< Ezekiyel 21 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then came the word of Jehovah to me, saying:
2 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka gāba da Urushalima ka kuma yi wa’azi a kan wuri mai tsarki. Ka yi annabci gāba da ƙasar Isra’ila
Son of man, set thy face toward Jerusalem, and drop thy word toward the holy places, and prophesy against the land of Israel,
3 ka faɗa mata, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina gāba da ke. Zan ja takobina daga kubensa in karkashe adalai da mugaye daga cikinki.
and say to the land of Israel, Thus saith Jehovah: Behold, I am against thee, and I will draw forth my sword out of its sheath, and will cut off from thee the righteous and the wicked.
4 Domin zan karkashe adalai da kuma mugaye, ba zan rufe takobina a kan kowa daga kudu zuwa arewa ba.
Seeing then that I cut off from thee the righteous and the wicked, therefore shall my sword go forth out of its sheath against all flesh from the south to the north.
5 Sa’an nan duka mutane za su san cewa Ni Ubangiji na ja takobina daga kubensa; ba zai sāke koma kuma ba.’
And all flesh shall know that I, Jehovah, have drawn forth my sword out of its sheath; it shall not return any more.
6 “Saboda ka yi nishi, ɗan mutum! Yi nishi a gabansu da ajiyar zuciya da ɓacin rai.
Thou, therefore, O son of man, sigh! With the breaking of thy loins, and with bitterness, sigh before their eyes!
7 Kuma sa’ad da suka tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Domin labarun da suke fitowa. Kowace zuciya za tă narke kowane hannu kuma ya gurgunta; kowane ruhu zai sume kowane gwiwa kuma ta rasa ƙarfi kamar ruwa.’ Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
And when they shall say to thee, “Wherefore sighest thou?” thou shalt say, “For the rumor, because it cometh; and every heart shall melt, and all hands shall be feeble, and every spirit shall fail, and all knees shall flow with water. Behold it cometh, it shall be brought to pass, saith the Lord Jehovah.”
8 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Also the word of Jehovah came to me, saying:
9 “Ɗan mutum, yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Takobi, takobi, wasasshe da kuma gogagge,
Son of man, prophesy, and say, Thus saith Jehovah: Say, The sword, the sword is sharpened and furbished.
10 wasasshe don kisa, gogagge har yana walwal kamar walƙiya! “‘Kada ku yi farin ciki, hukunci yana zuwa, domin kowa ya ƙi jin abin da na yi gargaɗi a kai.
It is sharpened, that it may make sore slaughter; it is furbished that it may glitter. Or shall we make mirth? The staff of my son despiseth every rod.
11 “‘An ba da wannan takobi don a goge, don a kama da hannu; an washe shi aka kuma goge, shiryayye don a yi kisa da shi.
And he gave it to be furbished that it might be handled. The sword is sharpened and furbished, to be given into the hand of the slayer.
12 Ka yi kuka ka yi makoki, ɗan mutum, gama yana gāba da dukan sarakunan Isra’ila. An jefa su ga takobi tare da jama’ata. Saboda haka ku buga ƙirjinku.
Cry and howl, son of man! for it cometh upon my people, upon all the princes of Israel. They are given up to the sword with my people. Therefore smite upon thy thigh.
13 “‘Gwaji tabbatacce zai zo. Kuma a ce sandan Yahuda, wanda takobi ya ƙi, ya ci gaba? In ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
The trial is made. And what if even the contemning staff should be no more? saith the Lord Jehovah.
14 “Saboda haka fa, ɗan mutum ka yi annabci ka kuma tafa hannuwanka. Bari takobi ya yi sara sau biyu, har sau uku ma. Takobin kisa ne, takobi ne don kisa mai girma, zai kewaye su a kowane gefe.
Thou, therefore, son of man, prophesy, and smite thine hands together! for twice, yea thrice, cometh the sword, a sword of slaughter, a sword of great slaughter, that besetteth them on every side.
15 Domin zukata su narke da yawa kuma su fāɗi, na tsai da takobin kisa a dukan ƙofofinsu. Kash! A sa ya haska kamar walƙiya, ana riƙe da shi don kisa.
That their hearts may faint, and their overthrown may be multiplied, I have set the terror of the sword against all their gates. Ah, how is it made to glitter, polished for slaughter!
16 Ya takobi, yi sara zuwa dama ka yi kuma zuwa hagu, duk inda aka juya ka.
Unite thyself, smite to the right, prepare thyself, smite to the left, whithersoever thine edge is turned!
17 Zan tafa hannuwana, fushina kuwa zai sauka. Ni Ubangiji na faɗa.”
I also will smite my hands together, and cause mine anger to cease. I, Jehovah, have spoken it.
