< Ezekiyel 23 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
HERRENS Ord kom til mig saaledes:
2 “Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
Menneskesøn! Der var to Kvinder, Døtre af en og samme Moder.
3 Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
De bolede i deres Ungdom i Ægypten: der krammedes deres Bryster, der krænkede man deres Jomfrubarm.
4 Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
Den ældste hed Ohola, hendes Søster Oholiba. Og de blev mine og fødte Sønner og Døtre. Ohola er Samaria, Oholiba Jerusalem.
5 “Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
Men i Stedet for at holde sig til mig bolede Ohola og var i Brynde for sine Elskere, Assurs Sønner, der nærmede sig hende
6 waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
klædt i Purpur, Statholdere og Landshøvdinger, alle sammen smukke unge Mænd, Ryttere højt til Hest;
7 Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
og hun gav dem sin bolerske Elskov, alle Assurs ypperste Sønner, og alle Vegne, hvor hun kom i Brynde, gjorde hun sig uren ved deres Afgudsbilleder.
8 Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
Men sin Bolen med Ægypterne opgav hun ikke, thi de hade ligget hos hende i hendes Ungdom; de havde skændet hendes Jomfrubarm og udøst deres bolerske Attraa over hende.
9 “Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
Derfor gav jeg hende i hendes Elskeres, Assurs Sønners, Haand, for hvem hun var i Brynde;
10 Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
og de blottede hendes Blusel, tog hendes Sønner og Døtre og dræbte hende selv med Sværd, saa hun fik Vanry blandt Kvinder; saaledes fuldbyrdede de Dommen over hende.
11 “Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
Det saa hendes Søster Oholiba, og dog kom hun i endnu værre Brynde og bolede endnu værre end Søsteren.
12 Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
Hun kom i Brynde for Assurs Sønner, Statholdere og Landshøvdinger, der nærmede sig hende herligt klædt, Ryttere højt til Hest, alle sammen smukke unge Mænd.
13 Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
Og jeg saa, at hun blev uren; begge fulgte samme Vej.
14 “Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
Men hun drev sin Bolen videre endnu; thi da hun saa Mænd afbildede paa Muren, Billeder af Kaldæere, malet med rødt,
15 da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
med Bælte om Lænd og nedhængende Hovedbind, alle at se til som Høvedsmænd, en Afbildning af Babels Sønner, hvis Hjemstavn Kaldæa er,
16 Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
saa kom hun i Brynde for dem, saa snart hun fik Øje paa dem, og hun sendte Bud til dem i Kaldæa:
17 Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
Og Babels Sønner gik ind til hende, laa hos hende i Elskov og gjorde hende uren ved deres Bolen; og hun blev uren ved dem, til hun følte Lede ved dem.
18 Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
Da hun havde aabenbaret sin bolerske Attraa og blottet sin Blusel, følte jeg Lede ved hende, som jeg var blevet led ved hendes Søster.
19 Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
Men hun drev sin Bolen videre endnu, idet hun kom sin Ungdoms Dage i Hu, da hun havde bolet i Ægypten,
20 A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
og hun kom i Brynde ved dets Bolere, der havde Kød som Æsler og var gejle som Hingste;
21 Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
og hun optog sin Ungdoms Skændsel, dengang Ægypterne krænkede hendes Jomfrubarm og krammede hendes unge Bryster,
22 “Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
Derfor, Oholiba, saa siger den Herre HERREN: Jeg hidser dine Elskere paa dig, dem, du følte Lede ved, og fører dem mod dig fra alle Kanter,
23 Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
Babels Sønner og alle Kaldæerne, Pekod, Sjoa og Koa og med dem alle Assurs Sønner, alle sammen smukke unge Mænd, Statholdere og Landshøvdinger, Høvedsmænd og navnkundige Mænd, alle højt til Hest;
24 Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
og de skal komme imod dig med en Vrimmel af Vogne og Hjul og en Hærskare af Folkeslag; store og smaa Skjolde og Hjelme skal de rette imod dig fra alle Kanter. Jeg overlader dem Dommen, og de skal dømme dig efter deres Ret.
