< Ezekiyel 22 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Opet mi doðe rijeè Gospodnja govoreæi:
2 “Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
A ti, sine èovjeèji, hoæeš li suditi, hoæeš li suditi gradu krvnièkom? i hoæeš li mu pokazati sve gadove njegove?
3 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
Reci: ovako veli Gospod Gospod: ide vrijeme gradu koji proljeva krv u sebi i gradi gadne bogove sebi da se skvrni.
4 kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
Skrivio si krvlju koju si prolio, i oskvrnio si se o gadne bogove svoje koje si naèinio; i uèinio si te se približiše dani tvoji, i došao si do godina svojih, zato æu uèiniti od tebe rug meðu narodima i potsmijeh po svijem zemljama;
5 Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
Koje su blizu tebe i koje su daleko potsmijevaæe ti se, gadni imenom, veliki smetnjom!
6 “‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
Gle, knezovi Izrailjevi u tebi dadoše se da proljevaju krv svaki svom silom svojom.
7 A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
Oca i mater preziru u tebi, èine krivo inostrancu usred tebe, siroti i udovici èine nasilje u tebi;
8 Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
Svete stvari moje prezireš, i subote moje skvrniš.
9 A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
U tebi su opadaèi da proljevaju krv, i na gorama jedu u tebi, grdila èine usred tebe.
10 A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
Golotinju oèinu otkrivaju u tebi, liježu u tebi sa ženom za neèistote njezine.
11 A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
I jedan èini gad sa ženom bližnjega svojega; a drugi skvrni snahu svoju grdilom; a drugi siluje sestru svoju, kæer oca svojega, u tebi.
12 A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Mito primaju u tebi da proljevaju krv; ujam i pridavak uzimaš, i tražiš dobitak od bližnjih svojih prijevarom, a mene si zaboravio, govori Gospod Gospod.
13 “‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
Zato, evo, pljeskam rukama svojim radi tvojega nepravednoga dobitka, koji dobijaš, i radi krvi što je u tebi.
14 Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
Hoæe li se održati srce tvoje, ili ruke tvoje hoæe li biti jake u one dane kad stanem raditi s tobom? Ja Gospod rekoh, i uèiniæu.
15 Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
Jer æu te rasijati po narodima i razasuti po zemljama, i istrijebiæu neèistotu tvoju iz tebe.
16 Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
I biæeš skvrnavan sobom pred narodima, i poznaæeš da sam ja Gospod.
17 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Potom doðe mi rijeè Gospodnja govoreæi:
18 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
Sine èovjeèji, dom Izrailjev posta mi droždina; svi su mjed i kositer i gvožðe i olovo u peæi; droždina od srebra postaše.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
Zato ovako veli Gospod Gospod: što svi vi postaste droždina, zato, evo, ja æu vas skupiti u Jerusalim.
20 Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
Kako se skuplja srebro i mjed i gvožðe i olovo i kositer usred peæi, te se raspali oganj oko njega da se istopi, tako æu vas skupiti gnjevom svojim i jarošæu, i složivši rastopiæu vas.
21 Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
Da, skupiæu vas, i raspaliæu oko vas oganj gnjeva svojega, i istopiæete se usred njega.
22 Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
Kako se topi srebro u peæi, tako æete se vi istopiti u njemu, i poznaæete da sam ja Gospod izlio gnjev svoj na vas.
23 Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
Opet mi doðe rijeè Gospodnja govoreæi:
24 “Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
Sine èovjeèji, kaži joj: ti si zemlja koja se nijesi oèistila; neæe pasti na te dažd u dan gnjeva.
25 Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
Proroci njezini složiše se u njoj, kao lav su, koji rièe i grabi plijen, žderu duše, otimaju blago i dragocjene stvari, umnožavaju udovice usred nje.
26 Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
Sveštenici njezini prestupaju zakon moj i skvrne moje svete stvari, ne razlikuju sveto od oskvrnjenoga, i neèisto od èistoga ne raspoznaju, kriju oèi svoje od subota mojih, i bivam oskvrnjen meðu njima.
27 Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
Knezovi su njezini usred nje kao vuci, koji grabe plijen, proljevajuæi krv, gubeæi duše sramotnoga dobitka radi.
28 Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
I proroci njezini mažu je nevaljalijem kreèem, viðaju taštinu i gataju im laž govoreæi: tako reèe Gospod Gospod; a Gospod ne reèe.
29 Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
Narod zemaljski vara i otima, i siromahu i ubogome èini nasilje, i došljaku èini krivo.
30 “Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
I tražih meðu njima koji bi opravio ogradu i stao na prolomu preda me za tu zemlju, da je ne zatrem; ali ne naðoh nikoga.
31 Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Zato æu izliti na njih gnjev svoj, ognjem jarosti svoje istrijebiæu ih, put njihov obratiæu im na glavu, govori Gospod Gospod.

< Ezekiyel 22 >