< Ezekiyel 26 >

1 A shekara ta goma sha ɗaya, a rana ta fari ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et il arriva en l'onzième année, le premier jour du mois, que la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
2 “Ɗan mutum, domin Taya ta yi magana a kan Urushalima ta ce, ‘Yauwa! Ƙofar zuwa al’ummai ta karye, an kuma buɗe mini ƙofofinta; yanzu da take kufai zan wadace,’
Fils d'homme, parce que Tyr a dit touchant Jérusalem: ha! ha! celle qui était la porte des peuples a été rompue, elle s'est réfugiée chez moi, je serai remplie [parce] qu'elle a été rendue déserte.
3 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da ke, ya Taya, zan kuwa kawo al’ummai masu yawa su yi gāba da ke, kamar yadda teku takan kawo raƙuman ruwa.
A cause de cela ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: voici, j'en veux à toi, Tyr, et je ferai monter contre toi plusieurs nations, comme la mer fait monter ses flots.
4 Za su hallaka katangar Taya su kuma rurrushe hasumiyoyinta; zan kankare tarkacenta, in maishe ta fā.
Et elles détruiront les murailles de Tyr, et démoliront ses tours; je raclerai sa poudre, et la rendrai semblable à une pierre sèche.
5 Za tă zama wurin shanya abin kamun kifi a tsakiyar teku, gama na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Za tă zama ganima ga sauran al’ummai,
Elle servira à étendre les filets au milieu de la mer; car j'ai parlé, dit le Seigneur l'Eternel, et elle sera en pillage aux nations.
6 za a kashe mazaunan filin ƙasar da takobi. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.
Et les villes de son ressort, qui sont à la campagne, seront mises au fil de l'épée, et elles sauront que je suis l'Eternel.
7 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa daga arewa zan kawo wa Taya Nebukadnezzar sarkin Babilon, sarkin sarakuna, tare da dawakai da kekunan yaƙi, da mahayan dawakai da babbar rundunar soja.
Car ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: voici je m'en vais faire venir de l'Aquilon contre Tyr, Nébucadnetsar, Roi de Babylone, le Roi des Rois, avec des chevaux, et des chariots, et des gens de cheval, et un grand peuple assemblé de toutes parts.
8 Zai kashe mazaunan filin ƙasar da takobi; zai yi miki ƙawanya, ya gina miki mahaurai, sa’an nan ya rufe ki da garkuwoyi.
Il mettra au fil de l'épée les villes de ton ressort qui sont à la campagne, il fera des forts contre toi, il dressera des terrasses contre toi, et il lèvera les boucliers contre toi.
9 Zai rushe katangarki da dundurusai, ya rurrushe hasumiyoyinki da makamai.
Et il posera ses machines de guerre contre tes murailles, et démolira tes tours avec ses marteaux.
10 Dawakansa za su yi yawa har su rufe ke da ƙura. Katanga za su girgiza saboda motsin dawakan yaƙi, kekunan doki da keken yaƙin sa’ad da suka shiga birnin da aka rushe katangar.
La poussière de ses chevaux te couvrira à cause de leur multitude; tes murailles trembleront du bruit des gens de cheval, des charrettes, et des chariots, quand il entrera par tes portes, comme on entre dans une ville à laquelle on a fait brèche.
11 Kofatan dawakansa za su tattake dukan titunanki; zai kashe mutanenki da takobi, ginshiƙanki masu ƙarfi kuma za su fāɗi a ƙasa.
Il foulera toutes tes rues avec la corne des pieds de ses chevaux; il tuera ton peuple avec l'épée, et les trophées de ta force tomberont par terre.
12 Za su washe dukiyarki, kayan cinikinki kuma su zama ganima; za su rurrushe katangarki su ragargaza gidajenki masu kyau su kuma zubar da duwatsunki, katakanki da kuma tarkacenki a cikin teku.
Puis ils butineront tes biens, et pilleront ta marchandise; ils ruineront tes murailles, et démoliront tes maisons de plaisance; et ils mettront tes pierres et ton bois et ta poussière au milieu des eaux.
