< Ezekiyel 22 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
І було мені слово Господнє таке:
2 “Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
„А ти, сину лю́дський, чи будеш судити, чи суди́тимеш ти місто крови? І завідо́м його про всі гидо́ти його,
3 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
та й скажеш: Так говорить Господь Бог: Місто проливає кров у своїй сере́дині, щоб прийшов його час, і робить божкі́в собі, щоб занечи́щуватися!
4 kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
Кров'ю, що ти проливала, о дочко Єрусалиму, грішила ти, а божка́ми, яких ти робила, занечи́стилася, і набли́зила свої дні, і прийшла аж до своїх ро́ків. Тому дам тебе наро́дам на га́ньбу, і на посміхо́висько для всіх країв!
5 Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
Близькі та далекі від тебе насміхаються з тебе, нечистойме́нна, багатозаколо́тна!
6 “‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
Ось Ізраїлеві князі, кожен за раме́ном своїм, були́ в тебе, щоб кров проливати.
7 A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
Батька та матір у тебе легкова́жать, чужи́нцеві роблять у́тиск серед тебе, сироту та вдову пригнічують у тебе.
8 Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
Моїми свя́тощами ти погорджуєш, а суботи Мої зневажаєш.
9 A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
У тебе є накле́пники, щоб кров проливати, і на па́гірках їдять у тебе, розпусту чинять серед тебе.
10 A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
Наготу́ батька в тебе відкривають, жінку, у ча́сі її місячної нечистоти́, безчестять у тебе.
11 A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
І один робить гидо́ту з жінкою свого ближнього, а той занечищує розпустою невістку свою, а той безчестить у тебе сестру свою, дочку́ батька свого́.
12 A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Пі́дкуп беруть у тебе, щоб кров проливати, ли́хву та відсо́тка береш ти й ошу́куєш у́тиском ближніх своїх. А Мене ти забуваєш, говорить Господь Бог.
13 “‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
І ось сплесну́в Я руками Своїми за твою кривду, яку ти робила, та за кровопролиття́ твої, що були в тебе.
14 Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
Чи всто́їть твоє серце, чи будуть міцні́ твої руки на ті дні, що Я буду з тобою чинити? Я, Господь, говорив це й зробив!
15 Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
І розпоро́шу тебе серед наро́дів, і розси́плю тебе по края́х, і викину твою нечистість із тебе.
16 Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
І станеш ти збезче́щеною через себе на оча́х народів, і пізнаєш, що Я — Госпо́дь!“
17 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
І було мені слово Господнє таке:
18 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
„Сину лю́дський, дім Ізраїлів став мені за жу́желицю; усі вони мідь, і ци́на, і залізо, і о́ливо в сере́дині го́рна, жу́желицею срі́бла сталися.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
Тому так говорить Господь Бог: За те, що всі ви стали жу́желицею, тому ось Я позбираю вас до сере́дини Єрусалиму.
20 Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
Як збирають срі́бло, і мідь, і залізо, і о́ливо, і цину до сере́дини го́рна, щоб дмухати на нього огнем, щоб розтопи́ти, — так зберу́ у Своїм гніві та в люті Своїй, і покладу́, і розтоплю́ вас!
21 Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
І позбираю вас, і дмухну́ на вас огнем Свого гніву, і ви будете розто́плені в сере́дині його.
22 Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
Як розто́плюється срібло в сере́дині го́рна, так бу́дете розто́плені ви в сере́дині його, і пізна́єте, що Я, Господь, вилив гнів Свій на вас!“
23 Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
І було мені слово Господнє таке:
24 “Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
„Сину лю́дський, скажи до неї: Ти земля неочи́щена, у дні гніву доще́м не поли́тая!
25 Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
Змо́ва її пророків серед нього, як реву́чий лев, що здо́бич шматує: жеру́ть душу, маєток та багатство забирають, прибі́льшують уді́в її в сере́дині її.
26 Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
Священики її ламають Зако́на Мого, і зневажаю́ть Мої святощі, не розрізняють між святим та несвятим, і не оголошують різни́ці між нечистим та чистим, і від субіт Моїх закривають свої очі. І був Я знева́жений серед них.
27 Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
Князі́ її в сере́дині її, немов ті вовки́, що здо́бич шмату́ють, щоб розливати кров, щоб губити ду́ші ради ко́ристи.
28 Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
А пророки її все замазують болотом, бачать марно́ту, і чару́ють собі неправдою, вони кажуть: „Так говорить Господь Бог“, а Господь не говорив.
29 Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
Наро́ди Кра́ю тиснуть у́тиском та грабують грабунком, а вбогого та бідака́ гно́блять, а чужи́нця тиснуть у безправ'ї.
30 “Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
І шукав Я між ними чоловіка, що поставив би загоро́ду, і став би в ви́ломі перед Моїм обличчям за цей Край, щоб Я не знищив його, — та Я не знайшов!
31 Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
І Я вилив на них Свій гнів, огнем пересе́рдя Свого повигу́блював їх, їхню дорогу Я дав на їхню го́лову, каже Господь Бог“.

< Ezekiyel 22 >