< Ezekiyel 25 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l'Éternel me fut adressée, en ces mots:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
Fils d'homme, tourne ta face vers les fils d'Ammon, et prophétise contre eux.
3 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
Dis aux enfants d'Ammon: « Écoute la parole du Seigneur Yahvé! Le Seigneur Yahvé dit: « Parce que vous avez dit: « Ah! » contre mon sanctuaire quand il a été profané, contre le pays d'Israël quand il a été dévasté, et contre la maison de Juda quand elle est allée en captivité,
4 saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
voici que je vous livre aux fils de l'Orient pour qu'ils vous possèdent. Ils établiront chez toi leurs campements et y feront leurs demeures. Ils mangeront tes fruits et boiront ton lait.
5 Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Je ferai de Rabba une étable pour les chameaux et des fils d'Ammon un lieu de repos pour les troupeaux. Alors vous saurez que je suis Yahvé ».
6 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
Car le Seigneur Yahvé dit: « Parce que tu as battu des mains, tapé des pieds, et que tu t'es réjoui avec tout le mépris de ton âme contre le pays d'Israël,
7 saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
voici que j'étends ma main sur toi, et je te livre au pillage des nations. Je te retrancherai du milieu des peuples, et je te ferai périr hors des pays. Je te détruirai. Alors vous saurez que je suis Yahvé. »
8 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
« Le Seigneur Yahvé dit: « Parce que Moab et Séir disent: Voici la maison de Juda comme toutes les nations,
9 saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
voici, j'ouvrirai le côté de Moab, depuis ses villes, depuis les villes qui sont sur ses frontières, la gloire du pays, Beth Jeshimoth, Baal Meon et Kiriathaim,
10 Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
vers les fils de l'Orient, pour aller contre les fils d'Ammon; et je les donnerai en possession, afin qu'on ne se souvienne pas des fils d'Ammon parmi les nations.
11 zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
J'exécuterai des jugements sur Moab. Alors ils sauront que je suis Yahvé. »
12 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
"'Le Seigneur Yahvé dit: « Parce qu'Édom a traité la maison de Juda en se vengeant, parce qu'il l'a gravement offensée et s'est vengé d'elle, »
13 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
c'est pourquoi le Seigneur Yahvé dit: « J'étendrai ma main sur Édom, j'en exterminerai l'homme et le bétail, et je le réduirai en désert depuis Théman. Ils tomberont par l'épée jusqu'à Dedan.
14 Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
J'exercerai ma vengeance sur Édom par la main de mon peuple d'Israël. On fera à Édom selon ma colère et selon ma fureur. Alors ils connaîtront ma vengeance, dit le Seigneur Yahvé.
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
"'Le Seigneur Yahvé dit: « Parce que les Philistins se sont vengés, et qu'ils se sont vengés avec mépris de l'âme pour détruire avec une hostilité perpétuelle, »
16 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
c'est pourquoi le Seigneur Yahvé dit: « Voici, j'étendrai ma main sur les Philistins, j'exterminerai les Chéréthiens, et je détruirai le reste de la côte maritime.
17 Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”
J'exercerai sur eux une grande vengeance, avec des châtiments violents. Alors ils sauront que je suis Yahvé, quand j'exercerai sur eux ma vengeance. »''

< Ezekiyel 25 >