< Ezekiyel 22 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Moreover the word of Jehovah came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
And thou, son of man, will thou judge, will thou judge the bloody city? Then cause her to know all her abominations.
3 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
And thou shall say, Thus says the lord Jehovah: A city that sheds blood in the midst of her, that her time may come, and who makes idols against herself to defile her!
4 kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
Thou have become guilty in thy blood that thou have shed, and are defiled in thine idols which thou have made. And thou have caused thy days to draw near, and have come even to thy years. Therefore I have made thee a reproach to the nations, and a mocking to all the countries.
5 Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
Those that are near, and those that are far from thee, shall mock thee, thou infamous one, full of tumult.
6 “‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
Behold, the rulers of Israel, each one according to his power, have been in thee to shed blood.
7 A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
In thee they have made light of father and mother. In the midst of thee they have dealt with the sojourner by oppression. In thee they have wronged the fatherless and the widow.
8 Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
Thou have despised my holy things, and have profaned my sabbaths.
9 A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
Slanderous men have been in thee to shed blood, and in thee they have eaten upon the mountains. In the midst of thee they have committed lewdness.
10 A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
In thee they have uncovered their fathers' nakedness. In thee they have humbled her who was unclean in her impurity.
11 A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
And one has committed abomination with his neighbor's wife, and another has lewdly defiled his daughter-in-law, and another in thee has humbled his sister, his father's daughter.
12 A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
In thee they have taken bribes to shed blood. Thou have taken interest and increase. And thou have greedily gained from thy neighbors by oppression, and have forgotten me, says the lord Jehovah.
13 “‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
Behold, therefore, I have smitten my hand at thy dishonest gain which thou have made, and at thy blood which has been in the midst of thee.
14 Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
Can thy heart endure, or can thy hands be strong, in the days that I shall deal with thee? I, Jehovah, have spoken it, and will do it.
15 Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
And I will scatter thee among the nations, and disperse thee through the countries, and I will consume thy filthiness out of thee.
16 Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
And thou shall be profaned in thyself, in the sight of the nations. And thou shall know that I am Jehovah.
17 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of Jehovah came to me, saying,
18 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
Son of man, the house of Israel has become dross to me. All of them are brass, and tin, and iron, and lead, in the midst of the furnace. They are the dross of silver.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
Therefore thus says the lord Jehovah: Because ye have all become dross, therefore, behold, I will gather you into the midst of Jerusalem
20 Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
as they gather silver and brass and iron and lead and tin into the midst of the furnace, to blow the fire upon it, to melt it. So I will gather you in my anger and in my wrath, and I will lay you there, and melt you.
21 Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
Yea, I will gather you, and blow upon you with the fire of my wrath, and ye shall be melted in the midst of it.
22 Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
As silver is melted in the midst of the furnace, so ye shall be melted in the midst of it. And ye shall know that I, Jehovah, have poured out my wrath upon you.
23 Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
And the word of Jehovah came to me, saying,
24 “Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
Son of man, say to her, Thou are a land that is not cleansed, nor rained upon in the day of indignation.
25 Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
There is a conspiracy by her prophets in the midst of it, like a roaring lion ravening the prey. They have devoured souls. They take treasure and precious things. They have made her widows many in the midst thereof.
26 Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
Her priests have done violence to my law, and have profaned my holy things. They have made no distinction between the holy and the common, nor have they caused men to discern between the unclean and the clean, and have hid their eyes from my sabbaths, and I am profaned among them.
27 Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
Her rulers in the midst of it are like wolves ravening the prey, to shed blood, to destroy souls, that they may get dishonest gain.
28 Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
And her prophets have daubed for them with untempered mortar, seeing false visions, and divining lies to them, saying, Thus says the lord Jehovah, when Jehovah has not spoken.
29 Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
The people of the land have used oppression, and exercised robbery. Yea, they have vexed the poor and needy man, and have oppressed the sojourner wrongfully.
30 “Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
And I sought for a man among them who should build up the wall, and stand in the gap before me for the land, that I should not destroy it, but I found none.
31 Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Therefore I have poured out my indignation upon them. I have consumed them with the fire of my wrath. I have brought their own way upon their heads, says the lord Jehovah.