< Ezekiyel 25 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Beseda Gospodova je ponovno prišla k meni, rekoč:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
»Človeški sin, naravnaj svoj obraz proti Amóncem in prerokuj zoper njih;
3 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
in reci Amóncem: ›Poslušajte besedo Gospoda Boga. Tako govori Gospod Bog, ker praviš: ›Aha, zoper moje svetišče, ko je bilo oskrunjeno; in zoper Izraelovo deželo, ko je bila zapuščena; in zoper Judovo hišo, ko so odšli v ujetništvo; ‹
4 saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
glej, zatorej te bom izročil možem vzhoda za posest in v tebi si bodo postavili svoje palače in svoja prebivališča bodo naredili v tebi. Jedli bodo tvoj sad in pili bodo tvoje mleko.
5 Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
In jaz bom Rabo naredil hlev za kamele in Amónce kraj ležišča za trope, in spoznali boste, da jaz sem Gospod.‹
6 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
Kajti tako govori Gospod Bog: ›Ker si ploskal s svojima rokama in topotal s stopali in se razveseljeval v srcu z vsem svojim prezirom zoper Izraelovo deželo;
7 saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
glej, zato bom nadte iztegnil svojo roko in te izročil v plen poganom; in jaz te bom odrezal izmed ljudstev in ti povzročil, da izgineš iz dežel. Uničil te bom, in vedel boš, da jaz sem Gospod.‹
8 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
Tako govori Gospod Bog: ›Zato ker Moáb in Seír govorita: ›Glej, Judova hiša je podobna vsem poganom; ‹
9 saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
zatorej, glej, odprl bom Moábov bok od mest, od njegovih mest, ki so na njegovih mejah, slavo dežele: Bet Ješimót, Báal Meón in Kirjatájim,
10 Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
do mož vzhoda z Amónci [vred] in jih dal v posest, da se Amóncev ne bo spominjalo med narodi.
11 zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
In izvršil bom sodbe nad Moábom; in spoznali bodo, da jaz sem Gospod.‹
12 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
Tako govori Gospod Bog: ›Zato ker je Edóm zoper Judovo hišo ravnal z maščevanjem in [jih] silno užalil in se maščeval nad njimi; ‹
13 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
zato tako govori Gospod Bog: ›Tudi jaz bom svojo roko iztegnil nad Edóm in iz njega bom iztrebil moža in žival; in opustošil ga bom od Temána; in tisti iz Dedána bodo padli pod mečem.
14 Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
In svoje maščevanje bom položil nad Edóm po roki svojega ljudstva Izraela, in v Edómu bodo storili glede na mojo jezo in glede na mojo razjarjenost; in spoznali bodo moje maščevanje, ‹ govori Gospod Bog.
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
Tako govori Gospod Bog: ›Ker so Filistejci postopali z maščevanjem in so se maščevali s krutim srcem, da ga uničijo zaradi starega sovraštva; ‹
16 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
zato tako govori Gospod Bog: ›Glej, svojo roko bom iztegnil nad Filistejce in iztrebil bom Keretéjce in uničil bom preostanek morske obale.
17 Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”
In nad njimi bom izvršil veliko maščevanje z besnimi grajami; in spoznali bodo, da jaz sem Gospod, ko bom nanje položil svoje maščevanje.‹«

< Ezekiyel 25 >