< Ezekiyel 27 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me saying,
2 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin Taya.
And thou, son of man, take up a lamentation against Sor;
3 Ka ce wa Taya, wadda take zaune a hanyar shiga zuwa teku, kasuwar masu yawa mutane a bakin teku, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kin ce, ya Taya, “Ni kyakkyawa ce cikakkiya.”
and thou shalt say to Sor that dwells at the entrance of the sea, to the mart of the nations coming from many islands, Thus saith the Lord to Sor; Thou hast said, I have clothed myself with my beauty.
4 Manyan tekuna ne wurin zamanki; maginanki sun sa kyanki ya zama cikakke.
In the heart of the sea thy sons have put beauty upon thee for Beelim.
5 Sun yi dukan katakanki daga itatuwan fir daga Senir; sun kwaso itatuwan al’ul daga Lebanon don su yi miki jigon jirgin ruwa.
Cedar in Senir was employed for thee in building: boards of cypress timber were taken out of Libanus, and wood to make thee masts of fir.
6 Da oak daga Bashan suka yi sandunan tuƙan jirgin ruwa da itatuwan kasharina daga bakin tekun Saifurus suka yi daɓe jirgin ruwanki, suka kuma manne masa hauren giwa.
They made thine oars [of wood] out of the land of Basan; thy sacred utensils they made of ivory, thy shady houses of wood from the isles of Chetiim.
7 Lilin mai kyau mai ado daga Masar ne filafilan jirgin ruwanki suka kuma zama tutarki; an yi tutarki da shuɗi da shunayya daga bakin tekun Elisha.
Fine linen with embroidery from Egypt supplied the couch, to put honour upon thee, and to clothe thee with blue and purple from the isles of Elisai; and they became thy coverings.
8 Mutanen Sidon da Arfad su ne matuƙan jirgin ruwanki; gwanayenki, ya Taya, suna ciki a matsayi matuƙan jiragen ruwa.
And thy princes were the dwellers in Sidon, and the Aradians were thy rowers: thy wise men, O Sor, who were in thee, these were thy pilots.
9 Masu hikima na Gebal suna ciki a matsayin masu tattoshe mahaɗan katakon jirginki. Dukan jiragen ruwa da matuƙansu sukan zo wurinki don kasuwanci.
The elders of the Biblians, and their wise men, who were in thee, these helped thy counsel: and all the ships of the sea and their rowers traded for thee to the utmost west.
10 “‘Mutanen Farisa, Lidiya da Fut su ne suka zama sojoji a cikin mayaƙanki. Sun rataye garkuwoyinsu da hulunan kwano a katangarki, suna kawo miki daraja.
Persians and Lydians and Libyans were in thine army: thy warriors hung in thee shields and helmets; these gave [thee] thy glory.
11 Mutanen Arfad da Helek sun yi tsaron katangar a kowace gefe; mutanen Gammad su ne a hasumiyoyinki. Sun rataye garkuwoyinsu kewaye da katangarki; sun sa kyanki ya zama cikakke.
The sons of the Aradians and thine army were upon the walls; there were guards in thy towers: they hung their quivers on thy battlements round about; these completed thy beauty.
12 “‘Tarshish ta yi ciniki da ke saboda yawan wadatar kayayyakinki; sun sayi kayan cinikinki da azurfa, ƙarfe, kuza da dalma.
The Carthaginians were thy merchants because of the abundance of all thy strength; they furnished thy market with silver, and gold, and iron, and tin, and lead.
13 “‘Girka, Tubal da Meshek sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki suka biya da bayi da kuma abubuwan da aka yi da tagulla.
Greece, both the whole [world], and the adjacent coasts, these traded with thee in the persons of men, and they gave [as] thy merchandise vessels of brass.
14 “‘Mutanen Bet Togarma sun sayi kayan cinikinki da dawakai, dawakan yaƙi da alfadarai.
Out of the house of Thogarma horses and horsemen furnished the market.
15 “‘Mutanen Dedan sun yi kasuwanci da ke, bakin teku masu yawa abokan cinikinki ne; sun biya ki da hauren giwa da katakon kanya.
The sons of the Rhodians were thy merchants; from the islands they multiplied thy merchandise, [even] elephants' teeth: and to them that came in thou didst return thy prices,
16 “‘Mutanen Aram sun yi ciniki da ke saboda yawan kayanki; suka sayi kayan cinikinki da zumurrudu, da shunayya, da kayan ado, da lilin mai taushi, da murjani, da yakutu.
[even] men [as] thy merchandise, from the multitude of thy trading [population], myrrh and embroidered works from Tharsis: Ramoth also and Chorchor furnished thy market.
17 “‘Yahuda da Isra’ila sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki da alkama da Minnit da alawa, da zuma, da mai, da ganyaye masu ƙanshi.
Juda and the children of Israel, these were thy merchants; in the sale of corn and ointments and cassia: and they gave the best honey, and oil, and resin, to thy trading [population].
18 “‘Mutanen Damaskus sun ga abin da za ki iya bayarwa sai suka yi ciniki da ke, ta sayi kayanki da ruwan inabi daga Helbon, da ulu daga Zahar.
