< Ezekiyel 26 >

1 A shekara ta goma sha ɗaya, a rana ta fari ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Kwasekusithi ngomnyaka wetshumi lanye, ngolokuqala lwenyanga, ilizwi leNkosi lafika kimi, lisithi:
2 “Ɗan mutum, domin Taya ta yi magana a kan Urushalima ta ce, ‘Yauwa! Ƙofar zuwa al’ummai ta karye, an kuma buɗe mini ƙofofinta; yanzu da take kufai zan wadace,’
Ndodana yomuntu, ngenxa yokuthi iTire itshilo ngeJerusalema isithi: Aha, yephukile ebingamasango abantu; isiphendukele kimi; ngizagcwaliswa, ichithekile.
3 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da ke, ya Taya, zan kuwa kawo al’ummai masu yawa su yi gāba da ke, kamar yadda teku takan kawo raƙuman ruwa.
Ngakho itsho njalo iNkosi uJehova: Khangela, ngimelane lawe, wena Tire, ngenze izizwe ezinengi zenyuke zimelane lawe, njengolwandle lusenza amagagasi alo enyuke.
4 Za su hallaka katangar Taya su kuma rurrushe hasumiyoyinta; zan kankare tarkacenta, in maishe ta fā.
Njalo zizachitha imiduli yeTire, zibhidlizele phansi imiphotshongo yayo; ngiphale inhlabathi yayo kuyo, ngiyenze ibe lidwala elize.
5 Za tă zama wurin shanya abin kamun kifi a tsakiyar teku, gama na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Za tă zama ganima ga sauran al’ummai,
Izakuba yindawo yokuchayela amambule, phakathi kolwandle; ngoba mina ngikhulumile, itsho iNkosi uJehova; njalo izakuba yimpango yezizwe.
6 za a kashe mazaunan filin ƙasar da takobi. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.
Lamadodakazi ayo asensimini azabulawa ngenkemba. Njalo bazakwazi ukuthi ngiyiNkosi.
7 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa daga arewa zan kawo wa Taya Nebukadnezzar sarkin Babilon, sarkin sarakuna, tare da dawakai da kekunan yaƙi, da mahayan dawakai da babbar rundunar soja.
Ngoba itsho njalo iNkosi uJehova: Khangela, ngizaletha phezu kweTire uNebhukadirezari inkosi yeBhabhiloni, inkosi yamakhosi, evela enyakatho, elamabhiza, lezinqola, labagadi bamabhiza, lamaxuku, labantu abanengi.
8 Zai kashe mazaunan filin ƙasar da takobi; zai yi miki ƙawanya, ya gina miki mahaurai, sa’an nan ya rufe ki da garkuwoyi.
Uzabulala ngenkemba amadodakazi akho ensimini, enze umduli wokuvimbezela emelene lawe, abuthelele idundulu emelene lawe, aphakamise isihlangu esikhulu simelene lawe.
9 Zai rushe katangarki da dundurusai, ya rurrushe hasumiyoyinki da makamai.
Uzamisa imigqala yokudiliza imelane lemiduli yakho, adilizele phansi imiphotshongo yakho ngezinkemba zakhe.
10 Dawakansa za su yi yawa har su rufe ke da ƙura. Katanga za su girgiza saboda motsin dawakan yaƙi, kekunan doki da keken yaƙin sa’ad da suka shiga birnin da aka rushe katangar.
Ngenxa yobunengi bamabhiza akhe uthuli lwawo luzakusibekela; imiduli yakho izanyikinywa ngumsindo wabagadi bamabhiza lamavili lezinqola, nxa ezangena emasangweni akho, njengokungena emzini ofohlelwayo.
11 Kofatan dawakansa za su tattake dukan titunanki; zai kashe mutanenki da takobi, ginshiƙanki masu ƙarfi kuma za su fāɗi a ƙasa.
Ngamasondo amabhiza akhe uzanyathela zonke izitalada zakho; uzabulala abantu bakho ngenkemba, lensika zakho eziqinileyo ziwele emhlabathini.
12 Za su washe dukiyarki, kayan cinikinki kuma su zama ganima; za su rurrushe katangarki su ragargaza gidajenki masu kyau su kuma zubar da duwatsunki, katakanki da kuma tarkacenki a cikin teku.
