< Ezekiyel 23 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Opět stalo se slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
2 “Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
Synu člověčí, dvě ženy, dcery jedné mateře byly.
3 Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
Ty smilnily v Egyptě, v mladosti své smilnily. Tam jsou mačkány prsy jejich, tam opiplány prsy panenství jejich.
4 Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
Jména pak jejich: větší Ahola, sestry pak její Aholiba. Tyť jsou byly mé, a rozplodily syny a dcery. Jména, pravím, jejich jsou: Samaří Ahola, Jeruzaléma pak Aholiba.
5 “Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
Ale Ahola maje mne, smilnila a frejů hleděla s milovníky svými, s Assyrskými blízkými,
6 waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
Oděnými postavcem modrým, s vývodami a knížaty, i všemi napořád mládenci krásnými, a s jezdci jezdícími na koních.
7 Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
Vydala se, pravím, v smilství svá s nimi, se všemi nejpřednějšími syny Assyrskými, a se všemi, jimž frejovala, a poškvrnila se všemi ukydanými bohy jejich.
8 Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
A tak smilství svých Egyptských nenechala; nebo ji zléhali v mladosti její, a oni mačkali prsy panenství jejího, a vylili smilství svá na ni.
9 “Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
Protož dal jsem ji v ruku frejířů jejích, v ruku Assyrských, jimž frejovala.
10 Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
Oniť jsou odkryli nahotu její, syny i dcery její pobrali, ji pak samu mečem zamordovali. Takž vzata jest na slovo od jiných žen, když soudy vykonali při ní.
11 “Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
To viděla sestra její Aholiba, však mnohem více než onano frejovala, a smilství její větší byla než smilství sestry její.
12 Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
S Assyrskými frejů hleděla, s vývodami a knížaty blízkými, oděnými nádherně, s jezdci jezdícími na koních, a všemi mládenci krásnými.
13 Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
I viděl jsem, že se poškvrnila, a že cesta jednostejná jest obou dvou.
14 “Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
Ale tato ještě to přičinila k smilstvím svým, že viduc muže vyryté na stěně, obrazy Kaldejských vymalované barvou,
15 da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
Přepásané pasem po bedrách jejich, a klobouky barevné na hlavách jejich, a že jsou všickni na pohledění jako hejtmané, podobní synům Babylonským v Kaldejské zemi, jejichž ona vlast jest,
16 Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
I zahořela k nim z pohledění očima svýma, a vyslala posly k nim do země Kaldejské.
17 Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
Tedy vešli k ní Babylonští na lůže nepoctivé, a poškvrnili ji smilstvím svým. A když se poškvrnila s nimi, odloučila se duše její od nich.
18 Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
A odkryla smilství svá, odkryla též nahotu svou, i odloučila se duše má od ní, tak jako se odloučila duše má od sestry její.
19 Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
Nebo rozmnožila smilství svá, rozpomínajíc se na dny mladosti své, v nichž smilnila v zemi Egyptské,
20 A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
A frejovala s kuběnáři jejich, jejichž tělo jest jako tělo oslů, a tok jejich jako tok koňský.
21 Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
A tak jsi zase navrátila se k nešlechetnosti mladosti své, když mačkali Egyptští prsy tvé z příčiny prsů mladosti tvé.
22 “Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
Protož ó Aholiba, takto praví Panovník Hospodin: Aj, já vzbudím frejíře tvé proti tobě, ty, od nichž se odloučila duše tvá, a přivedu je na tě odevšad,
23 Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
Babylonské a všecky Kaldejské, Pekodské, a Šohejské, i Kohejské, všecky syny Assyrské s nimi, mládence krásné, vývody a knížata všecka, hejtmany a slovoutné, všecky jezdící na koních.
24 Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
A přitáhnou na tě na vozích železných a přikrytých, i kárách, a to s zběří národů, s pavézami a štíty i lebkami, položí se proti tobě vůkol, i předložím jim právo, aby tě soudili soudy svými.
25 Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
Vyleji zajisté horlení své na tebe, tak že naloží s tebou prchlivě, nos tvůj i uši tvé odejmou, a ostatek tebe mečem padne. Ti syny tvé i dcery tvé poberou, a ostatek tebe spáleno bude ohněm.
