< Ezekiyel 22 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l'Eternel me fut encore [adressée], en disant:
2 “Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
Et toi, fils d'homme, ne jugeras-tu pas, ne jugeras-tu pas la ville sanguinaire, et ne lui donneras-tu pas à connaître toutes ses abominations?
3 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
Tu diras donc, ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: ville qui répands le sang au dedans de toi, afin que ton temps vienne, et qui as fait des idoles à ton préjudice, pour [en] être souillée.
4 kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
Tu t'es rendue coupable par ton sang que tu as répandu, et tu t'es souillée par tes idoles que tu as faites; tu as fait approcher tes jours, et tu es venue jusqu'à tes ans; c'est pourquoi je t'ai exposée en opprobre aux nations, et en dérision à tous les pays.
5 Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
Celles qui sont près de toi, et celles qui [en] sont loin, se moqueront de toi, infâme de réputation, et remplie de troubles.
6 “‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
Voici, les Princes d'Israël ont contribué au dedans de toi, chacun selon sa force, à répandre le sang.
7 A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
On a méprisé père et mère au dedans de toi; on a usé de tromperie à l'égard de l'étranger au dedans de toi; on a opprimé l'orphelin et la veuve au dedans de toi.
8 Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
Tu as méprisé mes choses saintes, et profané mes Sabbats.
9 A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
Des gens médisants ont été au dedans de toi pour répandre le sang, et ceux qui sont au dedans de toi ont mangé sur les montagnes; on a commis des actions énormes au milieu de toi.
10 A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
[L'enfant] a découvert la nudité du père au dedans de toi, et on a humilié au dedans de toi la femme dans le temps de sa souillure.
11 A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
Et l'un a commis abomination avec la femme de son prochain; et l'autre en commettant des actions énormes a souillé sa belle-fille; et l'autre a humilié sa sœur, fille de son père, au dedans de toi.
12 A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
On a reçu au dedans de toi des présents pour répandre le sang; tu as pris de l'usure et du surcroît; et tu as fait un gain déshonnête sur tes prochains, en usant de tromperie; et tu m'as oublié, dit le Seigneur l'Eternel.
13 “‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
Et voici, j'ai frappé de mes mains l'une contre l'autre à cause de ton gain déshonnête que tu as fait, et à cause de ton sang qui a été répandu au dedans de toi.
14 Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
Ton cœur pourra-t-il tenir ferme? ou tes mains seront-elles fortes aux jours que j'agirai contre toi? moi l'Eternel j'ai parlé, et je le ferai.
15 Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
Et je te disperserai parmi les nations, je te vannerai par les pays, et je consumerai ta souillure, jusqu'à ce qu'il n'y en ait plus en toi.
16 Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
Et tu seras partagée en toi-même en la présence des nations, et tu sauras que je suis l'Eternel.
17 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Puis la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
18 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
Fils d'homme: la maison d'Israël m'est devenue [comme] de l'écume; eux tous sont de l'airain, de l'étain, du fer et du plomb dans un creuset; ils sont devenus [comme] une écume d'argent.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: parce que vous êtes tous devenus [comme] de l'écume, voici, je vais à cause de cela vous assembler au milieu de Jérusalem,
20 Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
Comme qui assemblerait de l'argent, de l'airain, du fer, du plomb, et de l'étain dans un creuset, afin d'y souffler le feu pour les fondre; je vous assemblerai ainsi en ma colère, et en ma fureur, je me satisferai, et je vous fondrai.
21 Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
Je vous assemblerai donc, je soufflerai contre vous le feu de ma fureur, et vous serez fondus au milieu de [Jérusalem].
22 Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
Comme l'argent se fond dans le creuset, ainsi vous serez fondus au milieu d'elle, et vous saurez que moi l'Eternel j'ai répandu ma fureur sur vous.
23 Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
La parole de l'Eternel me fut encore [adressée], en disant:
24 “Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
Fils d'homme, dis-lui: tu es une terre qui n'a pas été nettoyée ni mouillée de pluie au jour de l'indignation.
25 Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
Il y a un complot de ses Prophètes au milieu d'elle; ils seront comme des lions rugissants, qui ravissent la proie: ils ont dévoré les âmes; ils ont emporté les richesses, et la gloire; ils ont multiplié les veuves au milieu d'elle.
26 Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
Ses Sacrificateurs ont fait violence à ma Loi; et ont profané mes choses saintes; ils n'ont point mis différence entre la chose sainte et la profane, ils n'ont point donné à connaître [la différence qu'il y a] entre la chose immonde et la nette, et ils ont caché leurs yeux de mes Sabbats, et j'ai été profané au milieu d'eux.
27 Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
Ses principaux ont été au milieu d'elle comme des loups qui ravissent la proie, pour répandre le sang et pour détruire les âmes, pour s'adonner au gain déshonnête.
28 Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
Ses Prophètes aussi les ont enduits de mortier mal lié; ils ont des visions fausses, et ils leur devinent le mensonge, en disant: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel; et cependant l'Eternel n'avait point parlé.
29 Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
Le peuple du pays a usé de tromperies, et ils ont ravi le bien d'autrui, et ont opprimé l'affligé et le pauvre, et ont foulé l'étranger contre tout droit.
30 “Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
Et j'ai cherché quelqu'un d'entre eux qui refît la cloison, et qui se tînt à la brèche devant moi pour le pays, afin que je ne le détruisisse point; mais je n'en ai point trouvé.
31 Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
C'est pourquoi je répandrai sur eux mon indignation, et je les consumerai par le feu de ma fureur; je ferai tomber la peine de leur train sur leur tête, dit le Seigneur l'Eternel.

< Ezekiyel 22 >