[The people of] Damascus were thy merchants by reason of the abundance of all thy power; wine out of Chelbon, and wool from Miletus; and they brought wine into thy market.
19 Wedan da Yaban kusa da Uzal, suka sayi kayanki; wato gyararren ƙarfe da kayan yaji.
Out of Asel [came] wrought iron, and there is the sound of wheels among thy trading [population].
20 “‘Mutanen Dedan sun sayi kayanki da sirdin zama a kan dawakai.
[The people of] Daedan were thy merchants, with choice cattle for chariots.
21 “‘Mutanen Arabiya da dukan sarakunan Kedar abokan cinikinki ne; sun yi ciniki da ke suka sayi kayanki da’yan raguna, da raguna, da awaki.
Arabia and all the princes of Kedar, these were thy traders with thee, [bringing] camels, and lambs, and rams, in which they trade with thee.
22 “‘’Yan kasuwan Sheba da Ra’ama sun yi ciniki da ke; suka sayi kayanki da kayan yaji mafi kyau iri-iri, da duwatsu masu daraja iri-iri, da zinariya.
The merchants of Sabba and Ramma, these were thy merchants, with choice spices, and precious stones: and they brought gold to thy market.
23 “‘Haran, Kanne da Eden da kuma’yan kasuwan Sheba, Assuriya da Kilmad sun yi ciniki da ke.
Charra, and Chanaa, these were thy merchants: Assur, and Charman, were thy merchants:
24 A kasuwarki sun yi ciniki da ke suka sayar miki tufafi masu tsada, da na shuɗi, da masu ado, da dardumai masu ƙyalƙyali da kirtani, da igiyoyi waɗanda aka tuƙa da kyau.
bringing [for] merchandise blue, and choice stores bound with cords, and cypress wood.
25 “‘Jiragen ruwan Tarshish sun zama masu jigilar kayanki. Kin cika da kaya masu nauyi a tsakiyar teku.
Ships were thy merchants, in abundance, with thy trading [population]: and thou wast filled and very heavily loaded in the heart of the sea.
26 Matuƙan jiragenki sun kai ki can cikin manyan tekuna. Amma iskar gabas za tă farfasa ki kucu-kucu a tsakiyar teku.
Thy rowers have brought thee into great waters: the south wind has broken thee in the heart of the sea.
27 Dukiyarki, cinikinki da kayan kasuwarki, ma’aikatanki na jirgi, matuƙan jiragenki da masu tattoshe mahaɗan katakan jiragenki,’yan kasuwarki da dukan sojojinki, da kuma kowa da yake cikin jirgi zai nutsa a tsakiyar teku a ranar da jirginki zai nutse.
Thy forces, and thy gain, and that of thy traders, and thy rowers, and thy pilots, and thy counselors, and they that traffic with thee, and all thy warriors that are in thee: and all thy company in the midst of thee shall perish in the heart of the sea, in the day of thy fall.
28 Ƙasashen bakin teku za su girgiza sa’ad da matuƙan jirginki suka yi kuka.
At the cry of thy voice thy pilots shall be greatly terrified.
29 Dukan waɗanda suke riƙe da matuƙi za su ƙyale jiragensu; ma’aikatan jirage da dukan matuƙan jirage za su tsaya a bakin teku.
And all the rowers and the mariners shall come down from the ships, and the pilots of the sea shall stand on the land.
30 Za su tā da muryarsu su yi kuka mai zafi a kanki; za su yayyafa ƙura a kawunansu, su yi ta birgima a cikin toka.
And they shall wail over thee with their voice, and cry bitterly, and put earth on their heads, and spread ashes under them.
31 Za su aske kawunansu saboda ke za su kuma sa tufafin makoki. Za su yi kuka dominki su yi ɓacin rai da kuma kuka mai zafi.
32 Yayinda suke kuka a kanki kuwa, za su yi makoki dominki suna cewa, “Wa ya taɓa yin shiru kamar Taya, kewaye da teku?”
And their sons shall take up a [lament] for thee, even a lamentation for Sor, [saying],
33 Sa’ad da kayan cinikinki suka tafi ƙasashen hayi, kin gamsar da al’ummai masu yawa; da dukiyarki masu yawa da kuma kayan cinikinki kin azurtar da sarakunan duniya.
How large a reward hast thou gained from the sea? thou hast filled nations out of thine abundance; and out of thy mixed merchandise thou hast enriched all the kings of the earth.
34 Yanzu teku ta farfashe ki cikin zurfafan ruwaye; kayan cinikinki da dukan kamfaninki sun nutse tare da ke.
Now art thou broken in the sea, thy traders are in the deep water, and all thy company in the midst of thee: all thy rowers have fallen.
35 Dukan mazaunan bakin teku sun giggice saboda masifarki; sarakunansu sun tsorata ƙwarai fuskokinsu kuwa sun yamutse don tsoro.
All the dwellers in the islands have mourned over thee, and their kings have been utterly amazed, and their countenance has wept.
36 ’Yan kasuwa a cikin al’ummai suna yin miki tsaki; kin zo ga mummunar ƙarshe ba za ki ƙara kasancewa ba har abada.’”
Merchants from the nations have hissed at thee; thou art utterly destroyed, and shalt not be any more for ever.