< Ezekiyel 24 >

1 A shekara ta tara, a wata na goma, a rana ta goma, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Dans la neuvième année, le dixième jour du dixième mois, la parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
2 “Ɗan mutum, ka rubuta wannan rana, wannan rana, domin sarkin Babilon ya yi ƙawanya wa Urushalima a wannan rana.
"Fils de l’homme, note-toi le nom de ce jour, du jour même où nous sommes: le roi de Babylone prend le contact de Jérusalem aujourd’hui même.
3 Ka faɗa wa wannan gidan’yan tawaye wani misali ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka sa tukunyar dahuwa; ka sa ta a kan wuta ka kuma zuba ruwa a cikinta.
Imagine aussi une parabole à l’endroit de la maison de rébellion; tu leur diras: Ainsi parle le Seigneur Dieu: Pose la marmite, pose-la, et puis verses-y de l’eau.
4 Ka sa gunduwoyin nama a cikinta dukan gunduwoyi masu kyau, cinya da kafaɗa. Ka cika ta da waɗannan ƙasusuwa mafi kyau;
Rassembles-y les morceaux, rien que de bons morceaux, cuisse et épaule, remplis-la d’os excellents.
5 ka kama mafi kyau daga cikin garken. Ka tara itace a ƙarƙashinta saboda ƙasusuwan; ka sa ta tafasa ka kuma dafa ƙasusuwan a cikinta.
Prends ce qu’il y a de mieux dans les agneaux, fais aussi cuire les os par dessous; qu’elle bouille à gros bouillons, pour que les os également puissent y cuire.
6 “‘Gama wannan shi ne abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini, ga tukunya wadda take da tsatsa, wadda tsatsarta ba za tă fita ba! Ka fitar da shi gunduwa-gunduwa ba tare da jefa ƙuri’a a kansu ba.
C’Est pourquoi, ainsi parle le Seigneur Dieu: Malheur, ô ville de sang, marmite à laquelle la crasse reste fixée, qui n’a pas été débarrassée de sa crasse! Qu’on la vide morceau par morceau, sans que le sort ait à intervenir à son sujet.
7 “‘Gama zubar da jini yana a tsakiyarta, ta zubar da shi a dutsen da yake a fili; ba tă zubar da shi a ƙasa ba, inda ƙura za tă rufe shi.
Car le sang qu’elle a versé est demeuré au milieu d’elle; elle l’a jeté sur une roche aride, elle ne l’a pas répandu sur le sol, de façon à le recouvrir de terre.
8 Don a zuga hasala a kuma yi sakayya na sa jininta a dutsen da ba a rufe ba, saboda kada a rufe.
C’Est pour faire éclater la colère, pour en tirer vengeance que j’ai exposé son sang sur une roche aride, où il ne pouvait être recouvert.
9 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini! Ni ma zan jibge itace da yawa.
C’Est pourquoi, ainsi parle le Seigneur Dieu: Malheur, ô ville de sang! Moi aussi j’élèverai un grand bûcher.
10 Ka tula gumagumai ka kuma ƙuna wuta. Ka dafa naman da kyau, kana haɗawa da yaji; ka kuma bar ƙasusuwan su ƙone.
Qu’on accumule le bois, qu’on allume le feu, qu’on consume la viande, qu’on brouille la mixture et que les os soient carbonisés!
11 Sa’an nan ka sa tukunyan nan da babu kome a kan garwashi sai ta yi zafi har darmarta ta yi ja wur domin dattinta ya narke tsatsarta kuma ta ƙone.
Puis, qu’on la pose à vide sur ses charbons, afin qu’elle s’échauffe, que s’embrase son cuivre, que son impureté fonde au dedans et que sa crasse disparaisse.
12 Ta gajiyar da dukan ƙoƙari; ba a fid da tsatsarta nan mai yawa ba, kai, ko a wuta ma.
Elle a coûté de vains efforts, l’abondance de sa crasse n’en sort pas: au feu sa crasse!
13 “‘Yanzu ƙazantarki ita ce lalaci. Domin na yi ƙoƙari in tsabtacce ke amma ba ki tsabtattu daga ƙazantarki ba, ba za ki ƙara yin tsabta ba sai hasalata a kanki ya kwanta.
II y a de l’infamie dans ton impureté: puisque j’ai cherché à t’épurer et que tu n’es pas devenue pure, tu ne te débarrasseras plus de ton impureté, jusqu’à ce que j’aie assouvi ma colère sur toi.