Njalo bazaphanga inotho yakho, bathumbe impahla yakho ethengiswayo, badilizele phansi imiduli yakho, babhidlize izindlu zakho eziloyisekayo, bafake amatshe akho lezigodo zakho lothuli lwakho phakathi kwamanzi.
13 Zan kawo ƙarshen waƙoƙinki masu surutu, ba kuwa za a ƙara jin kaɗe-kaɗen garayunki ba.
Ngizakwenza kuphele umsindo wengoma zakho, lelizwi lamachacho akho kalisayikuzwakala.
14 Zan maishe ki fā, za ki kuma zama wurin shanya abin kamun kifi. Ba za a sāke gina ki ba, gama Ni Ubangiji na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Njalo ngizakwenza ube lidwala elize; uzakuba yindawo yokuchayela amambule, kawusayikwakhiwa; ngoba mina Nkosi ngikhulumile, itsho iNkosi uJehova.
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Taya. Ƙasashen da suke a bakin teku ba za su girgiza saboda ƙarar fāɗuwarki, sa’ad da nishin waɗanda aka yi wa rauni da kashe-kashen da aka yi a cikinki suka faru ba?
Itsho njalo iNkosi uJehova kuyo iTire: Izihlenge kaziyikunyikinyeka yini ngomdumo wokuwa kwakho, lapho abalimeleyo bebubula, lapho kubulawa okubulawayo phakathi kwakho?
16 Sa’an nan sarakunan bakin teku za su sauka daga gadajen sarautarsu, su tuɓe rigunansu, da rigunansu waɗanda aka yi wa ado. Za su zauna a ƙasa suna rawar jiki a kowane lokaci suna razana saboda abin da ya same ki.
Khona zonke iziphathamandla zolwandle zizakwehla ezihlalweni zazo zobukhosi, zikhulule izigqoko zazo, zikhuphe izembatho zazo ezifekethisiweyo; zizembathise ukuthuthumela, zihlale emhlabathini, zithuthumele ngaso sonke isikhathi, zimangale kakhulu ngawe.
17 Sa’an nan za su yi makoki game da ke su ce, “‘Yaya kika hallaka haka nan, ya birnin da ta yi suna, cike da mutanen teku! Ke da kika zama mai ƙarfi cikin tekuna, ke da mazauna cikinki; kin sa tsoronki a kan dukan waɗanda suka zauna a can.
Zizakuphakamisela isililo, zithi kuwe: Uchithwe njani ezinlwandle wena owawuhlalwa, umuzi olodumo, owawulamandla olwandle, wona labahlali bawo, abamisa ukwesabeka kwabo kuye wonke umhlali wawo!
18 Yanzu tsibirai suna rawar jiki a ranar fāɗuwarki; tsibirai a cikin teku sun tsorata a ɓacewarki.’
Khathesi izihlenge zizathuthumela ngosuku lokuwa kwakho, yebo, izihlenge eziselwandle zizakhathazeka ngokuphuma kwakho.
19 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na maishe ki kufai, kamar sauran biranen da ba a ƙara zama a ciki, sa’ad da kuma na kawo zurfafan teku a kanki da yawan ruwansa suka rufe ki,
Ngoba itsho njalo iNkosi uJehova: Lapho ngizakwenza ube ngumuzi olunxiwa, njengemizi engahlalwayo; lapho ngizakwenyusa ukujula phezu kwakho, lamanzi amanengi akusibekele;
20 a sa’an nan zan sauko da ke ƙasa tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, zuwa wurin mutanen dā. Zan sa ki zauna ƙarƙashin ƙasa, kamar a kufai na tun dā, tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, ba kuwa za ki ƙara dawowa ba ko ki ɗauki matsayinki a ƙasar masu rai.
khona ngizakwehlisela phansi lalabo abehlela emgodini, ebantwini basendulo, ngikuhlalise ezindaweni eziphansi zomhlaba, emanxiweni asendulo, lalabo abehlela emgodini, ukuze ungahlalwa; njalo ngizabeka udumo elizweni labaphilayo.
21 Zan sa ki yi mummunan ƙarshe kuma ba za ki ƙara kasancewa ba. Za a neme ki, amma ba za a ƙara same ki ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Ngizakwenza ube ngokwesabekayo okukhulu, ungasabikho; lanxa udingwa, ungatholakali futhi kuze kube nininini, itsho iNkosi uJehova.

< Ezekiyel 26 >