26 Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
A vyvlekou tě z roucha tvého, a rozberou šperky okrasy tvé.
27 Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
A tak přítrž učiním při tobě nešlechetnosti tvé, i smilství tvému z země Egyptské vzatému, a nepozdvihneš očí svých k nim, a na Egypt nezpomeneš více.
28 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
Nebo takto praví Panovník Hospodin: Aj, já dám tebe v ruku těch, kterýchž nenávidíš, v ruku těch, od nichž se odloučila duše tvá,
29 Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
I budou nakládati s tebou podlé nenávisti, a poberou všecko úsilé tvé, a nechají tě nahé a obnažené. A tak bude zřejmá nahota smilství tvého a nešlechetnosti tvé, smilství, pravím, tvého.
30 sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
Což vše učiní tobě proto, že jsi smilnila, následujíc pohanů, proto že jsi poškvrnila se ukydanými bohy jejich.
31 Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
Cestou sestry své chodila jsi, protož dám kalich její v ruku tvou.
32 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
Takto praví Panovník Hospodin: Kalich sestry své píti budeš hluboký a široký; budeť sporý, tak že smích a žert budou míti z tebe.
33 Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
Opilstvím a zámutkem naplněna budeš, kalichem pustiny a zpuštění, kalichem sestry své Samaří.
34 Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
I vypiješ jej a vyvážíš, a než jej polámeš, snáze prsy své roztrháš; neboť jsem já mluvil, praví Panovník Hospodin.
35 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
Protož takto praví Panovník Hospodin: Z té příčiny, že jsi zapomenula na mne, a zavrhlas mne za hřbet svůj, i ty také vezmi za svou nešlechetnost, a za smilství svá.
36 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
I řekl Hospodin ke mně: Synu člověčí, budeš-liž zastávati Ahole neb Aholiby? Nýbrž oznam jim ohavnosti jejich,
37 gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
Že cizoložily, a krev jest na rukou jejich, a s ukydanými bohy svými cizoložily. Také i syny své, kteréž mně zplodily, vodily jim, aby sežráni byli.
38 Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
Ještě i toto činily mi, že zanečišťovaly svatyni mou v tentýž den, a sobot mých poškvrňovaly.
39 A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
Nebo obětovavše syny své ukydaným bohům svým, vcházely do svatyně mé v tentýž den, aby ji poškvrnily. Aj hle, takť jsou činívaly u prostřed mého domu.
40 “Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
Nadto, že vysílaly k mužům, jenž by přišli zdaleka, kteříž, jakž posel vyslán k nim, aj, hned přicházívali. Jimž jsi se umývala, a tvář svou líčila, a okrašlovalas se okrasou.
41 Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
A usazovalas se na loži slavném, před nímž stůl připravený byl, na něž jsi i kadidlo mé i masti mé vynakládala.
42 “Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
Když pak hlas toho množství poutichl, tedy i k mužům z obecného lidu vysílaly, jenž bývali přivozováni ožralí z pouště. I dávali náramky na ruce jejich, i koruny ozdobné na hlavy jejich.
43 Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
A ačkoli jsem se domlouval na cizoložství té lotryně, a že oni jednak s jednou, jednak s druhou smilství provodí,
44 Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
A že každý z nich vchází k ní, tak jako někdo vchází k ženě nevěstce: však vždy vcházeli k Ahole a Aholibě, ženám přenešlechetným.
45 Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
Protož muži spravedliví, tiť je souditi budou soudem cizoložných a soudem těch, jenž vylévaly krev, proto že cizoložily, a krev jest na rukou jejich.
46 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
Nebo takto praví Panovník Hospodin: Přivedu na ně vojsko, a dám je v posmýkání i v loupež.
47 Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
I uhází je to shromáždění kamením, a poseká je meči svými; syny jejich i dcery jejich pomordují, a domy jejich ohněm popálí.
48 “Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
A tak přítrž učiním nešlechetnosti v zemi této, i budou se tím káti všecky ženy, a nedopustí se nešlechetnosti podobné vaší.
49 Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”
Nebo vzložena bude na vás nešlechetnost vaše, a ponesete hříchy ukydaných bohů svých. I zvíte, že já jsem Panovník Hospodin.

< Ezekiyel 23 >