< Ezekiyel 21 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
2 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka gāba da Urushalima ka kuma yi wa’azi a kan wuri mai tsarki. Ka yi annabci gāba da ƙasar Isra’ila
Fils d'homme, tourne ta face vers Jérusalem, et fais découler [ta parole] vers les saints lieux, et prophétise contre la terre d'Israël.
3 ka faɗa mata, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina gāba da ke. Zan ja takobina daga kubensa in karkashe adalai da mugaye daga cikinki.
Et dis à la terre d'Israël: ainsi a dit l'Eternel: voici, j'en [veux] à toi, et je tirerai mon épée de son fourreau, et je retrancherai du milieu de toi le juste et le méchant.
4 Domin zan karkashe adalai da kuma mugaye, ba zan rufe takobina a kan kowa daga kudu zuwa arewa ba.
Parce que je retrancherai du milieu de toi le juste et le méchant, à cause de cela mon épée sortira de son fourreau contre toute chair, depuis le Midi jusqu'au Septentrion.
5 Sa’an nan duka mutane za su san cewa Ni Ubangiji na ja takobina daga kubensa; ba zai sāke koma kuma ba.’
Et toute chair saura que moi l'Eternel j'aurai tiré mon épée de son fourreau, [et] elle n'y retournera plus.
6 “Saboda ka yi nishi, ɗan mutum! Yi nishi a gabansu da ajiyar zuciya da ɓacin rai.
Aussi toi, fils d'homme gémis en te rompant les reins de douleur, et soupire avec amertume en leur présence.
7 Kuma sa’ad da suka tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Domin labarun da suke fitowa. Kowace zuciya za tă narke kowane hannu kuma ya gurgunta; kowane ruhu zai sume kowane gwiwa kuma ta rasa ƙarfi kamar ruwa.’ Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Et quand ils te diront: pourquoi gémis-tu? alors tu répondras: c'est à cause du bruit, car il vient, et tout cœur se fondra, et toutes les mains deviendront lâches, et tout esprit sera étourdi, et tous les genoux se fondront en eau; voici, il vient, et il sera accompli, dit le Seigneur l'Eternel.
8 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Puis la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
9 “Ɗan mutum, yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Takobi, takobi, wasasshe da kuma gogagge,
Fils d'homme, prophétise, et dis: ainsi a dit l'Eternel: dis, l'épée, l'épée a été aiguisée, et elle est aussi fourbie.
10 wasasshe don kisa, gogagge har yana walwal kamar walƙiya! “‘Kada ku yi farin ciki, hukunci yana zuwa, domin kowa ya ƙi jin abin da na yi gargaɗi a kai.
Elle a été aiguisée pour faire un grand carnage, elle a été fourbie afin qu'elle brille: nous réjouirons-nous? C'[est] la verge de mon fils; elle dédaigne tout bois.
11 “‘An ba da wannan takobi don a goge, don a kama da hannu; an washe shi aka kuma goge, shiryayye don a yi kisa da shi.
Et [l'Eternel] l'a donnée à fourbir, afin qu'on la tienne à la main; l'épée a été aiguisée, et elle a été fourbie pour la mettre en la main du destructeur.
12 Ka yi kuka ka yi makoki, ɗan mutum, gama yana gāba da dukan sarakunan Isra’ila. An jefa su ga takobi tare da jama’ata. Saboda haka ku buga ƙirjinku.
Crie et hurle, fils d'homme, car elle est contre mon peuple, elle est contre tous les principaux d'Israël; les frayeurs de l'épée seront sur mon peuple; c'est pourquoi frappe sur ta cuisse.
13 “‘Gwaji tabbatacce zai zo. Kuma a ce sandan Yahuda, wanda takobi ya ƙi, ya ci gaba? In ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
Quand ce serait une épreuve, et que serait-ce? Si même [cette épée] qui dédaigne [tout bois, était] une verge, il n'en serait rien, dit le Seigneur l'Eternel.
14 “Saboda haka fa, ɗan mutum ka yi annabci ka kuma tafa hannuwanka. Bari takobi ya yi sara sau biyu, har sau uku ma. Takobin kisa ne, takobi ne don kisa mai girma, zai kewaye su a kowane gefe.
Toi donc, fils d'homme, prophétise, et frappe d'une main contre l'autre, et que l'épée soit redoublée pour la troisième fois, l'épée des tués est l'épée contre les grands qui seront tués, passant jusqu'à eux dans leurs cabinets.
15 Domin zukata su narke da yawa kuma su fāɗi, na tsai da takobin kisa a dukan ƙofofinsu. Kash! A sa ya haska kamar walƙiya, ana riƙe da shi don kisa.
J'ai mis à toutes leurs portes l'épée luisante, afin que le cœur se fonde, et que les ruines soient multipliées. Ah! elle est faite pour briller et réservée pour tuer.
16 Ya takobi, yi sara zuwa dama ka yi kuma zuwa hagu, duk inda aka juya ka.
Joins-toi épée, frappe à la droite; avance-toi, frappe à la gauche, à quelque côté que tu te rencontres.
17 Zan tafa hannuwana, fushina kuwa zai sauka. Ni Ubangiji na faɗa.”
Je frapperai aussi d'une main contre l'autre, et je satisferai ma colère: moi l'Eternel j'ai parlé.
18 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
19 “Ɗan mutum, ka nuna hanyoyi biyu inda takobin sarkin Babilon zai bi, duka biyun su fara daga ƙasa guda. Ka kafa shaida inda hanyar za tă rabu zuwa cikin birni.
