< Ezekiyel 22 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying:
2 “Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
“And you, son of man, should you not judge, should you not judge the city of blood?
3 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
And you shall reveal to her all her abominations. And you shall say: Thus says the Lord God: This is the city which sheds blood in her midst, so that her time may come, and which has made idols against herself, so that she may be defiled.
4 kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
You have offended by your blood, which you shed from yourself. And you have been defiled by your idols which you yourself made. And you have caused your days to approach, and you have brought on the time of your years. Because of this, I have made you a disgrace to the Gentiles, and a derision to all the lands.
5 Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
Those that are near and those that are far from you will triumph over you. You are filthy, infamous, great in destruction.
6 “‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
Behold, the leaders of Israel have each used his arm to shed blood within you.
7 A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
They have abused father and mother within you. The new arrival has been oppressed in your midst. They have grieved the orphan and the widow among you.
8 Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
You have spurned my sanctuaries, and you have defiled my Sabbaths.
9 A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
Maligning men were within you, in order to shed blood, and they have eaten upon the mountains within you. They have worked wickedness in your midst.
10 A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
They have uncovered the nakedness of their father within you. They have debased the uncleanness of the menstruous woman within you.
11 A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
And each one has committed abomination with the wife of his neighbor. And the father-in-law has heinously defiled his daughter-in-law. The brother has oppressed his sister, the daughter of his father, within you.
12 A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
They have accepted bribes among you to shed blood. You have received usury and superabundance, and in avarice you have oppressed your neighbors. And you have forgotten me, says the Lord God.
13 “‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
Behold, I have clapped my hands over your avarice, which you have worked, and over the blood that has been shed in your midst.
14 Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
How can your heart endure, or your hands prevail, in the days that I will bring upon you? I, the Lord, have spoken, and I will act.
15 Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
And I will disperse you among the nations, and I will scatter you among the lands, and I will cause your uncleanness to fade away from you.
16 Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
And I will possess you in the sight of the Gentiles. And you shall know that I am the Lord.”
17 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying:
18 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
“Son of man, the house of Israel has become like dross to me. All these are brass, and tin, and iron, and lead in the midst of the furnace; they have become like the dross of silver.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
Because of this, thus says the Lord God: Since you have all turned into dross, therefore, behold, I will gather you together in the midst of Jerusalem,
20 Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
just as they gather silver, and brass, and tin, and iron, and lead in the midst of the furnace, so that I may kindle in it a fire to melt it. So will I gather you together in my fury and in my wrath, and I will be quieted, and I will melt you down.
21 Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
And I will gather you together, and I will burn you in the fire of my fury, and you will be melted in its midst.
22 Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
Just as silver is melted in the midst of the furnace, so will you be in its midst. And you shall know that I am the Lord, when I will have poured out my indignation upon you.”
23 Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
And the word of the Lord came to me, saying:
24 “Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
“Son of man, say to her: You are a land unclean and not rained upon, in the day of fury.
25 Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
There is a conspiracy of prophets in her midst. Like a lion, roaring and seizing the prey, they have devoured souls. They have taken riches and a price. They have multiplied widows in her midst.
26 Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
Her priests have despised my law, and they have defiled my sanctuaries. They have held no distinction between holy and profane. And they have not understood the difference between defiled and clean. And they have averted their eyes from my Sabbaths. And I was profaned in their midst.
27 Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
Her leaders in her midst are like wolves seizing the prey: to shed blood, and to perish souls, and to continually pursue profit with avarice.
28 Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
And her prophets have covered them without tempering the mortar, seeing emptiness, and divining lies for them, saying, ‘Thus says the Lord God,’ when the Lord has not spoken.
29 Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
The people of the land have oppressed with slander and have seized with violence. They have afflicted the needy and the poor, and they have oppressed the new arrival by accusations without judgment.
30 “Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
And I sought among them for a man who might set up a hedge, and stand in the gap before me on behalf of the land, so that I might not destroy it; and I found no one.
31 Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
And so I poured out my indignation upon them; in the fire of my wrath I consumed them. I have rendered their own way upon their head, says the Lord God.”

< Ezekiyel 22 >