< Ezekiyel 25 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l’Éternel vint à moi, disant:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
Fils d’homme, tourne ta face vers les fils d’Ammon, et prophétise contre eux,
3 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
et dis aux fils d’Ammon: Écoutez la parole du Seigneur, l’Éternel! Ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Parce que tu as dit: Ha ha! contre mon sanctuaire, quand il a été profané, et contre la terre d’Israël, quand elle a été désolée, et contre la maison de Juda, quand elle est allée en captivité:
4 saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
à cause de cela, voici, je te donne en possession aux fils de l’orient, et ils établiront chez toi leurs parcs, et placeront chez toi leurs demeures; ils mangeront tes fruits et boiront ton lait.
5 Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Et je ferai de Rabba un pâturage pour les chameaux, et [du pays] des fils d’Ammon un gîte pour le menu bétail; et vous saurez que je suis l’Éternel.
6 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
Car ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Parce que tu as battu des mains et que tu as frappé du pied, et que tu t’es réjoui dans tout le mépris que tu avais en ton âme contre la terre d’Israël, –
7 saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
à cause de cela, voici, j’étendrai ma main sur toi et je te livrerai en proie aux nations, et je te retrancherai d’entre les peuples, et je te ferai périr d’entre les pays; je te détruirai, et tu sauras que je suis l’Éternel.
8 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
Ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Parce que Moab et Séhir ont dit: Voici, la maison de Juda est comme toutes les nations;
9 saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
à cause de cela, voici, j’ouvre le côté de Moab par les villes, par ses villes, jusqu’à la dernière, la gloire du pays, Beth-Jeshimoth, Baal-Méon, et Kiriathaïm;
10 Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
[je l’ouvre] aux fils de l’orient, avec [le pays] des fils d’Ammon; et je le leur donnerai en possession, afin qu’on ne se souvienne plus des fils d’Ammon parmi les nations;
11 zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
et j’exécuterai des jugements sur Moab; et ils sauront que je suis l’Éternel.
12 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
Ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: À cause de ce qu’Édom a fait quand il s’est vengé cruellement de la maison de Juda, et parce qu’il s’est rendu fort coupable en se vengeant d’eux, –
13 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
à cause de cela, ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: J’étendrai ma main aussi sur Édom, et j’en retrancherai hommes et bêtes, et j’en ferai un désert depuis Théman, et, jusqu’à Dedan, ils tomberont par l’épée;
14 Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
et j’exercerai ma vengeance sur Édom par la main de mon peuple Israël; et ils agiront en Édom selon ma colère et selon ma fureur; et ils connaîtront ma vengeance, dit le Seigneur, l’Éternel.
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
Ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: À cause de ce que les Philistins ont fait par vengeance, et parce qu’ils se sont vengés cruellement, dans le mépris de leurs âmes, pour détruire par une inimitié perpétuelle, –
16 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
à cause de cela, ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Voici, j’étends ma main sur les Philistins, et je retrancherai les Keréthiens, et je ferai périr le reste qui est sur le bord de la mer;
17 Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”
et j’exercerai sur eux de grandes vengeances par des châtiments de fureur; et ils sauront que je suis l’Éternel, quand j’exécuterai sur eux ma vengeance.