< Ezekiyel 23 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de Yahweh me fut adressée en ces termes:
2 “Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
" Fils de l'homme, il y avait deux femmes, filles d'une même mère.
3 Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
Elles se prostituèrent en Egypte, elles se prostituèrent dans leur jeunesse. Là on a saisi leurs mamelles, là on a pressé leur sein virginal.
4 Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
Voici leurs noms: Oolla, la plus grande, et Ooliba, sa sœur. Elles furent à moi, et elles enfantèrent des fils et des filles. Voici leurs noms: Oolla, c'est Samarie; Ooliba, c'est Jérusalem.
5 “Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
Oolla me fut infidèle; elle brûla d'amour pour ses amants, les Assyriens, ses voisins.
6 waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
Vêtus de pourpre, gouverneurs et magistrats, tous beaux jeunes hommes, cavaliers montés sur des chevaux.
7 Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
C'est vers eux qu'elle dirigea ses prostitutions, vers toute l'élite des fils de l'Assyrie; et près de tous ceux pour qui elle brûlait d'amour, elle se souilla avec toutes leurs infâmes idoles.
8 Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
Et elle n'abandonna pas ses prostitutions de l'Egypte; car ils l'avaient déshonorée dans sa jeunesse; ils avaient pressé son sein virginal, et répandu sur elle leur impudicité.
9 “Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
C'est pourquoi je l'ai livrée aux mains de ses amants, aux mains des fils de l'Assyrie, pour qui elle avait brûlé d'amour.
10 Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
Ils ont découvert sa nudité; ils ont pris ses fils et ses filles; ils l'ont égorgée avec l'épée. Et elle devint en renom parmi les femmes; car justice en avait été faite.
11 “Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
Et sa sœur Ooliba l'a vu, et plus qu'elle elle a rendu pervers ses amours; et ses prostitutions ont surpassé celles de sa sœur.
12 Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
Elle a brûlé d'amour pour les fils de l'Assyrie, gouverneurs et chefs, ses voisins richement vêtus, cavaliers montés sur des chevaux, tous beaux jeunes hommes.
13 Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
Je vis qu'elle aussi se souillait; toutes deux suivaient la même voie.
14 “Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
Elle ajouta encore à ses prostitutions: elle vit des hommes peints sur le mur, des images de Chaldéens peintes au vermillon;
15 da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
ils portaient des ceintures sur leurs reins, ils avaient sur leurs têtes d'amples turbans; tous paraissaient de grands seigneurs. C'étaient les figures des fils de Babylone, dont la Chaldée était la terre d'origine.
16 Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
Elle brûla pour eux dès que ses yeux les virent, et elle envoya des messagers vers eux en Chaldée;
17 Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
et les fils de Babylone vinrent vers elle au lit des amours et ils la souillèrent par leurs prostitutions, et elle se souilla avec eux; puis son âme se dégoûta d'eux.
18 Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
Elle fit voir à découvert ses prostitutions, elle découvrit sa nudité; et mon âme se dégoûta d'elle, comme mon âme s'était dégoûtée de sa sœur.
19 Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
Elle a multiplié ses prostitutions, se rappelant les jours de sa jeunesse, lorsqu'elle se prostituait au pays d'Egypte.
20 A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
Elle a brûlé pour ses impudiques, dont les membres sont des membres d'âne, et l'ardeur lubrique celle des étalons.
21 Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
Tu es revenue aux crimes de ta jeunesse, quand les Egyptiens pressaient tes mamelles, à cause de ton sein virginal.
22 “Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
C'est pourquoi, Ooliba, ainsi parle le Seigneur Yahweh: Voici que je vais exciter contre toi tes amants, ceux dont ton âme s'est dégoûtée, et je les ferai venir contre toi de toute part,
23 Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
les fils de Babylone et tous les Chaldéens, princes, chefs et seigneurs, et avec eux tous les fils de l'Assyrie, beaux jeunes hommes, tous gouverneurs et magistrats, dignitaires et personnages illustres, tous montés sur des chevaux.
24 Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
Contre toi s'avancent armes, chars et roues, avec une multitude de peuples; ils disposent contre toi boucliers, écus et casques; je remets devant eux le jugement, et ils te jugeront selon leurs lois.
25 Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
Je dirigerai ma jalousie contre toi; et ils te traiteront avec fureur; ils te couperont le nez et les oreilles, et ce qui restera de toi tombera par l'épée; ils prendront tes fils et tes filles, et ce qui restera de toi sera dévoré par le feu.
