< Ezekiyel 21 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord was maad to me,
2 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka gāba da Urushalima ka kuma yi wa’azi a kan wuri mai tsarki. Ka yi annabci gāba da ƙasar Isra’ila
and he seide, Thou, sone of man, sette thi face to Jerusalem, and droppe thou to the seyntuaries, and profesie thou ayens the erthe of Israel.
3 ka faɗa mata, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina gāba da ke. Zan ja takobina daga kubensa in karkashe adalai da mugaye daga cikinki.
And thou schalt seie to the lond of Israel, The Lord God seith these thingis, Lo! Y to thee, and Y schal caste my swerd out of his schethe, and Y schal sle in thee a iust man and a wickid man.
4 Domin zan karkashe adalai da kuma mugaye, ba zan rufe takobina a kan kowa daga kudu zuwa arewa ba.
Forsothe for that that Y haue slayn in thee a iust man and a wickid man, therfor my swerd schal go out of his schethe to ech man, fro the south til to the north;
5 Sa’an nan duka mutane za su san cewa Ni Ubangiji na ja takobina daga kubensa; ba zai sāke koma kuma ba.’
that ech man wite, that Y the Lord haue drawe out my swerd fro his schethe, that schal not be clepid ayen.
6 “Saboda ka yi nishi, ɗan mutum! Yi nishi a gabansu da ajiyar zuciya da ɓacin rai.
And thou, sone of man, weile in sorewe of leendis, and in bitternessis thou schalt weile bifore hem.
7 Kuma sa’ad da suka tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Domin labarun da suke fitowa. Kowace zuciya za tă narke kowane hannu kuma ya gurgunta; kowane ruhu zai sume kowane gwiwa kuma ta rasa ƙarfi kamar ruwa.’ Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
And whanne thei schulen seie to thee, Whi weilist thou? thou schalt seie, For hering, for it cometh; and ech herte shal faile, and alle hondis schulen be aclumsid, and ech spirit schal be sike, and watris schulen flete doun bi alle knees; lo! it cometh, and it shal be don, seith the Lord God.
8 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord was maad to me,
9 “Ɗan mutum, yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Takobi, takobi, wasasshe da kuma gogagge,
and he seide, Sone of man, profesie thou; and thou schalt seie, The Lord God seith these thingis, Speke thou, The swerd, the swerd is maad scharp, and is maad briyt;
10 wasasshe don kisa, gogagge har yana walwal kamar walƙiya! “‘Kada ku yi farin ciki, hukunci yana zuwa, domin kowa ya ƙi jin abin da na yi gargaɗi a kai.
it is maad scharp to sle sacrifices; it is maad briyt, that it schyne. Thou that mouest the ceptre of my sone, hast kit doun ech tree.
11 “‘An ba da wannan takobi don a goge, don a kama da hannu; an washe shi aka kuma goge, shiryayye don a yi kisa da shi.
And Y yaf it to be forbischid, that it be holdun with hond; this swerd is maad scharp, and this is maad briyt, that it be in the hond of the sleere.
12 Ka yi kuka ka yi makoki, ɗan mutum, gama yana gāba da dukan sarakunan Isra’ila. An jefa su ga takobi tare da jama’ata. Saboda haka ku buga ƙirjinku.
Sone of man, crie thou, and yelle, for this swerd is maad in my puple, this in alle the duykis of Israel; thei that fledden ben youun to swerd with my puple. Therfor smite thou on thin hipe, for it is preuyd;
13 “‘Gwaji tabbatacce zai zo. Kuma a ce sandan Yahuda, wanda takobi ya ƙi, ya ci gaba? In ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
and this whanne it hath distried the ceptre, and it schal not be, seith the Lord God.
14 “Saboda haka fa, ɗan mutum ka yi annabci ka kuma tafa hannuwanka. Bari takobi ya yi sara sau biyu, har sau uku ma. Takobin kisa ne, takobi ne don kisa mai girma, zai kewaye su a kowane gefe.
Therfor, sone of man, profesie thou, and smyte thou hond to hond, and the swerd be doublid, and the swerd of sleeris be treblid; this is the swerd of greet sleyng, that schal make hem astonyed,
15 Domin zukata su narke da yawa kuma su fāɗi, na tsai da takobin kisa a dukan ƙofofinsu. Kash! A sa ya haska kamar walƙiya, ana riƙe da shi don kisa.
and to faile in herte, and multiplieth fallingis. In alle the yatis of hem Y yaf disturbling of a swerd, scharp and maad briyt to schyne, gird to sleynge.
16 Ya takobi, yi sara zuwa dama ka yi kuma zuwa hagu, duk inda aka juya ka.
Be thou maad scharp, go thou to the riyt side, ether to the left side, whidur euer the desir of thi face is.
17 Zan tafa hannuwana, fushina kuwa zai sauka. Ni Ubangiji na faɗa.”
Certis and Y schal smyte with hond to hond, and Y schal fille myn indignacioun; Y the Lord spak.
