< Ezekiyel 26 >

1 A shekara ta goma sha ɗaya, a rana ta fari ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Almost twelve [after we had been taken to Babylonia], on the first day of the month, Yahweh gave me another message. He said to me,
2 “Ɗan mutum, domin Taya ta yi magana a kan Urushalima ta ce, ‘Yauwa! Ƙofar zuwa al’ummai ta karye, an kuma buɗe mini ƙofofinta; yanzu da take kufai zan wadace,’
“You human, [the people of] Tyre [city] shouted joyfully and said about Jerusalem, ‘[Jerusalem, ] the city from which many traders/merchants went to many nations, is now destroyed. And now people from all over the world will come to us to buy and sell things. Because Jerusalem has now been ruined, we will prosper!’
3 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da ke, ya Taya, zan kuwa kawo al’ummai masu yawa su yi gāba da ke, kamar yadda teku takan kawo raƙuman ruwa.
Therefore, this is what [I, ] Yahweh the Lord, say: ‘I am now the enemy of [you people of] Tyre. I will [the armies of] many nations to come and attack your [city], like the waves of the sea beat against the shores.
4 Za su hallaka katangar Taya su kuma rurrushe hasumiyoyinta; zan kankare tarkacenta, in maishe ta fā.
Their soldiers will destroy the walls around Tyre and tear down its towers. Tyre will become a place where people from many nations steal valuable things, [and then the city will be completely destroyed]. Then they will scrape away the rubble and cause the city to become a bare rock.
5 Za tă zama wurin shanya abin kamun kifi a tsakiyar teku, gama na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Za tă zama ganima ga sauran al’ummai,
Out in the sea, Tyre will become an island where men spread [their fishing] nets to dry them. [That will surely happen because] I, Yahweh the Lord, have predicted it.
6 za a kashe mazaunan filin ƙasar da takobi. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.
The people in small villages on the coast near Tyre will be killed [their enemies’] swords. Then people will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].’
7 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa daga arewa zan kawo wa Taya Nebukadnezzar sarkin Babilon, sarkin sarakuna, tare da dawakai da kekunan yaƙi, da mahayan dawakai da babbar rundunar soja.
This is what I, Yahweh the Lord, [is going to happen]: ‘From the north, I am going to bring the most powerful king [in the world], King Nebuchadnezzar of Babylon, [with his army] to attack Tyre. They will bring horses and chariots, and men who ride the horses [and men who drive the chariots]; it will be a huge army.
8 Zai kashe mazaunan filin ƙasar da takobi; zai yi miki ƙawanya, ya gina miki mahaurai, sa’an nan ya rufe ki da garkuwoyi.
[In the battles in the small villages] on the coast, their soldiers will kill [many] people with their swords. [Then] they will set up devices to batter the wall around the city of Tyre, and they will build a dirt ramp up to the top of the wall, and they will all hold up shields [to protect themselves from arrows being shot from the ground].
9 Zai rushe katangarki da dundurusai, ya rurrushe hasumiyoyinki da makamai.
The king will direct the soldiers who operate the (rams/things) to batter the walls, and who will use their iron bars to tear down the towers in the wall.
10 Dawakansa za su yi yawa har su rufe ke da ƙura. Katanga za su girgiza saboda motsin dawakan yaƙi, kekunan doki da keken yaƙin sa’ad da suka shiga birnin da aka rushe katangar.
The king will have a huge number of horses, [the stamping of their hooves will result in] the city being covered with dust. [It will be as though] the walls will tremble because of the noise made by the horses, the [supply] wagons, and the chariots when they enter the city where the walls have been broken down.
11 Kofatan dawakansa za su tattake dukan titunanki; zai kashe mutanenki da takobi, ginshiƙanki masu ƙarfi kuma za su fāɗi a ƙasa.
The horses will trample all of the [of the city] with their hooves. The soldiers will kill the people with their swords; and they will cause your strong pillars to (collapse/fall to the ground).
12 Za su washe dukiyarki, kayan cinikinki kuma su zama ganima; za su rurrushe katangarki su ragargaza gidajenki masu kyau su kuma zubar da duwatsunki, katakanki da kuma tarkacenki a cikin teku.