26 Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
Ils te dépouilleront de tes vêtements, et ils enlèveront tes bijoux.
27 Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
Je mettrai un terme à ton crime, et à tes prostitutions du pays d'Egypte; tu ne lèveras plus les yeux vers eux, et tu ne te souviendras plus de l'Egypte.
28 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
Car ainsi parle le Seigneur Yahweh: Voici que je vais te livrer aux mains de ceux que tu hais, aux mains de ceux dont ton âme s'est dégoûtée.
29 Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
Ils te traiteront avec haine, ils emporteront tout ce que tu as gagné, et te laisseront nue, complètement nue; et ta nudité impudique, ton impureté et tes prostitutions seront découvertes.
30 sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
On te traitera ainsi parce que tu t'es prostituée aux nations, parce que tu t'es souillée avec leurs idoles infâmes.
31 Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
Tu as marché dans la voie de ta sœur; je mettrai sa coupe dans ta main.
32 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
Ainsi parle le Seigneur Yahweh: Tu boiras la coupe de ta sœur, coupe profonde et large; elle donnera à rire et à se moquer de toi, tant est grande sa capacité.
33 Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
Tu seras remplie d'ivresse et de douleur; c'est une coupe de désolation et de dévastation que la coupe de ta sœur, Samarie.
34 Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
Tu la boiras et la videras, tu en mordras les morceaux et t'en déchireras le sein; car moi j'ai parlé, — oracle du Seigneur Yahweh.
35 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
C'est pourquoi ainsi parle le Seigneur Yahweh: Parce que tu m'as oublié, et que tu m'as rejeté derrière ton dos, porte donc, toi aussi, la peine de ton impureté et de tes prostitutions! "
36 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
Et Yahweh me dit: " Fils de l'homme, jugeras-tu Oolla et Ooliba? Déclare-leur leurs abominations.
37 gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
Car elles ont été adultères, et il y a du sang dans leurs mains; elles ont commis l'adultère avec leurs idoles infâmes, et même leurs fils qu'elles m'avaient enfantés, elles les ont fait passer par le feu, pour qu'ils les mangent.
38 Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
Voici encore ce qu'elles ont fait: Elles ont souillé mon sanctuaire en ce jour-là, et elles ont profané mes sabbats.
39 A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
Et lorsqu'elles immolaient leurs fils à leurs idoles infâmes, elles entraient le même jour dans mon sanctuaire, pour le profaner: Voilà ce qu'elles ont fait au milieu de ma maison.
40 “Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
Et même elles ont envoyé chercher des hommes venant de loin; et ceux à qui avait été envoyé un messager, voici qu'ils sont venus, ... ceux pour qui tu t'es lavée, tu as mis du fard à tes yeux, tu t'es ornée de parures!
41 Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
Et tu t'es assise sur un lit d'apparat, devant lequel une table était dressée, où tu as posé mon encens et mon huile.
42 “Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
On y entendait le bruit d'une foule à l'aise; aux gens venus des grands amas d'hommes, se sont joints les buveurs du désert, qui ont mis des bracelets aux mains des deux sœurs, et des couronnes magnifiques sur leurs têtes.
43 Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
Et je dis à cette femme usée dans les adultères: Va-t-elle maintenant continuer ses prostitutions, elle aussi?
44 Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
On va vers elle comme on va chez une prostituée. C'est ainsi qu'on est allé chez Oolla et Ooliba, ces femmes criminelles.
45 Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
Mais des hommes justes les condamneront à la peine des femmes adultères, et à la peine de celles qui répandent le sang; car elles sont adultères, et il y a du sang dans leurs mains.
46 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
Car ainsi parle le Seigneur Yahweh: Fais monter contre elles une assemblée, et qu'on les livre à la terreur et au pillage;
47 Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
et que l'assemblée les accable sous les pierres, et les taille en pièces avec ses épées; qu'on tue leurs fils et leurs filles, et qu'on brûle au feu leurs maisons!
48 “Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
Et je ferai cesser l'impureté dans le pays, et toutes les femmes en recevront une leçon, et ne commettront point des impuretés pareilles aux vôtres,
49 Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”
On fera retomber votre impureté sur vous, et vous porterez la peine de votre idolâtrie; et vous saurez que je suis le Seigneur Yahweh. "

< Ezekiyel 23 >