13 Zan kawo ƙarshen waƙoƙinki masu surutu, ba kuwa za a ƙara jin kaɗe-kaɗen garayunki ba.
Et je ferai cesser le bruit de tes chansons, et le son de tes harpes ne sera plus ouï.
14 Zan maishe ki fā, za ki kuma zama wurin shanya abin kamun kifi. Ba za a sāke gina ki ba, gama Ni Ubangiji na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Je te rendrai semblable à une pierre sèche; elle sera un lieu pour étendre les filets, et elle ne sera plus rebâtie, parce que moi l'Eternel j'ai parlé, dit le Seigneur l'Eternel.
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Taya. Ƙasashen da suke a bakin teku ba za su girgiza saboda ƙarar fāɗuwarki, sa’ad da nishin waɗanda aka yi wa rauni da kashe-kashen da aka yi a cikinki suka faru ba?
Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel à Tyr: les Iles ne trembleront-elles pas du bruit de ta ruine, quand ceux qui seront blessés à mort gémiront, quand le carnage se fera au milieu de toi?
16 Sa’an nan sarakunan bakin teku za su sauka daga gadajen sarautarsu, su tuɓe rigunansu, da rigunansu waɗanda aka yi wa ado. Za su zauna a ƙasa suna rawar jiki a kowane lokaci suna razana saboda abin da ya same ki.
Tous les Princes de la mer descendront de leurs sièges, et ôteront leurs manteaux, et dépouilleront leurs vêtements de broderie, et se vêtiront de frayeur; ils s'assiéront sur la terre, et ils seront effrayés de moment en moment, et seront désolés à cause de toi.
17 Sa’an nan za su yi makoki game da ke su ce, “‘Yaya kika hallaka haka nan, ya birnin da ta yi suna, cike da mutanen teku! Ke da kika zama mai ƙarfi cikin tekuna, ke da mazauna cikinki; kin sa tsoronki a kan dukan waɗanda suka zauna a can.
Et ils prononceront à haute voix une complainte sur toi, et te diront: comment as-tu péri, toi qui étais fréquentée par ceux qui vont sur la mer, ville renommée, qui étais forte en la mer, toi et tes habitants, qui se sont fait redouter à tous ceux qui habitent en elle?
18 Yanzu tsibirai suna rawar jiki a ranar fāɗuwarki; tsibirai a cikin teku sun tsorata a ɓacewarki.’
Maintenant les Iles seront effrayées au jour de ta ruine, et les Iles qui [sont] en la mer seront étonnées à cause de ta fuite.
19 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na maishe ki kufai, kamar sauran biranen da ba a ƙara zama a ciki, sa’ad da kuma na kawo zurfafan teku a kanki da yawan ruwansa suka rufe ki,
Car ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: quand je t'aurai rendue une ville désolée, comme sont les villes qui ne sont point habitées, quand j'aurai fait tomber sur toi l'abîme, et que les grosses eaux t'auront couverte;
20 a sa’an nan zan sauko da ke ƙasa tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, zuwa wurin mutanen dā. Zan sa ki zauna ƙarƙashin ƙasa, kamar a kufai na tun dā, tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, ba kuwa za ki ƙara dawowa ba ko ki ɗauki matsayinki a ƙasar masu rai.
Alors je te ferai descendre avec ceux qui descendent en la fosse, vers le peuple d'autrefois, et je te placerai aux lieux les plus bas de la terre, aux endroits désolés depuis longtemps, avec ceux qui descendent en la fosse, afin que tu ne sois plus habitée; mais je remettrai la noblesse parmi la terre des vivants.
21 Zan sa ki yi mummunan ƙarshe kuma ba za ki ƙara kasancewa ba. Za a neme ki, amma ba za a ƙara same ki ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Je ferai qu'on sera tout étonné à cause de toi, de ce que tu n'es plus; et quand on te cherchera, on ne te trouvera plus à jamais, dit le Seigneur l'Eternel.

< Ezekiyel 26 >