< Ezekiyel 25 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
І було мені слово Господнє таке:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
„Сину лю́дський, зверни́ своє обличчя до Аммо́нових синів, і пророкуй на них.
3 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
І скажеш Аммо́новим синам: Послухайте слова Господа Бога: Так говорить Господь Бог: За те, що ти говориш „Ага!“про Мою святиню, бо вона збезче́щена, і про Ізраїлеву землю, бо спусто́шена, і про Юдин дім, бо пішов у поло́н,
4 saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
тому́ ось Я дам тебе синам сходу на спа́док, і поставлять вони в тебе ша́тра свої, і зроблять у тебе місця́ свого пробува́ння. Вони будуть їсти твій плід, і вони будуть пити твоє молоко.
5 Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
І дам я Раббу на ста́йню для верблю́дів, а Аммонових синів на лі́гво отари, і ви пізнаєте, що Я — Госпо́дь!
6 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
Бо так Господь Бог промовляє: За твоє пле́скання рукою, і твоє тупотіння ногою, і що в душі ті́шишся ти всією своєю пого́рдою до Ізраілевої землі,
7 saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
тому́ ось Я витягну Свою руку на тебе, і дам тебе на здо́бич для наро́дів, і витну тебе з наро́дів, і ви́гублю тебе з краї́в, знищу тебе, і пізнаєш, що Я — Госпо́дь!
8 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
Так сказав Господь Бог: За те, що Моа́в та Сеїр говорять: „Ось Юдин дім — як усі наро́ди“,
9 saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
тому ось Я відкрию Моа́вове узбіччя від міст, від його міст, від його кінця́, пишно́ту землі: Бен-Гаєшімот, Баал-Меон аж до Кір'ятаїму.
10 Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
Я дам його на спа́док для синів сходу ра́зом з синами Аммо́новими, щоб не згадувались Аммонові сини серед наро́дів.
11 zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
А над Моавом зроблю́ при́суди, і пізнають вони, що Я — Госпо́дь!
12 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
Так говорить Господь Бог: За те, що Едо́м мстився мстою над Юдиним домом, і тяжко гріши́ли, через те, що мсти́лися над ними,
13 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
тому так говорить Господь Бог: І витягну Я руку Свою на Едо́ма, і витну з нього люди́ну й скоти́ну, і вчиню́ його руїною, — від Теману й аж до Дедану вони попа́дають від меча!
14 Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
І дам Я Свою по́мсту над Едомом у руку Мого народу Ізраїля, і вчиню́ в Едомі за гнівом Своїм, за лютістю Своєю, і зазнають вони Моєї по́мсти, говорить Господь Бог!
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
Так говорить Господь Бог: За те, що филисти́мляни чинили в по́мсті, і мстилися мстою через пого́рду в душі, щоб нищити в вічній не́нависті,
16 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
тому так говорить Господь Вог: Ось Я витягну Свою руку на филисти́млян, і витну кере́тян, і вигублю останок морського берега,
17 Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”
і вчиню́ над ними жорсто́кі помсти лютими ка́рами. І пізнають вони, що Я — Господь, коли Я вчиню Свою помсту серед них!“

< Ezekiyel 25 >