< Ezekiyel 21 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
In k meni je prišla Gospodova beseda, rekoč:
2 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka gāba da Urushalima ka kuma yi wa’azi a kan wuri mai tsarki. Ka yi annabci gāba da ƙasar Isra’ila
»Človeški sin, naravnaj svoj obraz proti Jeruzalemu in spusti svojo besedo proti svetim krajem in prerokuj zoper Izraelovo deželo
3 ka faɗa mata, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina gāba da ke. Zan ja takobina daga kubensa in karkashe adalai da mugaye daga cikinki.
in reci Izraelovi deželi: ›Tako govori Gospod: ›Glej, jaz sem zoper tebe in izvlekel bom svoj meč iz nožnice in iz tebe bom iztrebil pravičnega in zlobnega.
4 Domin zan karkashe adalai da kuma mugaye, ba zan rufe takobina a kan kowa daga kudu zuwa arewa ba.
Ker bom iz tebe iztrebil pravičnega in zlobnega, bo zato moj meč šel iz nožnice zoper vse meso od juga do severa,
5 Sa’an nan duka mutane za su san cewa Ni Ubangiji na ja takobina daga kubensa; ba zai sāke koma kuma ba.’
da bo lahko vse meso vedelo, da sem jaz, Gospod, izvlekel svoj meč iz nožnice. Ta se ne bo več vrnil.
6 “Saboda ka yi nishi, ɗan mutum! Yi nishi a gabansu da ajiyar zuciya da ɓacin rai.
Zdihuj torej, ti, človeški sin, s trganjem svojih ledij; in z grenkim vzdihom pred njihovimi očmi.
7 Kuma sa’ad da suka tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Domin labarun da suke fitowa. Kowace zuciya za tă narke kowane hannu kuma ya gurgunta; kowane ruhu zai sume kowane gwiwa kuma ta rasa ƙarfi kamar ruwa.’ Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
In zgodilo se bo, ko ti bodo rekli: ›Zakaj vzdihuješ?‹ da boš odgovoril: ›Zaradi novic, ker le-te prihajajo.‹ In vsako srce se bo stopilo in vse roke bodo slabotne in vsak duh bo medlel in vsa kolena bodo šibka kakor voda. Glej, to prihaja in se bo zgodilo, ‹ govori Gospod Bog.«
8 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Ponovno je prišla k meni Gospodova beseda, rekoč:
9 “Ɗan mutum, yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Takobi, takobi, wasasshe da kuma gogagge,
»Človeški sin, prerokuj in reci: ›Tako govori Gospod: ›Reci: ›Meč, meč je nabrušen in tudi zglajen.
10 wasasshe don kisa, gogagge har yana walwal kamar walƙiya! “‘Kada ku yi farin ciki, hukunci yana zuwa, domin kowa ya ƙi jin abin da na yi gargaɗi a kai.
Nabrušen je, da naredi boleč pokol; zglajen je, da se lahko lesketa. Naj bi se mi potem razveseljevali? Ta zaničuje palico mojega sina kakor vsako drevo.
11 “‘An ba da wannan takobi don a goge, don a kama da hannu; an washe shi aka kuma goge, shiryayye don a yi kisa da shi.
In on ga je dal zgladiti, da bi lahko z njim rokoval. Ta meč je nabrušen in zglajen, da ga da v roko ubijalca.
12 Ka yi kuka ka yi makoki, ɗan mutum, gama yana gāba da dukan sarakunan Isra’ila. An jefa su ga takobi tare da jama’ata. Saboda haka ku buga ƙirjinku.
Jokaj in tuli, človeški sin, kajti ta bo nad mojim ljudstvom, ta bo nad Izraelovimi princi. Strahote zaradi meča bodo nad mojim ljudstvom. Udari torej na svoje stegno.
13 “‘Gwaji tabbatacce zai zo. Kuma a ce sandan Yahuda, wanda takobi ya ƙi, ya ci gaba? In ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
Ker je to preizkušnja in kaj če meč zaničuje celo palico? To ne bo več, ‹ govori Gospod Bog.
14 “Saboda haka fa, ɗan mutum ka yi annabci ka kuma tafa hannuwanka. Bari takobi ya yi sara sau biyu, har sau uku ma. Takobin kisa ne, takobi ne don kisa mai girma, zai kewaye su a kowane gefe.
›Ti torej, človeški sin, prerokuj in zaploskaj s svojima rokama in naj bo meč tretjič podvojen, meč umorjenih. To je meč velikih ljudi, ki so umorjeni, ki vstopa v njihove skrivne sobe.
15 Domin zukata su narke da yawa kuma su fāɗi, na tsai da takobin kisa a dukan ƙofofinsu. Kash! A sa ya haska kamar walƙiya, ana riƙe da shi don kisa.
Konico meča sem naravnal zoper vsa njihova velika vrata, da bo njihovo srce lahko slabelo in [bodo] njihovi propadi pomnoženi. Ah! Narejen je [da se] lesketa, zavit je za pokol.
16 Ya takobi, yi sara zuwa dama ka yi kuma zuwa hagu, duk inda aka juya ka.
Pojdi eno pot ali drugo, ali na desno ali na levo, kamor je naravnan tvoj obraz.
17 Zan tafa hannuwana, fushina kuwa zai sauka. Ni Ubangiji na faɗa.”
Tudi jaz bom plosknil s svojima rokama in bom umiril svojo razjarjenost. Jaz, Gospod, sem to govoril.‹«
18 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Ponovno je prišla k meni Gospodova beseda, rekoč:
19 “Ɗan mutum, ka nuna hanyoyi biyu inda takobin sarkin Babilon zai bi, duka biyun su fara daga ƙasa guda. Ka kafa shaida inda hanyar za tă rabu zuwa cikin birni.
