< Ezekiyel 21 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
2 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka gāba da Urushalima ka kuma yi wa’azi a kan wuri mai tsarki. Ka yi annabci gāba da ƙasar Isra’ila
Fils d’un homme, tourne ton visage vers Jérusalem; fais tomber tes paroles sur les sanctuaires, et prophétise contre la terre d’Israël;
3 ka faɗa mata, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina gāba da ke. Zan ja takobina daga kubensa in karkashe adalai da mugaye daga cikinki.
Et tu diras à la terre d’Israël: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Voici que je viens vers toi; et je tirerai le glaive de son fourreau, et je tuerai en toi le juste et l’impie;
4 Domin zan karkashe adalai da kuma mugaye, ba zan rufe takobina a kan kowa daga kudu zuwa arewa ba.
Mais parce que j’ai tué en toi le juste et l’impie, pour cela même mon glaive sortira de son fourreau contre toute chair, du midi jusqu’à l’aquilon;
5 Sa’an nan duka mutane za su san cewa Ni Ubangiji na ja takobina daga kubensa; ba zai sāke koma kuma ba.’
Afin que toute chair sache que moi le Seigneur j’ai tiré de son fourreau mon irrévocable glaive.
6 “Saboda ka yi nishi, ɗan mutum! Yi nishi a gabansu da ajiyar zuciya da ɓacin rai.
Et toi, fils d’un homme, gémis jusqu’au brisement de tes reins, et avec amertume gémis devant eux.
7 Kuma sa’ad da suka tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Domin labarun da suke fitowa. Kowace zuciya za tă narke kowane hannu kuma ya gurgunta; kowane ruhu zai sume kowane gwiwa kuma ta rasa ƙarfi kamar ruwa.’ Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Et lorsqu’ils te diront: Pourquoi gémis-tu? tu diras: À cause de ce que j’ai entendu et qui vient; et tout cœur se fondra, et toutes les mains deviendront défaillantes, et tout esprit sera sans force, et l’eau coulera de tous les genoux; voici que cela vient, et que cela s’accomplira, dit le Seigneur Dieu.
8 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
9 “Ɗan mutum, yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Takobi, takobi, wasasshe da kuma gogagge,
Fils d’un homme, prophétise, et dis: Voici ce que dit le Seigneur Dieu. Dis: Le glaive, le glaive a été aiguisé et poli.
10 wasasshe don kisa, gogagge har yana walwal kamar walƙiya! “‘Kada ku yi farin ciki, hukunci yana zuwa, domin kowa ya ƙi jin abin da na yi gargaɗi a kai.
C’est afin de tuer des victimes qu’il a été aiguisé; c’est afin de briller qu’il a été poli; toi qui abats le sceptre de mon fils, tu as coupé tout arbre par le pied.
11 “‘An ba da wannan takobi don a goge, don a kama da hannu; an washe shi aka kuma goge, shiryayye don a yi kisa da shi.
Et je l’ai donné à polir pour qu’il soit tenu à la main; il a été aiguisé, ce glaive, et il a été poli, afin qu’il soit dans la main de celui qui tue.
12 Ka yi kuka ka yi makoki, ɗan mutum, gama yana gāba da dukan sarakunan Isra’ila. An jefa su ga takobi tare da jama’ata. Saboda haka ku buga ƙirjinku.
Crie et hurle, fils d’un homme, parce qu’il a été fait pour tuer mon peuple, pour tuer tous les chefs d’Israël qui avaient pris la fuite: ils ont été livrés au glaive avec mon peuple; c’est pourquoi frappe sur ta cuisse,
13 “‘Gwaji tabbatacce zai zo. Kuma a ce sandan Yahuda, wanda takobi ya ƙi, ya ci gaba? In ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
Parce qu’il a été éprouvé; et ce sceptre, lorsqu’il l’aura renversé, ne sera plus, dit le Seigneur Dieu.
14 “Saboda haka fa, ɗan mutum ka yi annabci ka kuma tafa hannuwanka. Bari takobi ya yi sara sau biyu, har sau uku ma. Takobin kisa ne, takobi ne don kisa mai girma, zai kewaye su a kowane gefe.
Toi donc, fils d’un homme, prophétise, frappe des mains, et qu’il soit doublé le glaive, et qu’il soit triplé le glaive des tués; c’est le glaive de la grande tuerie, lequel les frappe de stupeur,
15 Domin zukata su narke da yawa kuma su fāɗi, na tsai da takobin kisa a dukan ƙofofinsu. Kash! A sa ya haska kamar walƙiya, ana riƙe da shi don kisa.
Et fait fondre les cœurs et multiplie les ruines. À toutes leurs portes j’ai jeté l’épouvante du glaive aiguisé et poli pour briller, engaîné pour le carnage.
16 Ya takobi, yi sara zuwa dama ka yi kuma zuwa hagu, duk inda aka juya ka.
Aiguise-toi, va à droite ou à gauche, partout où tu désires porter ta face.
17 Zan tafa hannuwana, fushina kuwa zai sauka. Ni Ubangiji na faɗa.”
Bien plus, moi-même je frapperai des mains et j’assouvirai mon indignation; c’est moi le Seigneur qui ai parlé.
18 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
19 “Ɗan mutum, ka nuna hanyoyi biyu inda takobin sarkin Babilon zai bi, duka biyun su fara daga ƙasa guda. Ka kafa shaida inda hanyar za tă rabu zuwa cikin birni.
