da dukiyarki masu yawa da kuma kayan cinikinki kin azurtar da sarakunan duniya.
Which by thy merchandise that went from thee by sea didst fill many people: which by the multitude of thy riches, and of thy people didst enrich the kings of the earth.
34 Yanzu teku ta farfashe ki cikin zurfafan ruwaye; kayan cinikinki da dukan kamfaninki sun nutse tare da ke.
Now thou art destroyed by the sea, thy riches are in the bottom of the waters, and all the multitude that was in the midst of thee is fallen.
35 Dukan mazaunan bakin teku sun giggice saboda masifarki; sarakunansu sun tsorata ƙwarai fuskokinsu kuwa sun yamutse don tsoro.
All the inhabitants of the islands are astonished at thee: and all their kings being struck with the storm have changed their countenance.
36 ’Yan kasuwa a cikin al’ummai suna yin miki tsaki; kin zo ga mummunar ƙarshe ba za ki ƙara kasancewa ba har abada.’”
The merchants of people have hissed at thee: thou art brought to nothing, and thou shalt never be any more.

< Ezekiyel 27 >