< Ezekiyel 25 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La palabra de Yahvé vino a mí, diciendo:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
“Hijo de hombre, pon tu rostro hacia los hijos de Amón y profetiza contra ellos.
3 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
Di a los hijos de Amón: “¡Oigan la palabra del Señor Yahvé! El Señor Yahvé dice: “Por cuanto dijisteis: ‘¡Ah!’ contra mi santuario cuando fue profanado, y contra la tierra de Israel cuando fue desolada, y contra la casa de Judá cuando fue en cautiverio,
4 saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
por tanto, he aquí que os entregaré a los hijos del oriente como posesión. Ellos pondrán sus campamentos en ti y harán sus moradas en ti. Comerán tus frutos y beberán tu leche.
5 Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Haré de Rabá un establo para los camellos y de los hijos de Amón un lugar de descanso para los rebaños. Entonces sabrán que yo soy Yahvé”.
6 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
Porque el Señor Yahvé dice: “Por haber batido las manos, estampado los pies y alegrado con todo el desprecio de tu alma contra la tierra de Israel,
7 saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
por lo tanto, he aquí que he extendido mi mano sobre ti y te entregaré como botín a las naciones. Te cortaré de entre los pueblos, y te haré perecer de entre los países. Te destruiré. Entonces sabrás que yo soy Yahvé”.
8 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
“‘Dice el Señor Yahvé: “Porque Moab y Seir dicen: ‘He aquí que la casa de Judá es como todas las naciones’,
9 saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
por lo tanto, he aquí que yo abro el costado de Moab desde las ciudades, desde sus ciudades que están en sus fronteras, la gloria del país, Beth Jeshimoth, Baal Meón y Quiriatáim,
10 Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
a los hijos del oriente, para que vayan contra los hijos de Amón; y se los daré por posesión, para que los hijos de Amón no sean recordados entre las naciones.
11 zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
Ejecutaré juicios sobre Moab. Entonces sabrán que yo soy Yahvé”.
12 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
“‘Dice el Señor Yahvé: “Por cuanto Edom se ha ensañado con la casa de Judá tomando venganza, y ha ofendido en gran manera, y se ha vengado de ellos”,
13 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
por eso dice el Señor Yahvé: “Extenderé mi mano sobre Edom, y cortaré de ella hombres y animales; y la haré desolada desde Temán. Caerán a espada hasta Dedán.
14 Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Yo pondré mi venganza en Edom por mano de mi pueblo Israel. Harán en Edom según mi cólera y según mi ira. Entonces conocerán mi venganza”, dice el Señor Yahvé.
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
“‘El Señor Yahvé dice: “Por cuanto los filisteos se han vengado, y se han vengado con desprecio del alma para destruir con hostilidad perpetua,”
16 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
por lo tanto, el Señor Yahvé dice: “He aquí que yo extiendo mi mano sobre los filisteos, y cortaré a los queretanos, y destruiré el remanente de la costa del mar.
17 Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”
Ejecutaré sobre ellos una gran venganza con reprimendas de ira. Entonces sabrán que yo soy Yahvé, cuando haga mi venganza contra ellos”.

< Ezekiyel 25 >