< Ezekiyel 26 >

1 A shekara ta goma sha ɗaya, a rana ta fari ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And it came to pass in the eleventh year, on the first day of the month, that the word of the Lord came unto me, saying,
2 “Ɗan mutum, domin Taya ta yi magana a kan Urushalima ta ce, ‘Yauwa! Ƙofar zuwa al’ummai ta karye, an kuma buɗe mini ƙofofinta; yanzu da take kufai zan wadace,’
Son of man, because Tyre hath said concerning Jerusalem, Aha, she is broken that was the gates of the people; she is turned unto me; I shall be made full, now she is laid in ruins:
3 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da ke, ya Taya, zan kuwa kawo al’ummai masu yawa su yi gāba da ke, kamar yadda teku takan kawo raƙuman ruwa.
Therefore thus hath said the Lord Eternal, Behold, I am against thee, O Tyre, and will bring up against thee many nations, as the sea causeth its waves to come up.
4 Za su hallaka katangar Taya su kuma rurrushe hasumiyoyinta; zan kankare tarkacenta, in maishe ta fā.
And they shall destroy the walls of Tyre, and pull down her towers: I will also flood away her earth from her, and I will change her into a naked rock.
5 Za tă zama wurin shanya abin kamun kifi a tsakiyar teku, gama na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Za tă zama ganima ga sauran al’ummai,
A place for the spreading out of nets shall she be in the midst of the sea; for I have spoken it, saith the Lord Eternal: and she shall become a spoil to the nations.
6 za a kashe mazaunan filin ƙasar da takobi. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.
And her daughters that are in the field shall be slain with the sword: and they shall know that I am the Lord.
7 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa daga arewa zan kawo wa Taya Nebukadnezzar sarkin Babilon, sarkin sarakuna, tare da dawakai da kekunan yaƙi, da mahayan dawakai da babbar rundunar soja.
For thus hath said the Lord Eternal, Behold, I will bring against Tyre Nebuchadrezzar the king of Babylon, from the north, the king of kings, with horses, and with chariot's, and with horsemen, and an assemblage, and a numerous people.
8 Zai kashe mazaunan filin ƙasar da takobi; zai yi miki ƙawanya, ya gina miki mahaurai, sa’an nan ya rufe ki da garkuwoyi.
Thy daughters in the field will he slay with the sword: and he shall place around thee works of attack, and cast up against thee a mound, and erect against thee a target-fence.
9 Zai rushe katangarki da dundurusai, ya rurrushe hasumiyoyinki da makamai.
And his catapults shall he set against thy walls, and thy towers shall he break down with his axes.
10 Dawakansa za su yi yawa har su rufe ke da ƙura. Katanga za su girgiza saboda motsin dawakan yaƙi, kekunan doki da keken yaƙin sa’ad da suka shiga birnin da aka rushe katangar.
By reason of the abundance of his horses shall the dust they raise cover thee: by reason of the noise of horsemen, and wheels, and chariots, shall thy walls quake, when he entereth into thy gates, as men enter into a city that is broken in.
11 Kofatan dawakansa za su tattake dukan titunanki; zai kashe mutanenki da takobi, ginshiƙanki masu ƙarfi kuma za su fāɗi a ƙasa.
With the hoofs of his horses shall he tread down all thy streets: thy people will he slay with the sword, and the statues of thy strength shall come down to the ground.
12 Za su washe dukiyarki, kayan cinikinki kuma su zama ganima; za su rurrushe katangarki su ragargaza gidajenki masu kyau su kuma zubar da duwatsunki, katakanki da kuma tarkacenki a cikin teku.
And they shall plunder thy riches, and make a spoil of thy merchandise; and they shall break down thy walls, and thy pleasure-houses shall they pull down: and thy stones and thy timber and thy earth shall they throw into the midst of the water.
13 Zan kawo ƙarshen waƙoƙinki masu surutu, ba kuwa za a ƙara jin kaɗe-kaɗen garayunki ba.
And I will cause the sound of thy songs to cease: and the tones of thy harps shall not be heard any more.
14 Zan maishe ki fā, za ki kuma zama wurin shanya abin kamun kifi. Ba za a sāke gina ki ba, gama Ni Ubangiji na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And I will change thee into a naked rock; a place to spread out nets upon shalt thou be; thou shalt not be rebuilt any more; for I the Lord have spoken it, saith the Lord Eternal.
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Taya. Ƙasashen da suke a bakin teku ba za su girgiza saboda ƙarar fāɗuwarki, sa’ad da nishin waɗanda aka yi wa rauni da kashe-kashen da aka yi a cikinki suka faru ba?
Thus hath said the Lord Eternal to Tyre, Truly at the noise of thy fall, when the deadly wounded whine, when the slaughter taketh place in the midst of thee, shall the islands quake.
16 Sa’an nan sarakunan bakin teku za su sauka daga gadajen sarautarsu, su tuɓe rigunansu, da rigunansu waɗanda aka yi wa ado. Za su zauna a ƙasa suna rawar jiki a kowane lokaci suna razana saboda abin da ya same ki.
Then shall all the princes of the sea come down from their thrones, and lay aside their robes, and their broidered garments shall they put off: with trembling shall they clothe themselves; upon the ground shall they sit, and shall tremble at every moment, and be astonished concerning thee.
17 Sa’an nan za su yi makoki game da ke su ce, “‘Yaya kika hallaka haka nan, ya birnin da ta yi suna, cike da mutanen teku! Ke da kika zama mai ƙarfi cikin tekuna, ke da mazauna cikinki; kin sa tsoronki a kan dukan waɗanda suka zauna a can.
And they shall lift up over thee a lamentation, and say to thee, How art thou lost, that wast inhabited [safely] by reason of the seas: O renowned city, which was strong on the sea, she and her inhabitants, who caused their terror to be on all that dwelt around her!
18 Yanzu tsibirai suna rawar jiki a ranar fāɗuwarki; tsibirai a cikin teku sun tsorata a ɓacewarki.’
Now shall the isles tremble on the day of thy fall; yea, the isles that are in the sea shall be troubled at thy end.
19 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na maishe ki kufai, kamar sauran biranen da ba a ƙara zama a ciki, sa’ad da kuma na kawo zurfafan teku a kanki da yawan ruwansa suka rufe ki,
For thus hath said the Lord Eternal, When I render thee a ruined city, like the cities that are not inhabited; when I bring up over thee the deep, and when the great waters cover thee:
20 a sa’an nan zan sauko da ke ƙasa tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, zuwa wurin mutanen dā. Zan sa ki zauna ƙarƙashin ƙasa, kamar a kufai na tun dā, tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, ba kuwa za ki ƙara dawowa ba ko ki ɗauki matsayinki a ƙasar masu rai.
Then will I bring thee down with those that descend into the pit, unto the people of olden time, and I will cause thee to dwell in the land of the nether world, among ruins of ancient days, with those that go down to the pit, in order that thou mayest not be inhabited; but I will bestow glory in the land of life.
21 Zan sa ki yi mummunan ƙarshe kuma ba za ki ƙara kasancewa ba. Za a neme ki, amma ba za a ƙara same ki ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
As though thou hadst not been will I render thee, and thou shalt be no more: and thou shalt be sought for, but thou shalt never be found any more to eternity, saith the Lord Eternal.

< Ezekiyel 26 >