< Ezekiyel 25 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
RAB bana şöyle seslendi:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
“İnsanoğlu, yüzünü Ammonlular'a çevir, onlara karşı peygamberlik et.
3 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
Onlara de ki, ‘Egemen RAB'bin sözünü dinleyin! Egemen RAB şöyle diyor: Madem tapınağım kirletildiği, İsrail ülkesi viraneye çevrildiği, Yahuda halkı sürgüne gittiği zaman, Hah, hah! diyerek alay ettiniz,
4 saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
ben de sizi miras olarak doğuda yaşayan halka teslim edeceğim. Obalarını, çadırlarını ülkenizde kuracaklar; ürününüzü yiyecek, sütünüzü içecekler.
5 Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Rabba Kenti'ni develer için otlak, Ammon ülkesini sürüler için ağıl yapacağım. O zaman benim RAB olduğumu anlayacaksınız.
6 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
Egemen RAB şöyle diyor: Madem İsrail'le alay ederek ellerinizi çırptınız, ayaklarınızı yere vurdunuz, bütün yüreğinizle sevindiniz,
7 saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
ben de size karşı elimi uzatacak, çapul malı olarak sizi uluslara teslim edeceğim. Sizi halklar arasından süpürüp atacak, ülkeler arasından söküp çıkaracak, yok edeceğim. O zaman benim RAB olduğumu anlayacaksınız.’”
8 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
“Egemen RAB şöyle diyor: ‘Madem Moav ve Seir halkı, Bakın, Yahuda halkının öteki uluslardan farkı yok, dedi,
9 saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
ben de Moav'ın sınırını, ülkenin süsü olan sınır kentlerini, Beytyeşimot, Baal-Meon ve Kiryatayim'i savunmasız bırakacağım.
10 Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
Ammonlular uluslar arasında bir daha anılmasın diye Moav'ı Ammonlular'la birlikte mülk olarak doğuda yaşayan halka vereceğim.
11 zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
Böylece Moav'ı cezalandıracağım. O zaman benim RAB olduğumu anlayacaklar.’”
12 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
“Egemen RAB şöyle diyor: ‘Madem Edom Yahuda halkından öç alarak büyük suç işledi,
13 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
Egemen RAB şöyle diyor: Ben de Edom'a karşı elimi uzatacak, insanları da hayvanları da yok edecek, ülkeyi viraneye çevireceğim. Teman'dan Dedan'a kadar Edomlular kılıçla vurulup yok olacaklar.
14 Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Halkım İsrail aracılığıyla Edom'dan öç alacağım. İsrailliler onlara öfkem, kızgınlığım uyarınca davranacak. Böylece Edomlular öcümü anlayacaklar. Egemen RAB böyle diyor.’”
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
“Egemen RAB şöyle diyor: ‘Madem Filistliler Yahuda'ya acımasızca davrandılar, eskiden var olan düşmanlıklarıyla onu yerle bir ederek öç aldılar,
16 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
Egemen RAB şöyle diyor: Elimi Filistliler'e karşı uzatacağım, Keretliler'i söküp atacağım, kıyıda yaşayanlardan sağ kalanlarını yok edeceğim.
17 Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”
Onlardan ağır bir öç alacak, onları öfkeyle paylayacağım. Kendilerinden öç alınca, benim RAB olduğumu anlayacaklar.’”

< Ezekiyel 25 >