Et toi, fils d'homme, propose-toi deux chemins par où l'épée du Roi de Babylone pourrait venir, [et] que les deux chemins sortent d'un même pays, et les choisis, choisis-les à l'endroit où commence le chemin de la ville de [Babylone].
20 Ka nuna hanya guda wadda takobi zai fāɗo wa Rabba ta Ammonawa ɗayan kuma da zai fāɗo a kan Yahuda da kuma Urushalima mai katanga.
Tu te proposeras le chemin par lequel l'épée doit venir contre Rabba des enfants de Hammon, et [le chemin] qui va en Judée, et à Jérusalem, ville forte.
21 Gama sarkin Babilon zai tsaya a mararrabar hanya, a inda hanyar ta rabu biyu, don yă yi duba. Zai jefa ƙuri’a da kibiyoyinsa, zai nemi shawarar gumakansa, zai bincike hanta.
Car le Roi de Babylone s'est arrêté dans un chemin fourchu, au commencement de deux chemins, pour consulter les devins; il a poli les flèches; il a interrogé les Théraphims; il a regardé au foie.
22 A hannunsa na dama ƙuri’a don Urushalima za tă fito, inda zai kafa dundurusai, ya ba da umarni kisa, a yi kururuwar yaƙi, a kafa dundurusai a kan ƙofofi, a gina mahaurai a kuma yi ƙawanya.
Dans sa main droite est la divination contre Jérusalem, pour y disposer les béliers, pour publier la tuerie, pour crier l'alarme à haute voix, pour ranger les béliers contre les portes, pour dresser des terrasses, [et] bâtir des forts.
23 Zai zama kamar duban ƙarya ne ga waɗanda suka yi rantsuwar yin masa biyayya, amma zai tunashe su game da laifinsu ya kuma kama su.
Mais ce leur sera comme qui devinerait faussement en leur présence; il y a de grands serments entre eux, mais il va rappeler le souvenir de leur iniquité, afin qu'on y soit surpris.
24 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku mutanen nan kun tuna da laifinku ta wurin tawaye, kun kuma bayyana zunubanku cikin dukan abin da kuke yi, domin kun yi haka, za a kama ku.
C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: parce que vous avez fait revenir le souvenir de votre iniquité, lorsque vos crimes se sont découverts, tellement que vos péchés se voient dans toutes vos actions; parce, [dis-je], que vous avez fait qu'on se souvienne de vous, vous serez surpris avec la main.
25 “‘Ya kai ƙazantaccen mugu, yerima Isra’ila, wanda kwanansa ta zo, wanda lokacin hukuncinsa ya cika fal,
Et toi profane, méchant, Prince d'Israël, le jour duquel est venu au temps de l'iniquité, ce qui fera sa fin.
26 ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka kunce rawanin, ka ɗauke rawanin nan. Ba zai zama kamar yadda yake ba. Za a ɗaukaka ƙasƙantacce, amma a ƙasƙantar da mai girma.
Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel, qu'on ôte cette tiare, et qu'on enlève cette couronne: ce ne sera plus celle-ci; j'élèverai ce qui est bas, et j'abaisserai ce qui est haut.
27 Hallaka! Hallaka! Zan hallaka shi! Ba za a maido da shi ba sai ya ga ainihin mai shi; gare shi zan bayar da shi.’
Je la mettrai à la renverse, à la renverse, à la renverse, et elle ne sera plus, jusqu'à ce que vienne celui auquel appartient le gouvernement, et je le lui donnerai.
28 “Kai kuma, ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da Ammonawa da kuma zarginsu. “‘Takobi, takobi, an ja don kisa, an goge don cinyewa yana haske kamar walƙiya!
Et toi, fils d'homme, prophétise, et dis: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel touchant les enfants de Hammon, et touchant leur opprobre; dis donc, épée, épée dégainée, fourbie pour faire la tuerie, pour consumer avec son éclat.
29 Duk da wahayin ƙarya game da kai, duban ƙarya game da kai, za a sa shi a wuyan mugaye waɗanda za a kashe, waɗanda kwanansu ta zo, waɗanda lokacin hukuncinsu ya cika fal.
Pendant qu'on voit pour toi des visions de vanité, et qu'on devine pour toi le mensonge, afin qu'on te mette sur le cou des méchants qui sont mis à mort; le jour desquels est venu au temps de l'iniquité, ce qui sera sa fin.
30 “‘Ka mai da takobi a kubensa. A inda aka halicce ka, a ƙasar kakanninka, zan hukunta ka.
La remettrait-on dans son fourreau? je te jugerai sur le lieu auquel tu as été créé, au pays de ton extraction.
31 Zan zub da hasalata a kanka in hura maka wutar fushina; Zan ba da kai a hannun mugayen mutanen da suka gwanince a hallakarwa.
Je répandrai mon indignation sur toi, j'allumerai sur toi le feu de ma fureur, et je te livrerai entre les mains d'hommes brutaux, et forgeurs de destruction.
32 Za ka zama itacen wuta, za a zub da jininka a ƙasarka, ba za a ƙara tuna da kai ba; gama Ni Ubangiji na faɗa.’”
Tu seras destiné au feu pour être dévoré; ton sang sera au milieu de la terre: on ne se souviendra plus de toi, car c'est moi l'Eternel, qui ai parlé.