< Ezekiyel 22 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Além disso, a palavra de Javé veio até mim, dizendo:
2 “Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
“Você, filho do homem, você vai julgar? Você julgará a cidade sangrenta? Então faça com que ela conheça todas as suas abominações.
3 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
Você dirá: 'O Senhor Javé diz: “Uma cidade que derrama sangue dentro de si mesma, para que seu tempo chegue, e que faz ídolos contra si mesma para profaná-la!
4 kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
Você se tornou culpada em seu sangue que derramou, e está contaminada em seus ídolos que você fez! Você fez com que seus dias se aproximassem, e chegou ao fim de seus anos. Portanto, fiz de vocês uma reprovação às nações e uma zombaria a todos os países.
5 Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
Aqueles que estão próximos e aqueles que estão longe de você zombarão de você, seu infame, cheio de tumulto.
6 “‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
“““Eis que os príncipes de Israel, todos de acordo com seu poder, estiveram em vós para derramar sangue.
7 A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
Em vocês eles trataram pai e mãe com desprezo. Entre vós, eles oprimiram o estrangeiro. Em vocês, eles injustiçaram o órfão de pai e a viúva.
8 Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
Vós desprezastes minhas coisas santas, e profanastes meus sábados.
9 A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
Homens caluniadores têm estado em vós para derramar sangue. Em você, eles comeram nas montanhas. Eles cometeram lascívia entre vocês.
10 A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
Em vocês eles descobriram a nudez de seus pais. Em vocês, eles a humilharam, que estava impura em sua impureza.
11 A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
Um cometeu abominação com a mulher de seu vizinho e outro contaminou lascivamente sua nora. Outro em você humilhou sua irmã, a filha de seu pai.
12 A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Em você, eles aceitaram subornos para derramar sangue. Vocês se interessaram e aumentaram, e ganham avidamente de seus vizinhos pela opressão, e me esqueceram”, diz o Senhor Yahweh.
13 “‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
“““Eis que, portanto, golpeei minha mão em seu ganho desonesto que você fez, e no sangue que foi derramado dentro de você.
14 Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
Seu coração pode suportar, ou suas mãos podem ser fortes, nos dias em que eu vou lidar com você? Eu, Yahweh, já o disse e o farei.
15 Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
Espalharei você entre as nações, e o dispersarei através dos países. Limparei sua imundície de vocês.
16 Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
Você será profanado em si mesmo, à vista das nações. Então vocês saberão que eu sou Yahweh””.
17 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
A palavra de Javé veio até mim, dizendo:
18 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
“Filho do homem, a casa de Israel se tornou uma escória para mim. Todos eles são bronze, estanho, ferro e chumbo no meio da fornalha. Eles são a escória de prata.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
Portanto, o Senhor Javé diz: “Porque todos vocês se tornaram escória, portanto, eis que eu os congregarei no meio de Jerusalém”.
20 Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
Enquanto recolhem prata, bronze, ferro, chumbo e estanho no meio da fornalha, para soprar o fogo sobre ela, para derretê-la, assim eu vos recolherei em minha ira e em minha ira, e vos porei ali e vos derreterei.
21 Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
Yes, eu te recolherei, e soprarei sobre ti com o fogo da minha ira, e tu serás derretido no meio dela.
22 Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
Como a prata é derretida no meio da fornalha, assim sereis derretidos no meio dela; e sabereis que eu, Yahweh, derramei minha ira sobre vós”.
23 Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
A palavra de Yahweh veio até mim, dizendo:
24 “Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
“Filho do homem, diz-lhe: 'Tu és uma terra que não está limpa nem chovendo no dia da indignação'.
25 Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
Há uma conspiração de seus profetas dentro dela, como um leão que ruge e devora a presa. Eles devoraram almas. Eles levam tesouros e coisas preciosas. Fizeram muitas viúvas dentro dela.
26 Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
Seus sacerdotes fizeram violência à minha lei e profanaram minhas coisas sagradas. Eles não fizeram distinção entre o santo e o comum, nem fizeram os homens discernir entre o impuro e o limpo, e esconderam seus olhos de meus sábados. Portanto, eu sou profanado entre eles.
27 Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
Seus príncipes dentro dela são como lobos devorando a presa, para derramar sangue e destruir almas, para que possam obter ganhos desonestos.
28 Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
Seus profetas têm emplastrado para eles com cal, vendo falsas visões e adivinhando-lhes mentiras, dizendo: 'O Senhor Javé diz', quando Javé não falou.
29 Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
O povo da terra tem usado a opressão e exercido o roubo. Sim, eles perturbaram os pobres e necessitados, e oprimiram o estrangeiro injustamente.
30 “Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
“Procurei entre eles um homem que construiria o muro e ficaria na brecha diante de mim para a terra, que eu não a destruiria; mas não encontrei ninguém.
31 Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Therefore “Derramei minha indignação sobre eles. Eu os consumi com o fogo da minha ira. Trouxe seu próprio caminho sobre suas cabeças”, diz o Senhor Yahweh.

< Ezekiyel 22 >