»Tudi ti, človeški sin, si določi dve poti, da bo lahko prišel meč babilonskega kralja. Obe bosta izšli iz ene dežele in izberi kraj, izberi ga ob začetku poti v mesto.
20 Ka nuna hanya guda wadda takobi zai fāɗo wa Rabba ta Ammonawa ɗayan kuma da zai fāɗo a kan Yahuda da kuma Urushalima mai katanga.
Določi pot, da lahko pride meč v Rabo Amóncev in v Juda in zaščiteno [prestolnico] Jeruzalem.
21 Gama sarkin Babilon zai tsaya a mararrabar hanya, a inda hanyar ta rabu biyu, don yă yi duba. Zai jefa ƙuri’a da kibiyoyinsa, zai nemi shawarar gumakansa, zai bincike hanta.
Kajti babilonski kralj je stal pri razpotju poti, ob začetku dveh poti, da uporabi vedeževanje. Svoje puščice je posvetlil, posvetoval se je z družinskimi maliki, gledal je v jetra.
22 A hannunsa na dama ƙuri’a don Urushalima za tă fito, inda zai kafa dundurusai, ya ba da umarni kisa, a yi kururuwar yaƙi, a kafa dundurusai a kan ƙofofi, a gina mahaurai a kuma yi ƙawanya.
Pri njegovi desni roki je bilo vedeževanje za [prestolnico] Jeruzalem, da določi častnike, da odpre usta v pokol, da povzdigne glas s kričanjem, da določi oblegovalne ovne proti velikim vratom, da nasuje nasip in da zgradi utrdbo.
23 Zai zama kamar duban ƙarya ne ga waɗanda suka yi rantsuwar yin masa biyayya, amma zai tunashe su game da laifinsu ya kuma kama su.
In to jim bo kakor napačno vedeževanje v njihovem pogledu, tistim, ki so prisegli prisege, toda v spomin bo priklical krivičnost, da bodo lahko zajeti.‹
24 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku mutanen nan kun tuna da laifinku ta wurin tawaye, kun kuma bayyana zunubanku cikin dukan abin da kuke yi, domin kun yi haka, za a kama ku.
Zato tako govori Gospod Bog: ›Ker ste storili, da se bo spominjalo vaše krivičnosti v tem, da so vaši prestopki odkriti, tako da se pri vseh vaših dejanjih pojavijo vaši grehi; ker jaz pravim, da ste prišli v spomin, boste zajeti z roko.
25 “‘Ya kai ƙazantaccen mugu, yerima Isra’ila, wanda kwanansa ta zo, wanda lokacin hukuncinsa ya cika fal,
In ti, oskrunjen, zloben Izraelov princ, katerega dan je prišel, ko se krivičnosti naredi konec, ‹
26 ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka kunce rawanin, ka ɗauke rawanin nan. Ba zai zama kamar yadda yake ba. Za a ɗaukaka ƙasƙantacce, amma a ƙasƙantar da mai girma.
tako govori Gospod Bog: ›Odstrani diadem in snemi krono. To ne bo [več] isto. Povišaj tistega, ki je nizek in ponižaj tistega, ki je visok.
27 Hallaka! Hallaka! Zan hallaka shi! Ba za a maido da shi ba sai ya ga ainihin mai shi; gare shi zan bayar da shi.’
Jaz bom to preobrnil, preobrnil, preobrnil in tega ne bo nič več, dokler ne pride tisti, katerega pravica je to in njemu jo bom izročil.‹
28 “Kai kuma, ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da Ammonawa da kuma zarginsu. “‘Takobi, takobi, an ja don kisa, an goge don cinyewa yana haske kamar walƙiya!
Ti pa, človeški sin, prerokuj in reci: ›Tako govori Gospod Bog glede Amóncev in glede njihove graje; celo reci: ›Meč, meč je izvlečen. Za pokol je zglajen, da použiva zaradi lesketanja.
29 Duk da wahayin ƙarya game da kai, duban ƙarya game da kai, za a sa shi a wuyan mugaye waɗanda za a kashe, waɗanda kwanansu ta zo, waɗanda lokacin hukuncinsu ya cika fal.
Medtem ko zate vidijo ničnost, medtem ko ti vedežujejo laž, da te privedejo nad vratove tistih, ki so umorjeni izmed zlobnih, katerih dan je prišel, ko bo njihova krivičnost končana.
30 “‘Ka mai da takobi a kubensa. A inda aka halicce ka, a ƙasar kakanninka, zan hukunta ka.
Ali mu bom povzročil, da se vrne v svojo nožnico? Sodil te bom na kraju, kjer si bil ustvarjen, v deželi tvojega rojstva.
31 Zan zub da hasalata a kanka in hura maka wutar fushina; Zan ba da kai a hannun mugayen mutanen da suka gwanince a hallakarwa.
In nate bom izlil svoje ogorčenje in zoper tebe bom pihal v ognju svojega besa in te izročil v roko brutalnežev in veščih, da uničujejo.
32 Za ka zama itacen wuta, za a zub da jininka a ƙasarka, ba za a ƙara tuna da kai ba; gama Ni Ubangiji na faɗa.’”
Ti boš za gorivo ognju; tvoja kri bo v sredi dežele; ne bo se te več spominjalo, kajti jaz, Gospod, sem to govoril.‹«

< Ezekiyel 21 >