< Ezekiyel 25 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord was maad to me,
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
and he seide, Thou, sone of man, sette thi face ayens the sones of Amon, and thou schalt profesie of hem.
3 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
And thou schalt seie to the sones of Amon, Here ye the word of the Lord God; the Lord God seith these thingis, For that that ye seiden, Wel! wel! on my seyntuarie, for it is defoulid, and on the lond of Israel, for it is maad desolat, and on the hous of Juda, for thei ben led in to to caitifte; lo!
4 saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
therfor Y schal yyue thee the sones of the eest in to eritage, and thei schulen sette her foldis in thee, and thei shulen sette her tentis in thee; thei schulen ete thi fruytis, and thei schulen drynke thi mylk.
5 Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
And Y schal yyue Rabath in to a dwellyng place of camels, and the sones of Amon in to a bed of beestis; and ye schulen wite, that Y am the Lord.
6 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
For the Lord God seith these thingis, For that that thou flappidist with hond, and smytidist with the foot, and ioyedist of al desijr on the lond of Israel;
7 saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
therfor lo! Y schal stretche forth myn hond on thee, and Y schal yyue thee in to rauyschyng of hethene men, and Y schal sle thee fro puplis, and Y schal leese thee, and al to-breke thee fro londis; and ye schulen wite, that Y am the Lord.
8 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
The Lord God seith these thingis, For that that Moab and Seir seiden, Lo! the hous of Juda is as alle folkis; therfor lo!
9 saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
Y schal opene the schuldre of Moab of citees, sotheli of citees therof and of the endis therof, the noble citees of the lond, Bethiesmoth, and Beelmoth,
10 Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
and Cariathaym, to the sones of the eest, with the sones of Amon. And Y schal yyue it in to eritage, that mynde of the sones of Amon be no more among hethene men,
11 zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
and in Moab Y schal make domes; and thei schulen wite, that Y am the Lord.
12 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
The Lord God seith these thingis, For that that Ydumee dide veniaunce, that it avengide it silf of the sones of Juda, and synnede doynge trespas, and axide greetli veniaunce of hem;
13 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
therfor the Lord God seith these thingis, Y schal stretche forth myn hond on Idumee, and Y schal take awei fro it man and beeste, and Y schal make it desert of the south; and thei that ben in Dedan schulen falle bi swerd.
14 Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
And Y schal yyue my veniaunce on Idumee, bi the hond of my puple Israel; and thei schulen do in Edom bi my wraththe, and bi my strong veniaunce; and thei schulen knowe my veniaunce, seith the Lord God.
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
The Lord God seith these thingis, For that that Palestyns diden veniaunce, and auengiden hem silf, with al wille sleynge, and fillynge elde enemytees;
16 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
therfor the Lord God seith these thingis, Lo! Y schal stretche forth myn hond on Palestyns, and Y schal sle sleeris, and Y schal leese the remenauntis of the se coost;
17 Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”
and Y schal make grete veniaunces in hem, and Y schal repreue in strong veniaunce; and thei schulen wite, that Y am the Lord, whanne Y schal yyue my veniaunce on hem.

< Ezekiyel 25 >