Et toi, fils de l’homme, pose-toi deux voies, afin que vienne le glaive du roi de Babylone; toutes deux sortiront d’une seule terre; et c’est de la main qu’il tirera sa conjecture, et à la tête de la voie de la cité qu’il conjecturera.
20 Ka nuna hanya guda wadda takobi zai fāɗo wa Rabba ta Ammonawa ɗayan kuma da zai fāɗo a kan Yahuda da kuma Urushalima mai katanga.
Tu feras une voie, afin que vienne le glaive à Rabbath des fils d’Ammon, et à Juda contre Jérusalem, ville très fortifiée.
21 Gama sarkin Babilon zai tsaya a mararrabar hanya, a inda hanyar ta rabu biyu, don yă yi duba. Zai jefa ƙuri’a da kibiyoyinsa, zai nemi shawarar gumakansa, zai bincike hanta.
Car le roi de Babylone s’est arrêté à la double voie, à la tête des deux chemins, cherchant un augure, mêlant les flèches: il a interrogé les idoles, il a consulté les entrailles,
22 A hannunsa na dama ƙuri’a don Urushalima za tă fito, inda zai kafa dundurusai, ya ba da umarni kisa, a yi kururuwar yaƙi, a kafa dundurusai a kan ƙofofi, a gina mahaurai a kuma yi ƙawanya.
À sa droite le sort est tombé sur Jérusalem, afin qu’il place des béliers, qu’il ouvre sa bouche pour le carnage, qu’il élève la voix avec un hurlement, qu’il place des béliers contre les portes, qu’il forme un rempart et qu’il bâtisse des fortifications.
23 Zai zama kamar duban ƙarya ne ga waɗanda suka yi rantsuwar yin masa biyayya, amma zai tunashe su game da laifinsu ya kuma kama su.
Et il sera à leurs yeux comme consultant vainement un oracle, et imitant le repos des sabbats; mais lui-même se souviendra de leur iniquité, pour prendre Jérusalem.
24 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku mutanen nan kun tuna da laifinku ta wurin tawaye, kun kuma bayyana zunubanku cikin dukan abin da kuke yi, domin kun yi haka, za a kama ku.
C’est pourquoi voici ce que dit le Seigneur Dieu: Parce que vous vous êtes souvenus de votre iniquité, et que vous avez révélé vos prévarications, et que vos péchés ont paru dans toutes vos pensées; parce que, dis-je, vous vous en êtes souvenus, vous serez saisis par sa main.
25 “‘Ya kai ƙazantaccen mugu, yerima Isra’ila, wanda kwanansa ta zo, wanda lokacin hukuncinsa ya cika fal,
Mais toi, profane, chef impie d’Israël, dont le jour marqué d’avance est venu dans le temps de la punition de ton iniquité;
26 ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka kunce rawanin, ka ɗauke rawanin nan. Ba zai zama kamar yadda yake ba. Za a ɗaukaka ƙasƙantacce, amma a ƙasƙantar da mai girma.
Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Ôte la tiare, enlève la couronne; n’est-ce pas cette couronne qui a élevé l’homme et humilié le grand?
27 Hallaka! Hallaka! Zan hallaka shi! Ba za a maido da shi ba sai ya ga ainihin mai shi; gare shi zan bayar da shi.’
Je la montrerai iniquité, iniquité, iniquité [mais cela n’arriva pas jusqu’à ce que vînt celui à qui appartient le jugement], et je la lui livrerai.
28 “Kai kuma, ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da Ammonawa da kuma zarginsu. “‘Takobi, takobi, an ja don kisa, an goge don cinyewa yana haske kamar walƙiya!
Et toi, fils d’un homme, prophétise et dis: Voici ce que dit le Seigneur Dieu aux fils d’Ammon, et pour leur opprobre: Glaive, glaive, sors du fourreau pour tuer, polis-toi, afin que tu lues et que tu brilles,
29 Duk da wahayin ƙarya game da kai, duban ƙarya game da kai, za a sa shi a wuyan mugaye waɗanda za a kashe, waɗanda kwanansu ta zo, waɗanda lokacin hukuncinsu ya cika fal.
Lorsqu’on voit pour toi des choses vaines, et qu’on prédit des mensonges, afin que tu tombes sur le cou des impies blessés à mort, dont le jour marqué d’avance est venu dans le temps de la punition de leur iniquité.
30 “‘Ka mai da takobi a kubensa. A inda aka halicce ka, a ƙasar kakanninka, zan hukunta ka.
Rentre dans ton fourreau, dans le lieu où tu as été créé, dans la terre de ta naissance je te jugerai;
31 Zan zub da hasalata a kanka in hura maka wutar fushina; Zan ba da kai a hannun mugayen mutanen da suka gwanince a hallakarwa.
Et je verserai sur toi mon indignation: dans le feu de ma fureur je soufflerai sur toi, et je t’abandonnerai aux mains d’hommes insensés, et qui ont machiné ta perte.
32 Za ka zama itacen wuta, za a zub da jininka a ƙasarka, ba za a ƙara tuna da kai ba; gama Ni Ubangiji na faɗa.’”
Du feu tu seras la pâture, ton sang sera répandu au milieu de la terre, tu seras livré à l’oubli, parce que c’est moi le Seigneur qui ai parlé.

< Ezekiyel 21 >