< Ezekiyel 25 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
I dođe mi riječ Jahvina:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
“Sine čovječji, okreni lice k sinovima Amonovim te prorokuj protiv njih!
3 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
Reci sinovima Amonovim: 'Poslušajte riječ Jahve Gospoda! Ovako govori Jahve Gospod: Zato što vi klicaste 'ha, ha!' nad mojim Svetištem kad ono bijaše oskvrnuto, i nad zemljom Izraelovom kad ona bijaše opustošena, i nad domom Judinim kad odlažaše u izgnanstvo,
4 saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
predat ću vas, evo, u posjed sinovima Istoka da usred vas razapnu svoje šatore, udare svoja prebivališta. Oni neka jedu tvoje plodove i piju mlijeko tvoje!
5 Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Od Rabe ću pašnjake za deve načiniti, a u zemlji Amonovih sinova torove ću za ovce podići. I znat ćete da sam ja Jahve!'
6 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
Jer ovako govori Jahve Gospod: 'Zato što si pljeskao rukama i udarao nogama i svom se dušom radovao nad zemljom Izraelovom,
7 saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
ja ću, evo, ruku na te podići i kao plijen te predati narodima! Istrijebit ću te iz narodÄa, iskorijeniti iz zemalja! Zatrijet ću te! I znat ćeš da sam ja Jahve!
8 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
Ovako govori Jahve Gospod: 'Zato što Moab i Seir govorahu: 'Gle, dom je Judin poput svih naroda',
9 saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
otkrit ću, evo, obronke moapske, da s kraja na kraj ostane bez gradova što bijahu ukras zemlje: Bet Haješimot, Baal Meon i Kirjatajim.
10 Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
Dat ću ih u posjed sinovima Istoka, neprijateljima Amonaca, da se sinovi Amonovi među narodima više ne spominju!
11 zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
Tako ću izvršiti sud nad Moabom. I znat će da sam ja Jahve!'
12 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
Ovako govori Jahve Gospod: 'Zato što se Edom osveti domu Judinu i tom se osvetom teško ogriješi,
13 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
ovako govori Jahve Gospod: Podići ću ruku na Edom, istrijebit ću iz njega ljude i životinje! Pretvorit ću ga u pustinju: od Temana do Dedana svi će od mača izginuti.
14 Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Tako ću se osvetiti Edomu rukom svojega naroda izraelskog. Oni će postupiti s Edomom prema mojem gnjevu i mojoj srdžbi. I spoznat će moju osvetu!' - riječ je Jahve Gospoda.
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
Ovako govori Jahve Gospod: 'Zato što Filistejci izvršiše odmazdu, krvavo se osvećujući s mržnjom u srcu, razarajući sve zbog svojeg neprijateljstva,
16 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
ovako govori Jahve Gospod: Evo, podižem ruku na Filistejce, istrijebit ću Kerećane, uništit ću sve što preostane na morskoj obali!
17 Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”
Tako ću im se strašno osvetiti kaznama jarosnim. I kad im se osvetim, znat će da sam ja Jahve.'”