< Ezekiyel 22 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Opět stalo se slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
2 “Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
Ty pak synu člověčí, zastával-li bys, zastával-liž bys toho města vražedlného? Raději mu oznam všecky ohavnosti jeho,
3 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
A rci: Takto praví Panovník Hospodin: Přicházíť čas města toho, jenž prolévá krev u prostřed sebe, a dělá ukydané bohy proti sobě, aby se poškvrňovalo.
4 kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
Ty krví svou, kterouž jsi prolilo, zavinivší, a ukydanými bohy svými, jichž jsi nadělalo, sebe poškvrnivší, to jsi způsobilo, že se přiblížili dnové tvoji, a přišlo jsi k letům svým. Protož vydám tě v pohanění národům, a ku posměchu všechněm zemím.
5 Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
Blízké i daleké od tebe budou se tobě posmívati, ó zlopověstné a různic plné.
6 “‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
Aj, knížata Izraelská jeden každý vší silou na to se vydali, aby krev v tobě prolévali.
7 A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
Otce i matku zlehčují v tobě, pohostinnému činí nátisk u prostřed tebe, sirotka a vdovu utiskují v tobě.
8 Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
Svatými věcmi mými zhrdáš, a sobot mých poškvrňuješ.
9 A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
Utrhači jsou v tobě, aby prolévali krev, a na horách jídají v tobě; nešlechetnost páší u prostřed tebe.
10 A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
Nahotu otce syn odkrývá v tobě, a nečisté v oddělení ponižují v tobě.
11 A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
Jiný pak s ženou bližního svého páše ohavnost, a jiný s nevěstou svou poškvrňuje se nešlechetností, a jiný sestry své, dcery otce svého, ponižuje v tobě.
12 A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Dar berou v tobě, aby krev prolili; lichvu a úrok béřeš, a zisku hledáš s útiskem bližního svého, na mne se pak zapomínáš, dí Panovník Hospodin.
13 “‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
Protož aj, já tleskl jsem rukama svýma nad ziskem tvým, jehož dobýváš, i nad tou krví, kteráž byla u prostřed tebe.
14 Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
Zdali ostojí srdce tvé? Zdaž odolají ruce tvé dnům, v nichž já budu zacházeti s tebou? Já Hospodin mluvil jsem i učiním.
15 Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
Nebo rozptýlím tě mezi pohany, a rozženu tě po krajinách, a do konce vyprázdním nečistotu tvou z tebe.
16 Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
A zavrženo jsuc před očima pohanů, poznáš, že já jsem Hospodin.
17 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Potom stalo se slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
18 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
Synu člověčí, obrátili se mi dům Izraelský v trůsku, všickni napořád jsou měď, cín, železo a olovo u prostřed peci, trůsky stříbra jsou.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
Pročež takto praví Panovník Hospodin: Proto že jste vy všickni obrátili se v trůsky, protož aj, já shromáždím vás do Jeruzaléma.
20 Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
Jakž se shromažďuje stříbro a měď, železo, olovo i cín do prostřed peci, k rozdmýchání ohně vůkol něho a k rozpouštění: tak shromáždím v hněvě a v prchlivosti své, a slože, rozpouštěti vás budu.
21 Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
Sberu vás, pravím, a rozdmýchám okolo vás oheň prchlivosti své, i rozpustíte se u prostřed města.
22 Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
Jakž se stříbro rozpouští v peci, tak se rozpustíte u prostřed něho, i zvíte, že já Hospodin vylil jsem prchlivost svou na vás.
23 Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
Ještě stalo se slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
24 “Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
Synu člověčí, rci: Ty země jsi nečistá, nebudeš deštěm svlažena v den rozhněvání.
25 Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
Spiknutí proroků jejích u prostřed ní, jsou podobni lvu řvoucímu, uchvacujícímu loupež, duše žerou, bohatství a věci drahé berou, a činí mnoho vdov u prostřed ní.
26 Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
Kněží její natahují zákona mého, a svaté věci mé poškvrňují, mezi svatým a poškvrněným rozdílu nečiní, a mezi nečistým a čistým nerozeznávají. Nadto od sobot mých skrývají oči své, tak že zlehčován bývám mezi nimi.
27 Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
Knížata její u prostřed ní jsou jako vlci uchvacující loupež, vylévajíce krev, hubíce duše, aby sháněli mrzký zisk.
28 Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
Proroci pak jejich obmítají jim vápnem ničemným, předpovídají marné věci, a hádají jim lež, říkajíce: Takto praví Panovník Hospodin, ješto Hospodin nemluvil.
29 Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
Lid této země činí nátisk, a cizí věci mocí béře, chudému a nuznému ubližují, a pohostinného utiskují nespravedlivě.
30 “Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
Hledaje pak někoho z nich, kterýž by udělal hradbu, a postavil se v mezeře před tváří mou za tuto zemi, abych jí nezkazil, žádného nenacházím.
31 Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Protož vyleji na ně rozhněvání své, ohněm prchlivosti své konec jim učiním, cestu jejich jim na hlavu obrátím, praví Panovník Hospodin.