25 Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
Jeg retter min Nidkærhed imod dig, og de skal handle med dig i Vrede; din Næse og dine Ører skal de skære af, dit Afkom skal falde for Sværdet; de skal tage dine Sønner og Døtre, og dit Afkom skal fortæres af Ild;
26 Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
de skal rive Klæderne af dig og tage alle dine Smykker;
27 Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
jeg gør Ende paa din Skændsel og din Bolen, som du hengav dig til i Ægypten, og du skal ikke mere løfte dit Blik til dem eller komme Ægypten i Hu.
28 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
Thi saa siger den Herre HERREN: Se, jeg giver dig i deres Haand, som du hader og ledes ved;
29 Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
de skal handle med dig i Had og tage alt dit Gods og efterlade dig nøgen og bar, saa din bolerske Blusel blottes.
30 sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
Det kan du takke din Skændsel og din Bolen for, thi du bolede med Folkene og gjorde dig uren med deres Afgudsbilleder.
31 Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
Du vandrede i din Søsters Spor; derfor giver jeg dig hendes Bæger i Haanden.
32 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
Saa siger den Herre HERREN: Du skal drikke af din Søsters Bæger, som er baade dybt og bredt; du skal blive til Latter og Spot; Bægeret rummer meget;
33 Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
det er fuldt af Beruselse og Stønnen, et Bæger med Gru og Rædsel er din Søster Samarias Bæger.
34 Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
Du skal drikke det ud til sidste Draabe, gnave dets Skaar og sønderrive dine Bryster, saa sandt jeg har talet, lyder det fra den Herre HERREN.
35 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
Derfor, saa siger den Herre HERREN: Fordi du glemte mig og kastede mig bag din Ryg, skal du bære Følgen af din Skændsel og Bolen.
36 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
Og HERREN sagde til mig: Menneskesøn! Vil du dømme Ohola og Oholiba, saa forehold dem deres Vederstyggeligheder,
37 gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
at de horede og har Blod paa Hænderne; de horede med deres Afgudsbilleder, og til Føde for dem lod de Børnene, de fødte mig, gaa igennem Ilden.
38 Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
Fremdeles har de gjort mig dette: De har gjort min Helligdom uren og vanhelliget mine Sabbater;
39 A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
endog samme Dag de havde slagtet deres Børn til Afgudsbillederne, kom de til min Helligdom og vanhelligede den. Sandelig, saaledes gjorde de i mit Hus.
40 “Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
Ja, for Mænd, som kom langvejs fra, straks der var sendt dem Bud, badede du dig, sminkede du dine Øjne og tog dine Smykker paa;
41 Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
og du satte dig paa et prægtigt Leje, og foran det dækkedes et Bord, paa hvilket du satte min Røgelse og min Olie.
42 “Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
Og det ligefrem larmede hos Søstrene; saa mange Mænd kom der fra Ørkenen; og de lagde Spange om deres Arme og satte en herlig Krone paa deres Hoved.
43 Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
Saa sagde jeg: Saaledes har de horet, paa Skøgevis har de bolet.
44 Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
Man gik ind til dem som til en Skøge; saaledes gik man ind til Ohola og Oholiba og øvede Skændsel.
45 Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
Uvildige Mænd skal dømme dem efter Ægteskabsbryderskers og Morderskers Ret; thi de horede og har Blod paa Hænderne.
46 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
Thi saa siger den Herre HERREN: En Forsamling skal sammenkaldes imod dem, og de skal gives hen til at mishandles og udplyndres;
47 Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
Forsamlingen skal stene dem og hugge dem sønder og sammen med Sværd; deres Sønner og Døtre skal man dræbe, og deres Huse skal man brænde.
48 “Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
Jeg gør Ende paa Skændselen i Landet, og alle Kvinder skal lade sig advare derved og ikke efterligne eders Skændsel.
49 Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”
Man skal lade eders Skændsel komme over eder, og I skal bære Følgen af de Synder, I gjorde med eders Afgudsbilleder; og I skal kende, at jeg er den Herre HERREN.

< Ezekiyel 23 >