< Ezekiyel 24 >

1 A shekara ta tara, a wata na goma, a rana ta goma, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l’Éternel vint à moi, en la neuvième année, au dixième mois, le dixième [jour] du mois, disant:
2 “Ɗan mutum, ka rubuta wannan rana, wannan rana, domin sarkin Babilon ya yi ƙawanya wa Urushalima a wannan rana.
Fils d’homme, écris pour toi le nom de ce jour, de ce propre jour: le roi de Babylone s’approche contre Jérusalem, en ce jour même.
3 Ka faɗa wa wannan gidan’yan tawaye wani misali ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka sa tukunyar dahuwa; ka sa ta a kan wuta ka kuma zuba ruwa a cikinta.
Et propose une parabole à la maison rebelle, et dis-leur: Ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Place la marmite, place-la, et verses-y aussi de l’eau.
4 Ka sa gunduwoyin nama a cikinta dukan gunduwoyi masu kyau, cinya da kafaɗa. Ka cika ta da waɗannan ƙasusuwa mafi kyau;
Rassembles-y ses morceaux, tous les bons morceaux, la cuisse et l’épaule; remplis-la d’os choisis,
5 ka kama mafi kyau daga cikin garken. Ka tara itace a ƙarƙashinta saboda ƙasusuwan; ka sa ta tafasa ka kuma dafa ƙasusuwan a cikinta.
prends du meilleur du menu bétail; et [mets] aussi dessous un tas de bois pour les os; fais-la bien bouillir, et que les os cuisent au-dedans d’elle.
6 “‘Gama wannan shi ne abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini, ga tukunya wadda take da tsatsa, wadda tsatsarta ba za tă fita ba! Ka fitar da shi gunduwa-gunduwa ba tare da jefa ƙuri’a a kansu ba.
C’est pourquoi, ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Malheur à la ville de sang, la marmite en laquelle est sa rouille, et dont la rouille ne se détache pas! Tires-en morceau par morceau; qu’on ne jette pas le sort sur elle;
7 “‘Gama zubar da jini yana a tsakiyarta, ta zubar da shi a dutsen da yake a fili; ba tă zubar da shi a ƙasa ba, inda ƙura za tă rufe shi.
car son sang est au milieu d’elle: elle l’a mis sur le roc nu, elle ne l’a pas versé sur la terre pour le couvrir de poussière.
8 Don a zuga hasala a kuma yi sakayya na sa jininta a dutsen da ba a rufe ba, saboda kada a rufe.
Pour faire monter la fureur, pour exécuter la vengeance, j’ai mis son sang sur le roc nu, pour qu’il ne soit pas couvert.
9 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini! Ni ma zan jibge itace da yawa.
C’est pourquoi, ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Malheur à la ville de sang! Moi aussi je ferai une grande pile de bois.
10 Ka tula gumagumai ka kuma ƙuna wuta. Ka dafa naman da kyau, kana haɗawa da yaji; ka kuma bar ƙasusuwan su ƙone.
Entasse le bois, allume le feu, fais consommer la chair, assaisonne-la bien, et que les os soient brûlés.
11 Sa’an nan ka sa tukunyan nan da babu kome a kan garwashi sai ta yi zafi har darmarta ta yi ja wur domin dattinta ya narke tsatsarta kuma ta ƙone.
Place-la vide sur les charbons ardents, afin qu’elle s’échauffe et que son airain devienne brûlant, et que son impureté soit fondue au-dedans d’elle [et] que sa rouille soit consumée.
12 Ta gajiyar da dukan ƙoƙari; ba a fid da tsatsarta nan mai yawa ba, kai, ko a wuta ma.
Elle a lassé les efforts, et la rouille dont elle est pleine ne se détache pas: – au feu sa rouille!
13 “‘Yanzu ƙazantarki ita ce lalaci. Domin na yi ƙoƙari in tsabtacce ke amma ba ki tsabtattu daga ƙazantarki ba, ba za ki ƙara yin tsabta ba sai hasalata a kanki ya kwanta.
Il y a de l’infamie dans ton impureté; puisque je t’ai purifiée, et tu n’es point pure. Tu ne seras plus purifiée de ton impureté, jusqu’à ce que j’aie satisfait sur toi ma fureur.
