< Ezekiyel 22 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Och Herrans ord skedde till mig, och sade:
2 “Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
Du menniskobarn, vill du icke straffa den mordiska staden, och hålla honom före all hans styggelse?
3 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
Säg: Så säger Herren Herren: O du stad, som utgjuter dinas blod, på det din tid skall komma, och du, som afgudar gör när dig, på det du skall orena dig.
4 kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
Du förbryter dig på det blod, som du utgjuter, och orenar dig uppå de afgudar, som du gör, dermed du låter dina dagar nalkas, och beställer att din år komma måste; derföre skull jag göra dig till spott ibland Hedningarna, och till hån i all land.
5 Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
Både när och fjerran skola de bespotta dig, så att du måste hafva ett skändeligit rykte, och stor jämmer lida.
6 “‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
Si, Förstarna i Israel hvar och en är mägtig när dig, till att utgjuta blod.
7 A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
Fader och moder förakta de; främlinganom göra de våld och orätt; enkor och faderlös barn förtrycka de.
8 Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
Du föraktar min helgedom, och ohelgar mina Sabbather.
9 A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
Förrädare äro uti dig, på det de skola utgjuta blod; de äta på bergomen, och handla vrångvisliga i dig.
10 A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
De blotta fädernas blygd, och nödga qvinnorna i deras krankhet;
11 A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
Och bedrifva styggelig ting, hvar och en med sin skyldmans hustru; de skämma sina egna söners hustrur öfverdådeliga; de göra sina egna systrar, sina fäders döttrar, skam.
12 A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
De taga gåfvor, till att utgjuta blod; de ockra och vinna på hvarannan, och bruka girighet emot sin nästa, och öfverfalla hvarannan, och förgäta mig, säger Herren Herren.
13 “‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
Si, jag slår mina händer tillsamman öfver den girighet, som du bedrifver, och öfver det blod, som i dig utgjutet är.
14 Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
Men menar du, att ditt hjerta kan det lida, eller dina händer det fördraga, på den tid, när jag det med dig görandes varder? Jag, Herren, hafver det sagt, och vill också görat;
15 Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
Och skall förströ dig ibland Hedningarna, och bortdrifva dig i landena; och skall göra en ända på dina slemhet;
16 Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
Så, att du skall ibland Hedningarna aktad varda, såsom en förbannad, och förnimma att jag är Herren.
17 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Och Herrans ord skedde till mig, och sade:
18 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
Du menniskobarn, Israels hus är vordet mig till slagg; all deras koppar, tenn, jern och bly, är i ugnenom vordet till slagg.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
Derföre säger Herren Herren alltså: Efter I nu alle ären slagg vordne, si, så skall jag samka eder tillhopa i Jerusalem.
20 Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
Lika som man tillhopasamkar silfver, koppar, jern, bly och tenn, in uti en ugn, att man må, uppblåsa der en eld under, och smälta det; alltså vill jag ock, i mine vrede och grymhet, sammansamka, inlägga och smälta eder.
21 Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
Ja, jag skall sammansamka eder, och uppblåsa mine vredes eld under eder, att I deruti försmälta skolen.
22 Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
Lika som silfret smälter i ugnenom, så skolen I ock derinne smälta, och förnimma att jag, Herren, hafver utgjutit mina grymhet öfver eder.
23 Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
Och Herrans ord skedde till mig, och sade:
24 “Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
Du menniskobarn, säg till dem: Du äst ett land, som intet står till rensande, såsom ett, der intet regn uppå kommer på vredenes tid.
25 Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
De Propheter, som derinne äro, hafva sig tillhopagaddat, att de skola uppfräta själar, lika som ett rytande lejon, då det röfvar; de rifva till sig gods och penningar, och göra der många enkor inne.
26 Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
Dess Prester drifva orätt under lagsens namn, och ohelga min helgedom; de hålla ingen åtskilnad, emellan heligt och oheligt, och akta intet hvad rent eller orent är, och sköta intet om mina Sabbather, och jag varder ohelgad ibland dem.
27 Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
Dess Förstar derinne äro lika som glupande ulfvar, till att utgjuta blod, och förgöra själar för sina girighets skull.
28 Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
Och dess Propheter bestryka dem med obrukad kalk, predika fåfängelighet, och prophetera dem lögn, och säga: Detta säger Herren Herren; ändock att Herren hafver det intet sagt.
29 Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
Folket i landena brukar våld, och röfva fritt, och öfverfalla de fattiga och elända, och göra främlingomen öfvervåld och orätt.
30 “Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
Jag sökte ibland dem, om någor ville förtaga och stilla vredena för mig, att jag icke skulle förderfva landet; men jag fann ingen.
31 Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Derföre utgöt jag mina vrede öfver dem, och med mine grymhets eld gjorde jag en ända med dem, och gaf dem deras förtjenst uppå deras hufvud, säger Herren Herren.