< Ezekiyel 24 >

1 A shekara ta tara, a wata na goma, a rana ta goma, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Or en la neuvième année, au dixième jour du dixième mois, la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
2 “Ɗan mutum, ka rubuta wannan rana, wannan rana, domin sarkin Babilon ya yi ƙawanya wa Urushalima a wannan rana.
Fils d'homme, écris-toi le nom de ce jour, de ce propre jour; [car] en ce même jour le Roi de Babylone s'est approché contre Jérusalem.
3 Ka faɗa wa wannan gidan’yan tawaye wani misali ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka sa tukunyar dahuwa; ka sa ta a kan wuta ka kuma zuba ruwa a cikinta.
Mets donc en avant une similitude à la maison rebelle, et leur dis: Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: mets, mets la chaudière, et verse de l'eau dedans.
4 Ka sa gunduwoyin nama a cikinta dukan gunduwoyi masu kyau, cinya da kafaɗa. Ka cika ta da waɗannan ƙasusuwa mafi kyau;
Assemble ses pièces dans elle, toutes les bonnes pièces, la cuisse, et l'épaule, et la remplis des meilleurs os.
5 ka kama mafi kyau daga cikin garken. Ka tara itace a ƙarƙashinta saboda ƙasusuwan; ka sa ta tafasa ka kuma dafa ƙasusuwan a cikinta.
Prends la meilleure bête du troupeau, et fais brûler des os sous la chaudière, fais-la bouillir à gros bouillons, et que les os cuisent dans elle.
6 “‘Gama wannan shi ne abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini, ga tukunya wadda take da tsatsa, wadda tsatsarta ba za tă fita ba! Ka fitar da shi gunduwa-gunduwa ba tare da jefa ƙuri’a a kansu ba.
Car ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: malheur à la ville sanguinaire, à la chaudière dans laquelle est son écume, et de laquelle l'écume n'est point sortie; vide-la pièce après pièce; et que le sort ne soit point jeté sur elle.
7 “‘Gama zubar da jini yana a tsakiyarta, ta zubar da shi a dutsen da yake a fili; ba tă zubar da shi a ƙasa ba, inda ƙura za tă rufe shi.
Parce que son sang est au milieu d'elle, qu'elle l'a mis sur la pierre sèche, [et] qu'elle ne l'a point répandu sur la terre pour le couvrir de poussière.
8 Don a zuga hasala a kuma yi sakayya na sa jininta a dutsen da ba a rufe ba, saboda kada a rufe.
J'ai mis son sang sur une pierre sèche, afin qu'il ne soit point couvert, pour faire monter la fureur, [et] pour en prendre vengeance.
9 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini! Ni ma zan jibge itace da yawa.
C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: malheur à la ville sanguinaire; j'en ferai aussi un grand tas de bois à brûler.
10 Ka tula gumagumai ka kuma ƙuna wuta. Ka dafa naman da kyau, kana haɗawa da yaji; ka kuma bar ƙasusuwan su ƙone.
Amasse beaucoup de bois, allume le feu, fais cuire la chair entièrement, et la fais consumer, et que les os soient brûlés.
11 Sa’an nan ka sa tukunyan nan da babu kome a kan garwashi sai ta yi zafi har darmarta ta yi ja wur domin dattinta ya narke tsatsarta kuma ta ƙone.
Puis mets sur les charbons ardents la chaudière toute vide, afin qu'elle s'échauffe, et que son airain se brûle, et que son ordure soit fondue au dedans d'elle, [et] que son écume soit consumée.
12 Ta gajiyar da dukan ƙoƙari; ba a fid da tsatsarta nan mai yawa ba, kai, ko a wuta ma.
Elle m'a travaillé par des mensonges, et sa grosse écume n'est point sortie d'elle; son écume s'en ira au feu.
13 “‘Yanzu ƙazantarki ita ce lalaci. Domin na yi ƙoƙari in tsabtacce ke amma ba ki tsabtattu daga ƙazantarki ba, ba za ki ƙara yin tsabta ba sai hasalata a kanki ya kwanta.
[Il y a] de l'énormité en ta souillure; car je t'avais purifiée, et tu n'as point été nette; tu ne seras point encore nettoyée de ta souillure, jusqu'à ce que j'aie satisfait ma fureur sur toi.
