< Ezekiyel 22 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came unto me, saying,
2 “Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
And thou, son of man, wilt thou take to task, wilt thou take to task the city of blood? and wilt thou make her know all her abominations?
3 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
Then say thou, Thus hath said the Lord Eternal, O city that sheddeth blood in her midst, that her time [of sorrow] may come, and that hath made idols for herself to become unclean:
4 kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
Through thy blood which thou hast shed, are thou become guilty; and through thy idols which thou hast made art thou become unclean; and thou hast caused thy days [of destruction] to draw near, and thou art come even unto thy years; therefore do I make thee a disgrace unto the nations, and a mocking to all the countries.
5 Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
Those who are near, and those who are far from thee, shall mock thee, O thou unclean in name, and great in confusion!
6 “‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
Behold, the princes of Israel were each [ready] with his arm within thee, in order to shed blood.
7 A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
Father and mother they esteemed lightly within thee, toward the stranger they acted with extortion in the midst of thee, the fatherless and the widow they oppressed within thee.
8 Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
My holy things thou didst despise, and my sabbaths thou didst profane.
9 A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
Tale-bearers [also] were within thee, in order to shed blood; and upon the mountains did they eat within thee; incest did they commit in the midst of thee.
10 A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
Their father's nakedness they uncovered within thee; her that was unclean in her separation did they violate within thee.
11 A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
And one with his neighbor's wife did commit abomination; and another did defile his daughter-in-law with incest; and another did violate his sister, the daughter of his father, within thee.
12 A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Bribes they took within thee, in order to shed blood; interest and increase didst thou take, and thou didst acquire gain off thy neighbors by extortion: and me thou didst forget, saith the Lord Eternal.
13 “‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
And behold, I have struck my hands together at thy wrongful gain which thou hast acquired, and at thy blood-guilt which hath been in the midst of thee.
14 Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
Will thy courage endure, or will thy hands remain strong, on the days that I will deal with thee? I the Lord have spoken, and will do it.
15 Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
And I will scatter thee among the nations, and disperse thee in the countries, and I will entirely remove thy uncleanness out of thee.
16 Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
And thou shalt be degraded through thyself before the eyes of nations, and thou shalt know that I am the Lord.
17 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came unto me, saying,
18 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
Son of man, the house of Israel are become to me dross: they all are copper, and tin, and iron, and lead, in the midst of the furnace; the dross of silver are they become.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
Therefore thus hath said the Lord Eternal, Because ye are all become dross, therefore, behold, I will gather you into the midst of Jerusalem.
20 Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
As silver, and copper, and iron, and lead, and tin are gathered into the midst of the furnace, to blow the fire upon it, to melt it: so will I gather you in my anger and in my fury and I will lay you down there, and melt you.
21 Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
Yea, I will assemble you in a heap, and blow upon you with the fire of my wrath, and ye shall be melted in the midst of it.
22 Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
As silver is melted in the midst of the furnace, so shall ye be melted in the midst of it: and ye shall know that I am the Lord who have poured out my fury over you.
23 Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
And the word of the Lord came unto me, saying,
24 “Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
Son of man, say unto her, Thou art a land that is not cleansed; [and] which is not rained upon on the day of indignation.
25 Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
The banded troop of her prophets in the midst of her is like a roaring lion that teareth in pieces the prey: souls do they devour; wealth and precious things do they take away; the number of her widows do they increase in the midst of her.
26 Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
Her priests violate my law, and profane my holy things: between the holy and profane do they make no distinction, and the difference between the unclean and the clean do they not make known, and from [the violation of] my sabbaths do they turn away their eyes, so that I am profaned among them.
27 Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
Her princes in her midst are like wolves that tear in pieces the prey, to shed blood, to destroy souls, in order to obtain selfish gain.
28 Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
And her prophets plastered for them with unadhesive mortar, foreseeing falsehood, and divining unto them lies, saying, Thus hath said the Lord Eternal; when the Lord had not spoken.
29 Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
The people of the land are guilty of extortion, and practise robbery, and the poor and the needy they defraud: and they extort from the stranger with injustice.
30 “Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
And I seek now among them for a man, that could erect a fence, and stand in the breach before me in behalf of the land, so that I should not destroy it; but I find none.
31 Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
And I therefore pour out over them my indignation; with the fire of my wrath do I make an end of them: their own way do I bring upon their head, saith the Lord Eternal.