< Ezekiyel 22 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Ilizwi leNkosi laselifika kimi lisithi:
2 “Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
Wena-ke, ndodana yomuntu, uzakwehlulela yini, wahlulele umuzi wegazi? Yebo uzawazisa zonke izinengiso zawo.
3 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
Ubususithi: Itsho njalo iNkosi uJehova: Umuzi ochitha igazi phakathi kwawo, ukuze isikhathi sawo sifike, wenze izithombe ezimelene lawo, ukuze uzingcolise.
4 kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
Wena usulecala ngegazi olichithileyo, wazingcolisa ngezithombe zakho ozenzileyo, wasondeza insuku zakho, usufikile eminyakeni yakho. Ngalokho ngikwenzile waba lihlazo ezizweni lenhlekisa kuwo wonke amazwe.
5 Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
Abaseduze labakhatshana lawe bazakuhleka usulu, wena ongcolileyo ngebizo, ogcwele isiphithiphithi.
6 “‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
Khangela, iziphathamandla zakoIsrayeli zaziphakathi kwakho, yileso laleso ngengalo yaso, ukuthi sichithe igazi.
7 A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
Baphathe uyihlo lonyoko ngokweyisa kuwe; benze ngocindezelo kowemzini phakathi kwakho; bacindezele izintandane lomfelokazi kuwe.
8 Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
Uzidelele izinto zami ezingcwele, wangcolisa amasabatha ami.
9 A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
Abantu abahlebayo babekuwe ukuze bachithe igazi; badla kuwe phezu kwezintaba; benza amanyala phakathi kwakho.
10 A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
Bembule ubunqunu baboyise phakathi kwakho; bathobise kuwe owesifazana ongcoliswe yikuba semfuleni.
11 A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
Futhi omunye wenze amanyala lomfazi kamakhelwane wakhe, lomunye wangcolisa umalokazana wakhe ngokuhlazisayo, lomunye uthobise udadewabo phakathi kwakho, indodakazi kayise.
12 A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Phakathi kwakho bemukele izipho ukuze bachithe igazi; uyemukela inzalo lokwengezelelweyo, uphangile umakhelwane wakho ngocindezelo, wangikhohlwa, itsho iNkosi uJehova.
13 “‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
Khangela-ke ngitshayile isandla sami ngenzuzo yakho embi oyenzileyo, langegazi lakho ebeliphakathi kwakho.
14 Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
Inhliziyo yakho izakuma yini, kumbe izandla zakho ziqine, ensukwini engizaphathana lawe kizo? Mina Nkosi ngikhulumile, njalo ngizakwenza.
15 Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
Ngikuhlakaze phakathi kwezizwe, ngikusabalalise phakathi kwamazwe, ngiqede ukungcola kwakho kuwe.
16 Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
Njalo uzangcoliswa phakathi kwakho emehlweni abezizwe; ubususazi ukuthi ngiyiNkosi.
17 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Ilizwi leNkosi laselifika kimi lisithi:
18 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
Ndodana yomuntu, indlu kaIsrayeli isibengamanyele kimi; bonke balithusi, lezenge, lensimbi, lomnuso, phakathi kwesithando; bangamanyele esiliva.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
Ngakho itsho njalo iNkosi uJehova: Ngoba lonke selibengamanyele, ngakho khangelani, ngizalibuthelela phakathi kweJerusalema.
20 Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
Njengoba bebuthelela isiliva lethusi lensimbi lomnuso lezenge phakathi kwesithando, ukuze bafuthe umlilo phezu kwakho ukukuncibilikisa; ngokunjalo ngizalibuthelela ekuthukutheleni kwami lelakeni lwami, ngilitshiye, ngilincibilikise.
21 Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
Yebo, ngizalibuthelela, ngivuthele phezu kwenu emlilweni wentukuthelo yami, beselincibilikiswa phakathi kwawo.
22 Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
Njengesiliva sincibilikiswa phakathi kwesithando, ngokunjalo lizancibilikiswa phakathi kwaso; njalo lizakwazi ukuthi mina Nkosi ngithulule ulaka lwami phezu kwenu.
23 Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
Ilizwi leNkosi laselifika kimi lisithi:
24 “Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
Ndodana yomuntu, wothi kiyo: Wena uyilizwe elingahlanjululwanga, lelinganethwanga ngosuku lwentukuthelo.
25 Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
Ugobe lwabaprofethi bayo phakathi kwayo lunjengesilwane esibhongayo esidlithiza impango; bayidlile imiphefumulo, bathatha inotho lezinto eziligugu, benza abafelokazi baba banengi phakathi kwayo.
26 Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
Abapristi bayo baphathe umlayo wami ngodlakela, bangcolisa izinto zami ezingcwele; kabenzanga mehluko phakathi kokungcwele lokungcolileyo; kabazisanga umehluko phakathi kokungcolileyo lokuhlambulukileyo; bafihla amehlo abo kumasabatha ami; ngakho ngangcoliswa phakathi kwabo.
27 Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
Iziphathamandla zayo phakathi kwayo zinjengezimpisi ezidlithiza impango, ukuthi zichithe igazi, zibhubhise imiphefumulo, ukuze zizuze inzuzo embi.
28 Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
Labaprofethi bayo babacombe ngekalaga, bebona okuyize, bebavumisa amanga, besithi: Itsho njalo iNkosi uJehova; kanti iNkosi ingakhulumanga.
29 Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
Abantu belizwe bacindezele ngocindezelo, baphanga impango, bacindezela umyanga loswelayo, bacindezela owezizwe kungelakulunga.
30 “Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
Njalo ngadinga umuntu phakathi kwabo ongabiya uthango, ame esikhexeni phambi kwami emele ilizwe ukuze ngingalichithi, kodwa kangimtholanga.
31 Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Ngakho ngithululele intukuthelo yami phezu kwabo, ngibaqede ngomlilo wolaka lwami; ngehlisele indlela yabo phezu kwekhanda labo, itsho iNkosi uJehova.

< Ezekiyel 22 >