18 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord was maad to me,
19 “Ɗan mutum, ka nuna hanyoyi biyu inda takobin sarkin Babilon zai bi, duka biyun su fara daga ƙasa guda. Ka kafa shaida inda hanyar za tă rabu zuwa cikin birni.
and he seide, And thou, sone of man, sette to thee twei weies, that the swerd of the king of Babiloyne come; bothe schulen go out of o lond, and bi the hond he schal take coniecting; he schal coniecte in the heed of the weie of the citee,
20 Ka nuna hanya guda wadda takobi zai fāɗo wa Rabba ta Ammonawa ɗayan kuma da zai fāɗo a kan Yahuda da kuma Urushalima mai katanga.
settinge a weye, that the swerd come to Rabath of the sones of Amon, and to Juda in to Jerusalem moost strong.
21 Gama sarkin Babilon zai tsaya a mararrabar hanya, a inda hanyar ta rabu biyu, don yă yi duba. Zai jefa ƙuri’a da kibiyoyinsa, zai nemi shawarar gumakansa, zai bincike hanta.
For the king of Babiloyne stood in the meeting of twey weies, in the heed of twei weies, and souyte dyuynyng, and medlide arowis; he axide idols, and took councel at entrails.
22 A hannunsa na dama ƙuri’a don Urushalima za tă fito, inda zai kafa dundurusai, ya ba da umarni kisa, a yi kururuwar yaƙi, a kafa dundurusai a kan ƙofofi, a gina mahaurai a kuma yi ƙawanya.
Dyuynyng was maad to his riyt side on Jerusalem, that he sette engyns, that he opene mouth in sleyng, that he reise vois in yelling, that he sette engyns ayens the yatis, that he bere togidere erthe, that he bilde strengthinges.
23 Zai zama kamar duban ƙarya ne ga waɗanda suka yi rantsuwar yin masa biyayya, amma zai tunashe su game da laifinsu ya kuma kama su.
And he shal be as counceling in veyn goddis answer bifor the iyen of hem, and seruynge the reste of sabatis; but he schal haue mynde on wickidnesse, to take.
24 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku mutanen nan kun tuna da laifinku ta wurin tawaye, kun kuma bayyana zunubanku cikin dukan abin da kuke yi, domin kun yi haka, za a kama ku.
Therfor the Lord God seith these thingis, For that that ye hadden mynde on youre wickidnesse, and schewiden youre trespassyngis, and youre synnes apperiden in alle youre thouytis, forsothe for that that ye hadden mynde, ye schulen be takun bi hond.
25 “‘Ya kai ƙazantaccen mugu, yerima Isra’ila, wanda kwanansa ta zo, wanda lokacin hukuncinsa ya cika fal,
But thou, cursid wickid duyk of Israel, whos dai bifor determyned is comun in the tyme of wickidnesse,
26 ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka kunce rawanin, ka ɗauke rawanin nan. Ba zai zama kamar yadda yake ba. Za a ɗaukaka ƙasƙantacce, amma a ƙasƙantar da mai girma.
the Lord God seith these thingis, Do awei the mitre, take awei the coroun; whether it is not this that reiside the meke man, and made low the hiy man?
27 Hallaka! Hallaka! Zan hallaka shi! Ba za a maido da shi ba sai ya ga ainihin mai shi; gare shi zan bayar da shi.’
Wickidnesse, wickidnesse, wickidnesse Y schal putte it; and this schal not be doon til he come, whos the doom is, and Y schal bitake to hym.
28 “Kai kuma, ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da Ammonawa da kuma zarginsu. “‘Takobi, takobi, an ja don kisa, an goge don cinyewa yana haske kamar walƙiya!
And thou, sone of man, profesie, and seie, The Lord God seith these thingis to the sones of Amon, and to the schenschipe of hem; and thou schalt seie, A! thou swerd, A! thou swerd, drawun out to sle, maad briyte, that thou sle and schyne,
29 Duk da wahayin ƙarya game da kai, duban ƙarya game da kai, za a sa shi a wuyan mugaye waɗanda za a kashe, waɗanda kwanansu ta zo, waɗanda lokacin hukuncinsu ya cika fal.
whanne veyn thingis weren seien to thee, and leesingis weren dyuynyd, that thou schuldist be youun on the neckis of wickid men woundid, the dai of whiche bifore determyned schal come in the tyme of wickidnesse, turne thou ayen in to thi schethe,
30 “‘Ka mai da takobi a kubensa. A inda aka halicce ka, a ƙasar kakanninka, zan hukunta ka.
in to the place in which thou were maad. Y schal deme thee in the lond of thi birthe,
31 Zan zub da hasalata a kanka in hura maka wutar fushina; Zan ba da kai a hannun mugayen mutanen da suka gwanince a hallakarwa.
and Y schal schede out myn indignacioun on thee; in the fier of my strong veniaunce Y schal blowe in thee, and Y schal yyue thee in to the hondis of vnwise men, and makinge deth.
32 Za ka zama itacen wuta, za a zub da jininka a ƙasarka, ba za a ƙara tuna da kai ba; gama Ni Ubangiji na faɗa.’”
Thou schalt be mete to fier, thi blood schal be in the middis of erthe; thou schalt be youun to foryetyng, for Y the Lord spak.

< Ezekiyel 21 >