< Ezekiyel 25 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l'Éternel me fut adressée, en ces termes:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
Fils de l'homme, tourne ta face vers les enfants d'Ammon, et prophétise contre eux.
3 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
Dis aux enfants d'Ammon: Écoutez la parole du Seigneur, l'Éternel. Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Parce que tu as dit: ah! ah! à propos de mon sanctuaire, quand il fut profané, et du pays d'Israël, quand il fut dévasté, et de la maison de Juda, lorsqu'elle se rendit en captivité,
4 saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
Voici, je te livre aux enfants de l'Orient. Ils établiront au milieu de toi leurs parcs, et ils y placeront leurs demeures; ils mangeront tes fruits, et ils boiront ton lait.
5 Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
De Rabba, je ferai un pâturage pour les chameaux, et du pays des enfants d'Ammon, un bercail pour les moutons, et vous saurez que je suis l'Éternel.
6 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
Car ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Parce que tu as battu des mains et frappé du pied, que tu t'es réjoui avec dédain en ton âme, au sujet du pays d'Israël,
7 saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
Voici, j'étends ma main sur toi et je te livre en proie aux nations; je te retranche d'entre les peuples, je te fais disparaître d'entre les pays, je t'extermine, et tu sauras que je suis l'Éternel.
8 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Parce que Moab et Séïr ont dit: voici, il en est de la maison de Juda comme de toutes les nations;
9 saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
A cause de cela, voici, j'ouvre le flanc de Moab, du côté de ses villes, ses villes frontières, l'ornement du pays, Beth-Jéshimoth, Baal-Méon et Kirjathaïm;
10 Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
Je l'ouvre aux enfants de l'Orient, qui marchent contre les enfants d'Ammon, et je le leur donne en possession, afin que les enfants d'Ammon ne soient plus rangés au nombre des nations.
11 zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
J'exercerai mes jugements contre Moab et ils sauront que je suis l'Éternel.
12 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Parce qu'Édom s'est livré à la vengeance à l'égard de la maison de Juda, et s'est rendu coupable en se vengeant d'elle,
13 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: J'étends ma main sur Édom; j'en extermine hommes et bêtes; je le réduis en désert; de Théman à Dédan ils tomberont par l'épée.
14 Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
J'exercerai ma vengeance sur Édom par la main de mon peuple d'Israël, et ils traiteront Édom selon ma colère et selon ma fureur; ils sauront ce qu'est ma vengeance, dit le Seigneur, l'Éternel.
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Parce que les Philistins ont agi par vengeance, et qu'ils se sont vengés inhumainement, avec mépris, et selon leur désir, jusqu'à tout détruire dans une haine éternelle,
16 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
A cause de cela, ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Voici, j'étends ma main sur les Philistins, et j'extermine les Kéréthiens, et je fais périr ce qui reste sur la côte de la mer.
17 Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”
J'exercerai sur eux de grandes vengeances par des châtiments pleins de fureur, et ils sauront que je suis l'Éternel, quand j'exécuterai contre eux ma vengeance.

< Ezekiyel 25 >