14 “‘Ni Ubangiji na faɗa. Lokaci ya zo da zan aikata. Ba zan janye ba; ba zan ji tausayi ba, ba kuwa zan bari ba. Za a hukunta ki bisa ga hali da ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Moi l'Eternel j'ai parlé, cela arrivera, et je [le] ferai; et je ne me retirerai point en arrière, je n'épargnerai point, et je ne serai point apaisé. On t'a jugée selon ton train, et selon tes actions, dit le Seigneur l'Eternel.
15 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
16 “Ɗan mutum, da farat ɗaya ina gab da ɗauke abin da idanunka suke jin daɗin gani. Duk da haka kada ka yi makoki ko ka yi kuka ko ka zub da hawaye.
Fils d'homme, voici, je vais t'ôter par une plaie ce que tes yeux voient avec le plus de plaisir; mais n'en mène point de deuil, et ne pleure point, ne fais point couler tes larmes.
17 Ka yi nishi shiru; kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka ka kuma sa takalmanka a ƙafa; kada ka rufe sashen fuskarka daga ƙasa ko ka ci abincin da masu kuka sukan ci.”
Garde-toi de gémir, et ne mène point le deuil qu'on a accoutumé de mener sur les morts; laisse ton bonnet sur ta tête, et mets tes souliers à tes pieds, et ne cache point la lèvre de dessus, et ne mange point le pain des autres.
18 Da gari ya waye, sai na yi magana da mutane, da yamma kuwa matata ta rasu. Kashegari na yi yadda aka umarce ni.
Je parlai donc au peuple le matin, et ma femme mourut le soir; et le [lendemain] matin je fis comme il m'avait été commandé.
19 Sai mutane suka tambaye ni suka ce, “Ba za ka faɗa mana abin da waɗannan abubuwa suke nufi a gare mu ba?”
Et le peuple me dit: ne nous déclareras-tu point ce que nous signifient ces choses-là que tu fais?
20 Sai na ce musu, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
Et je leur répondis: la parole de l'Eternel m'a été [adressée], en disant:
21 faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da ƙazantar da wuri mai tsarkina, kagarar da kuke taƙama, abin da idanunku suke jin daɗin gani, abin faranta zuciyarku.’Ya’yanku maza da mata waɗanda kun bari a baya za su mutu ta wurin takobi.
Dis à la maison d'Israël: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: voici, je m'en vais profaner mon Sanctuaire, la magnificence de votre force, ce qui est le plus agréable à vos yeux, ce que vous voudriez qu'on épargnât sur toutes choses; et vos fils et vos filles, que vous aurez laissés, tomberont par l'épée.
22 Za ku kuma yi yadda na yi. Ba za ku rufe sashe ƙasa na fuskarku ko ku ci abinci da masu kuka sukan ci ba.
Vous ferez alors comme j'ai fait; vous ne couvrirez point vos lèvres, et vous ne mangerez point le pain des autres.
23 Za ku naɗa rawunanku a kai ku sa takalmanku a ƙafafunku. Ba za ku yi kuka ko makoki ba amma za ku lalace saboda zunubanku ku kuma yi ta yin nishi.
Et vos bonnets seront sur vos têtes, et vos souliers à vos pieds; vous ne mènerez point de deuil, ni ne pleurerez; mais vous fondrez à cause de vos iniquités, et vous gémirez les uns avec les autres.
24 Ezekiyel zai zama alama gare ku; za ku yi daidai yadda ya yi. Sa’ad da wannan ya faru, za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’
Et Ezéchiel vous sera pour un signe; vous ferez selon toutes les choses qu'il a faites; [et] quand cela sera arrivé, vous connaîtrez que je suis le Seigneur l'Eternel.
25 “Kai kuma ɗan mutum, a ranar da zan ɗauke musu kagararsu, farin cikinsu da darajarsu, abin da idanunsu ke jin daɗin gani, abin da yake faranta musu zuciya, da kuka’ya’yansu maza da mata,
Et quant à toi, fils d'homme, au jour que je leur ôterai leur force, la joie de leur ornement, l'objet le plus agréable à leurs yeux, et l'objet de leurs cœurs, leurs fils et leurs filles;
26 a ranan nan wanda ya tsere zai zo don yă ba ka labari.
En ce même jour-là quelqu'un qui sera échappé ne viendra-t-il pas vers toi pour te le raconter?
27 A lokacin bakinka zai buɗe, za ka yi magana da shi ba kuwa za ka ƙara yin shiru ba. Ta haka za ka zama alama gare su, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.”
En ce jour-là ta bouche sera ouverte envers celui qui sera échappé, et tu parleras, et ne seras plus muet; ainsi tu leur seras pour un signe, et ils sauront que je suis l'Eternel.

< Ezekiyel 24 >