18 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
The word of Jehovah came to me again, saying:
19 “Ɗan mutum, ka nuna hanyoyi biyu inda takobin sarkin Babilon zai bi, duka biyun su fara daga ƙasa guda. Ka kafa shaida inda hanyar za tă rabu zuwa cikin birni.
Do thou, son of man, appoint thee two ways by which the sword of the king of Babylon may come; from one land shall both of them come; and choose thou a place, choose it at the head of the way to the city.
20 Ka nuna hanya guda wadda takobi zai fāɗo wa Rabba ta Ammonawa ɗayan kuma da zai fāɗo a kan Yahuda da kuma Urushalima mai katanga.
Appoint a way, that the sword may come towards Rabbath of the sons of Ammon, and towards Judah, to Jerusalem, the fenced city.
21 Gama sarkin Babilon zai tsaya a mararrabar hanya, a inda hanyar ta rabu biyu, don yă yi duba. Zai jefa ƙuri’a da kibiyoyinsa, zai nemi shawarar gumakansa, zai bincike hanta.
For the king of Babylon shall stand at the parting of the way, at the head of the two ways, to use divination; he shall shake together his arrows, he shall consult the teraphim, he shall look at the liver.
22 A hannunsa na dama ƙuri’a don Urushalima za tă fito, inda zai kafa dundurusai, ya ba da umarni kisa, a yi kururuwar yaƙi, a kafa dundurusai a kan ƙofofi, a gina mahaurai a kuma yi ƙawanya.
In his right hand shall be the lot: Jerusalem, to set battering-rams, to open the mouth with the war-cry, to lift up the voice in shouting, to set battering-rams against the gates, to cast up a mound, to build a tower.
23 Zai zama kamar duban ƙarya ne ga waɗanda suka yi rantsuwar yin masa biyayya, amma zai tunashe su game da laifinsu ya kuma kama su.
And this shall appear a false divination in their sight, because they swore oaths to them. But he shall call to remembrance their iniquity, that they may be taken.
24 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku mutanen nan kun tuna da laifinku ta wurin tawaye, kun kuma bayyana zunubanku cikin dukan abin da kuke yi, domin kun yi haka, za a kama ku.
Therefore thus saith the Lord Jehovah: Because ye make your iniquity to be remembered, in that your transgressions are discovered, so that in all your doings your sins do appear, —because, I say, ye bring yourselves into remembrance, ye shall be taken with that hand.
25 “‘Ya kai ƙazantaccen mugu, yerima Isra’ila, wanda kwanansa ta zo, wanda lokacin hukuncinsa ya cika fal,
And thou, profane, wicked prince of Israel, whose day cometh in the time when iniquity bringeth destruction!
26 ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka kunce rawanin, ka ɗauke rawanin nan. Ba zai zama kamar yadda yake ba. Za a ɗaukaka ƙasƙantacce, amma a ƙasƙantar da mai girma.
Thus saith the Lord Jehovah: I will remove the diadem, and take away the crown! This shall no more be this. I exalt him that is low, and abase him that is high.
27 Hallaka! Hallaka! Zan hallaka shi! Ba za a maido da shi ba sai ya ga ainihin mai shi; gare shi zan bayar da shi.’
I will destroy, destroy, destroy it; and it shall be no more until he come to whom the right belongeth, and to whom I will give it.
28 “Kai kuma, ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da Ammonawa da kuma zarginsu. “‘Takobi, takobi, an ja don kisa, an goge don cinyewa yana haske kamar walƙiya!
And thou, son of man, prophesy, and say: Thus saith the Lord Jehovah concerning the sons of Ammon and their scorn; even say thou, The sword, the sword is drawn; to slay, to consume, is it furbished, so that it glittereth;
29 Duk da wahayin ƙarya game da kai, duban ƙarya game da kai, za a sa shi a wuyan mugaye waɗanda za a kashe, waɗanda kwanansu ta zo, waɗanda lokacin hukuncinsu ya cika fal.
while they see deceit for thee, and prophesy falsehood, that it may bring thee to the necks of the wicked that are slain, whose day cometh in the time when iniquity bringeth destruction.
30 “‘Ka mai da takobi a kubensa. A inda aka halicce ka, a ƙasar kakanninka, zan hukunta ka.
Return the sword into its sheath! In the place where thou wast created, in the land of thy nativity, I will judge thee,
31 Zan zub da hasalata a kanka in hura maka wutar fushina; Zan ba da kai a hannun mugayen mutanen da suka gwanince a hallakarwa.
and I will pour upon thee my indignation, I will blow upon thee in the fire of my wrath, and deliver thee into the hands of brutal men, skilful to destroy.
32 Za ka zama itacen wuta, za a zub da jininka a ƙasarka, ba za a ƙara tuna da kai ba; gama Ni Ubangiji na faɗa.’”
Thou shalt be fuel for the fire; thy blood shall be in the midst of the land; men shall no more remember thee. I, Jehovah, have spoken it.