14 “‘Ni Ubangiji na faɗa. Lokaci ya zo da zan aikata. Ba zan janye ba; ba zan ji tausayi ba, ba kuwa zan bari ba. Za a hukunta ki bisa ga hali da ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Moi, le Seigneur, j’ai parlé; cela arrivera, je l’accomplirai; je ne me raviserai point, je n’aurai ni pitié ni regret. Selon tes voies et selon tes actes, on te jugera, dit le Seigneur Dieu."
15 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
16 “Ɗan mutum, da farat ɗaya ina gab da ɗauke abin da idanunka suke jin daɗin gani. Duk da haka kada ka yi makoki ko ka yi kuka ko ka zub da hawaye.
"Fils de l’homme, je vais t’enlever les délices de tes yeux par un coup soudain; mais tu ne te lamenteras pas, tu ne pleureras pas et tes larmes ne couleront pas.
17 Ka yi nishi shiru; kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka ka kuma sa takalmanka a ƙafa; kada ka rufe sashen fuskarka daga ƙasa ko ka ci abincin da masu kuka sukan ci.”
Soupire en silence, ne prends pas le deuil comme pour des morts; attache sur toi ta coiffure, mets tes chaussures à tes pieds. Tu ne t’envelopperas pas jusqu’aux lèvres et tu ne mangeras pas le pain des hommes.
18 Da gari ya waye, sai na yi magana da mutane, da yamma kuwa matata ta rasu. Kashegari na yi yadda aka umarce ni.
Je parlai au peuple le matin, et le soir ma femme mourut; le lendemain matin je fis comme il m’avait été ordonné.
19 Sai mutane suka tambaye ni suka ce, “Ba za ka faɗa mana abin da waɗannan abubuwa suke nufi a gare mu ba?”
Le peuple me dit: "Ne nous expliqueras-tu pas ce que signifie pour nous ta manière d’agir?"
20 Sai na ce musu, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
Je leur répondis: "La parole de l’Eternel m’a été adressée en ces termes:
21 faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da ƙazantar da wuri mai tsarkina, kagarar da kuke taƙama, abin da idanunku suke jin daɗin gani, abin faranta zuciyarku.’Ya’yanku maza da mata waɗanda kun bari a baya za su mutu ta wurin takobi.
Dis à la maison d’Israël: Ainsi parle le Seigneur Dieu: Je vais profaner mon sanctuaire, votre orgueil et votre force, les délices de vos yeux, l’objet de votre amour; et vos fils et vos filles que vous avez laissés tomberont sous l’épée.
22 Za ku kuma yi yadda na yi. Ba za ku rufe sashe ƙasa na fuskarku ko ku ci abinci da masu kuka sukan ci ba.
Et vous ferez comme j’ai fait; vous ne vous envelopperez point jusqu’aux lèvres, et vous ne mangerez pas le pain des hommes.
23 Za ku naɗa rawunanku a kai ku sa takalmanku a ƙafafunku. Ba za ku yi kuka ko makoki ba amma za ku lalace saboda zunubanku ku kuma yi ta yin nishi.
Votre coiffure restera sur votre tête et vos chaussures à vos pieds; vous ne vous lamenterez point et ne pleurerez point; mais vous vous consumerez par vos fautes et vous geindrez l’un en présence de l’autre.
24 Ezekiyel zai zama alama gare ku; za ku yi daidai yadda ya yi. Sa’ad da wannan ya faru, za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’
Et Ézéchiel vous servira de symbole: tout ce qu’il a fait, vous l’imiterez; quand cela arrivera, vous saurez que je suis le Seigneur Dieu."
25 “Kai kuma ɗan mutum, a ranar da zan ɗauke musu kagararsu, farin cikinsu da darajarsu, abin da idanunsu ke jin daɗin gani, abin da yake faranta musu zuciya, da kuka’ya’yansu maza da mata,
Pour toi, fils de l’homme, certes, le jour où je leur prendrai le boulevard de leur force, la joie de leur parure, les délices de leurs yeux et l’attrait de leur âme, leurs fils et leurs filles,
26 a ranan nan wanda ya tsere zai zo don yă ba ka labari.
ce jour-là, il viendra un fuyard auprès de toi pour l’annoncer aux oreilles de tous.
27 A lokacin bakinka zai buɗe, za ka yi magana da shi ba kuwa za ka ƙara yin shiru ba. Ta haka za ka zama alama gare su, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.”
Ce jour-là, ta bouche s’ouvrira avec celle du fuyard, tu parleras et ne seras plus réduit au mutisme; tu leur serviras de symbole, et ils sauront que je suis l’Eternel."

< Ezekiyel 24 >