< Ezekiyel 25 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Og Herrens ord kom til mig, og det lød så:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
Menneskesønn! Vend ditt åsyn mot Ammons barn og spå mot dem!
3 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
Si til Ammons barn: Hør Herrens, Israels Guds ord! Så sier Herren, Israels Gud: Fordi du ropte: Ha, ha! over min helligdom, som er blitt vanhelliget, og over Israels land, som er blitt ødelagt, og over Judas hus, som er ført bort i fangenskap,
4 saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
se, derfor vil jeg la Østens sønner få dig til eie, og de skal slå op sine teltleire i dig og sette op sine boliger i dig; de skal ete din frukt og drikke din melk.
5 Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Og jeg vil gjøre Rabba til beitemark for kameler og Ammons barns land til hvileplass for småfe, og I skal kjenne at jeg er Herren.
6 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
For så sier Herren, Israels Gud: Fordi du klappet i hendene og stampet med føttene og gledet dig med dyp forakt av hele ditt hjerte over Israels land,
7 saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
se, derfor rekker jeg min hånd ut imot dig og gir dig til føde for folkene; jeg utrydder dig av folkene og utsletter dig av landene; jeg vil gjøre dig til intet, og du skal kjenne at jeg er Herren.
8 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
Så sier Herren, Israels Gud: Fordi Moab og Se'ir sa: Se, det er gått med Judas hus som med alle de andre folk,
9 saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
se, derfor vil jeg åpne Moabs side helt fra byene, fra dets byer på alle kanter, den fagreste del av landet, Bet-Jesimot, Ba'al-Meon og like til Kirjata'im,
10 Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
så Østens sønner kan slippe inn, likesom jeg vil gjøre med Ammons barns land, som jeg gir dem til eie, forat Ammons barns land ikke mere skal kommes i hu blandt folkene.
11 zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
Jeg vil holde dom over Moab, og de skal kjenne at jeg er Herren.
12 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
Så sier Herren, Israels Gud: Fordi Edom tok hevn over Judas hus og førte skyld over sig ved å hevne sig på dem,
13 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
derfor sier Herren, Israels Gud, så: Jeg vil rekke min hånd ut imot Edom og utrydde der både folk og fe, og jeg vil gjøre det til en ørken helt fra Teman, og like til Dedan skal de falle for sverdet.
14 Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Og jeg vil fullbyrde min hevn på Edom ved mitt folk Israels hånd, og de skal gjøre med Edom efter min vrede og harme, og de skal få kjenne min hevn, sier Herren, Israels Gud.
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
Så sier Herren, Israels Gud: Fordi filistrene tok hevn, fordi de hevnet sig med forakt av hele sitt hjerte for å ødelegge på grunn av eldgammelt fiendskap,
16 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
derfor sier Herren, Israels Gud, så: Se, jeg rekker min hånd ut imot filistrene og utrydder kreterne og utsletter det som er igjen ved havets strand.
17 Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”
Jeg vil ta stor hevn over dem og tukte dem i min vrede, og de skal kjenne at jeg er Herren, når jeg fullbyrder min hevn på dem.

< Ezekiyel 25 >