14 “‘Ni Ubangiji na faɗa. Lokaci ya zo da zan aikata. Ba zan janye ba; ba zan ji tausayi ba, ba kuwa zan bari ba. Za a hukunta ki bisa ga hali da ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Moi, l’Éternel, j’ai parlé: cela arrivera, et je le ferai; je ne reculerai point, et je n’aurai point de compassion, et je ne me repentirai pas. On te jugera selon tes voies et selon tes actions, dit le Seigneur, l’Éternel.
15 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l’Éternel vint à moi, disant:
16 “Ɗan mutum, da farat ɗaya ina gab da ɗauke abin da idanunka suke jin daɗin gani. Duk da haka kada ka yi makoki ko ka yi kuka ko ka zub da hawaye.
Fils d’homme, voici, je vais t’ôter, par une plaie, le désir de tes yeux; et tu ne mèneras pas deuil, et tu ne pleureras pas, et tes larmes ne couleront pas.
17 Ka yi nishi shiru; kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka ka kuma sa takalmanka a ƙafa; kada ka rufe sashen fuskarka daga ƙasa ko ka ci abincin da masu kuka sukan ci.”
Gémis en silence: tu ne feras point le deuil des morts. Enroule ton turban sur toi, et mets tes sandales à tes pieds, et ne couvre pas ta barbe, et ne mange pas le pain des hommes. –
18 Da gari ya waye, sai na yi magana da mutane, da yamma kuwa matata ta rasu. Kashegari na yi yadda aka umarce ni.
Et je parlai au peuple le matin, et ma femme mourut le soir; et, le matin, je fis comme il m’avait été commandé.
19 Sai mutane suka tambaye ni suka ce, “Ba za ka faɗa mana abin da waɗannan abubuwa suke nufi a gare mu ba?”
Et le peuple me dit: Ne nous déclareras-tu pas ce que signifient pour nous ces choses que tu fais?
20 Sai na ce musu, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
Et je leur dis: La parole de l’Éternel est venue à moi, disant:
21 faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da ƙazantar da wuri mai tsarkina, kagarar da kuke taƙama, abin da idanunku suke jin daɗin gani, abin faranta zuciyarku.’Ya’yanku maza da mata waɗanda kun bari a baya za su mutu ta wurin takobi.
Dis à la maison d’Israël: Ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Voici, je profane mon sanctuaire, l’orgueil de votre force, le désir de vos yeux, et l’affection de votre âme; et vos fils et vos filles que vous avez laissés en arrière tomberont par l’épée.
22 Za ku kuma yi yadda na yi. Ba za ku rufe sashe ƙasa na fuskarku ko ku ci abinci da masu kuka sukan ci ba.
Et vous ferez comme j’ai fait: vous ne couvrirez point votre barbe et vous ne mangerez pas le pain des hommes;
23 Za ku naɗa rawunanku a kai ku sa takalmanku a ƙafafunku. Ba za ku yi kuka ko makoki ba amma za ku lalace saboda zunubanku ku kuma yi ta yin nishi.
et vos turbans seront sur vos têtes, et vos sandales à vos pieds; vous ne mènerez pas deuil et vous ne pleurerez pas, mais vous vous consumerez dans vos iniquités, et vous gémirez l’un vis-à-vis de l’autre.
24 Ezekiyel zai zama alama gare ku; za ku yi daidai yadda ya yi. Sa’ad da wannan ya faru, za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’
Et Ézéchiel sera pour vous un signe: selon tout ce qu’il a fait, vous ferez. Quand cela arrivera, vous saurez que je suis le Seigneur, l’Éternel.
25 “Kai kuma ɗan mutum, a ranar da zan ɗauke musu kagararsu, farin cikinsu da darajarsu, abin da idanunsu ke jin daɗin gani, abin da yake faranta musu zuciya, da kuka’ya’yansu maza da mata,
Et toi, fils d’homme, au jour où je leur ôterai ce qui a été leur confiance, la joie de leur ornement, le désir de leurs yeux, et ce que recherchent leurs âmes, leurs fils et leurs filles,
26 a ranan nan wanda ya tsere zai zo don yă ba ka labari.
en ce jour-là celui qui sera réchappé ne viendra-t-il pas vers toi pour le faire entendre à tes oreilles?
27 A lokacin bakinka zai buɗe, za ka yi magana da shi ba kuwa za ka ƙara yin shiru ba. Ta haka za ka zama alama gare su, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.”
En ce jour-là ta bouche sera ouverte avec le réchappé, et tu parleras et tu ne seras plus muet; et tu seras pour eux un signe, et ils sauront que je suis l’Éternel.

< Ezekiyel 24 >