They will take away all the people’s valuable possessions and steal the things that the merchants sell. They will tear down the walls of the houses and destroy their fine houses. Then they will throw into the sea the stones [from the walls] of those houses and the timber and the rubble.
13 Zan kawo ƙarshen waƙoƙinki masu surutu, ba kuwa za a ƙara jin kaɗe-kaɗen garayunki ba.
No longer will you sing noisy songs, and people will not play their harps any more.
14 Zan maishe ki fā, za ki kuma zama wurin shanya abin kamun kifi. Ba za a sāke gina ki ba, gama Ni Ubangiji na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
The enemy soldiers will cause the city to become a bare rock and [only] a place where men spread [their fishing] nets. And the city will never be rebuilt. [Those things will surely happen] because [I], Yahweh the Lord, have [that they will happen].’
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Taya. Ƙasashen da suke a bakin teku ba za su girgiza saboda ƙarar fāɗuwarki, sa’ad da nishin waɗanda aka yi wa rauni da kashe-kashen da aka yi a cikinki suka faru ba?
This is [also] what [I], Yahweh the Lord, say about [the people of] Tyre: ‘When the wounded [people in Tyre] groan and many people are slaughtered and the city is destroyed, [it will surely be as though] [RHQ] the areas along the coast will tremble.
16 Sa’an nan sarakunan bakin teku za su sauka daga gadajen sarautarsu, su tuɓe rigunansu, da rigunansu waɗanda aka yi wa ado. Za su zauna a ƙasa suna rawar jiki a kowane lokaci suna razana saboda abin da ya same ki.
Then all the kings [in the cities] along the coast will step down from their thrones and lay aside their robes and their embroidered clothes. They will be terrified, and they will sit on the ground, trembling. They will be appalled because of what has happened to the city of Tyre.
17 Sa’an nan za su yi makoki game da ke su ce, “‘Yaya kika hallaka haka nan, ya birnin da ta yi suna, cike da mutanen teku! Ke da kika zama mai ƙarfi cikin tekuna, ke da mazauna cikinki; kin sa tsoronki a kan dukan waɗanda suka zauna a can.
Then they will sing a sad song about the city, and they will sing this: “The famous city [APO], in which many [who sailed on] the seas lived, is now destroyed! The people of that city had great power [because they had many ships that sailed] on the seas; they caused all the people who lived near them to be terrified.
18 Yanzu tsibirai suna rawar jiki a ranar fāɗuwarki; tsibirai a cikin teku sun tsorata a ɓacewarki.’
Now on the day when that city is destroyed, [it is as though the people in] the areas along the coast tremble and the [the people on the] islands in the sea are terrified because of that city being ruined.”’
19 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na maishe ki kufai, kamar sauran biranen da ba a ƙara zama a ciki, sa’ad da kuma na kawo zurfafan teku a kanki da yawan ruwansa suka rufe ki,
This is also what [I], Yahweh the Lord, say: ‘When I cause the city [of Tyre] to become desolate/empty, like [other] cities in which people no [longer] live, and when I cause the huge waves of the sea to cover it,
20 a sa’an nan zan sauko da ke ƙasa tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, zuwa wurin mutanen dā. Zan sa ki zauna ƙarƙashin ƙasa, kamar a kufai na tun dā, tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, ba kuwa za ki ƙara dawowa ba ko ki ɗauki matsayinki a ƙasar masu rai.
then I will bring the people of that city down to be with those who have gone down to where the dead people are, people who lived long ago. I will cause them to remain in the place below the earth that is like old/ancient ruins, with those who have gone down to that pit [previously], and they will never return to the earth, to where people are alive.
21 Zan sa ki yi mummunan ƙarshe kuma ba za ki ƙara kasancewa ba. Za a neme ki, amma ba za a ƙara same ki ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
I will cause them to die in a horrible way (OR, people will be very afraid because of what happens to that city), and that will be the end of (them/their lives). People will search for that city but it will no longer exist. [That is what I, ] Yahweh the Lord, declare [will happen].’”

< Ezekiyel 26 >