< Ezekiyel 22 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Og Herrens ord kom til mig, og det lød så:
2 “Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
Og du menneskesønn! Vil du dømme, vil du dømme blodstaden? Forehold den alle dens vederstyggeligheter!
3 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
Og du skal si: Så sier Herren, Israels Gud: Du by som har utøst dine innbyggeres blod, forat din tid skal komme, du som har gjort dig motbydelige avguder og således er blitt uren!
4 kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
Ved det blod som du har utøst, er du blitt skyldig, og ved de motbydelige avguder som du har gjort, er du blitt uren, og du har fått dine dager til å nærme sig og har nådd dine år; derfor gjør jeg dig til hån for folkene og til spott for alle landene.
5 Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
De land som er nær, og de som er langt borte fra dig, skal spotte dig, du med ditt utskjemte navn og din store forvirring!
6 “‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
Se, Israels fyrster i dig brukte alle sin arm til å utøse blod.
7 A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
Far og mor blev ringeaktet hos dig; mot den fremmede blev det brukt vold hos dig; den farløse og enken blev undertrykt hos dig.
8 Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
Mine helligdommer foraktet du, og mine sabbater vanhelliget du.
9 A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
Baktalere stod frem hos dig for å utøse blod, og på dine fjell blev der ett avgudsoffer; skjenselsgjerninger skjedde hos dig.
10 A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
Farens blusel blottedes hos dig; en kvinne som var uren i sin månedlige svakhet, krenkedes hos dig.
11 A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
En bar sig vederstyggelig at mot sin næstes hustru, og en annen vanæret sin sønnekone i skammelig utukt, atter en annen krenket sin søster, sin fars datter, hos dig.
12 A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Gaver tok de hos dig for å utøse blod; rente og overmål tok du, og mot din næste gjorde du urett og vold, og mig glemte du, sier Herren, Israels Gud.
13 “‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
Men se, jeg har slått mine hender sammen over den urettferdige vinning du har samlet dig, og over det blod du har utøst i din midte.
14 Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
Skal ditt hjerte holde stand eller dine hender ha sin styrke i de dager da jeg vil ha med dig å gjøre? Jeg, Herren, har sagt det, og jeg skal gjøre det.
15 Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
Jeg vil sprede dig iblandt folkene og strø dig omkring i landene, og jeg vil ta bort fra dig all din urenhet.
16 Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
Du skal bli vanhelliget ved din egen skyld for folkenes øine, og du skal kjenne at jeg er Herren.
17 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Og Herrens ord kom til mig, og det lød så:
18 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
Menneskesønn! Israels hus er blitt mig til slagg; de er alle sammen som kobber og tinn og jern og bly i en ovn; sølvslagg er de blitt.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
Derfor sier Herren, Israels Gud, så: Fordi I alle er blitt til slagg, se, derfor vil jeg samle eder sammen i Jerusalem.
20 Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
Likesom en samler sølv og kobber og jern og bly og tinn i en ovn og blåser ild på det for å smelte det, således vil jeg samle eder i min vrede og min harme og legge eder i ovnen og smelte eder.
21 Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
Ja, jeg vil samle eder og blåse på eder med min vredes ild, og I skal smeltes i den;
22 Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
som sølv smeltes i en ovn, således skal I smeltes i den, og I skal kjenne at jeg, Herren, har utøst min harme over eder.
23 Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
Og Herrens ord kom til mig, og det lød så:
24 “Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
Menneskesønn! Si til det: Du er et land som ikke er renset, som ikke har fått skyllregn på vredens dag.
25 Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
De profeter det har i sin midte, er en flokk av sammensvorne; de er lik en brølende løve, som raner og røver; de fortærer menneskeliv, de tar gods og kostbarheter; de gjør mange til enker der.
26 Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
Dets prester gjør vold på min lov og vanhelliger mine helligdommer; mellem hellig og vanhellig gjør de ingen forskjell, og de lærer ikke å skjelne mellem urent og rent; for mine sabbater lukker de sine øine, og jeg blir vanhelliget midt iblandt dem.
27 Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
De fyrster det har i sin midte, er lik ulver, som raner og røver; de utøser blod, de ødelegger menneskeliv for å samle urettferdig vinning.
28 Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
Dets profeter stryker over med kalk for dem; de skuer tomhet og spår dem løgn og sier: Så sier Herren, Israels Gud - enda Herren ikke har talt.
29 Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
Folket i landet gjør voldsverk og raner og røver, og den elendige og fattige undertrykker de, og mot den fremmede gjør de voldsverk uten lov og rett.
30 “Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
Jeg søkte blandt dem efter en mann som vilde mure op en mur og stille sig i gapet for mitt åsyn til vern for landet, så jeg ikke skulde ødelegge det; men jeg fant ingen.
31 Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Så utøser jeg da min vrede over dem; ved min harmes ild gjør jeg ende på dem; deres gjerninger lar jeg komme over deres eget hode, sier Herren, Israels Gud.

< Ezekiyel 22 >