< Ezekiyel 21 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying:
2 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka gāba da Urushalima ka kuma yi wa’azi a kan wuri mai tsarki. Ka yi annabci gāba da ƙasar Isra’ila
“Son of man, set your face toward Jerusalem, and pour in drops toward the sanctuaries, and prophesy against the soil of Israel.
3 ka faɗa mata, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina gāba da ke. Zan ja takobina daga kubensa in karkashe adalai da mugaye daga cikinki.
And you shall say to the land of Israel: Thus says the Lord God: Behold, I am against you, and I will cast my sword from its sheath, and I will slay the just and the impious among you.
4 Domin zan karkashe adalai da kuma mugaye, ba zan rufe takobina a kan kowa daga kudu zuwa arewa ba.
But in as much as I have slain among you the just and the impious, for this reason my sword will go forth from its sheath against all flesh, from the south even to the north.
5 Sa’an nan duka mutane za su san cewa Ni Ubangiji na ja takobina daga kubensa; ba zai sāke koma kuma ba.’
So may all flesh know that I, the Lord, have led my sword out of its sheath irrevocably.
6 “Saboda ka yi nishi, ɗan mutum! Yi nishi a gabansu da ajiyar zuciya da ɓacin rai.
And as for you, son of man, groan in the breaking of your back, and groan in bitterness before them.
7 Kuma sa’ad da suka tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Domin labarun da suke fitowa. Kowace zuciya za tă narke kowane hannu kuma ya gurgunta; kowane ruhu zai sume kowane gwiwa kuma ta rasa ƙarfi kamar ruwa.’ Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
And when they will say to you, ‘Why are you groaning?’ you shall say: ‘On behalf of the report, for it is approaching. And every heart will waste away, and every hand will be broken, and every spirit will be weakened, and water will flow across every knee.’ Behold, it is approaching and it will happen, says the Lord God.”
8 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying:
9 “Ɗan mutum, yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Takobi, takobi, wasasshe da kuma gogagge,
“Son of man, prophesy, and you shall say: Thus says the Lord God: Speak: The sword! The sword has been sharpened and polished!
10 wasasshe don kisa, gogagge har yana walwal kamar walƙiya! “‘Kada ku yi farin ciki, hukunci yana zuwa, domin kowa ya ƙi jin abin da na yi gargaɗi a kai.
It has been sharpened, so that it may cut down victims! It has been polished, so that it may shine! You are disturbing the scepter of my son. You have cut down every tree.
11 “‘An ba da wannan takobi don a goge, don a kama da hannu; an washe shi aka kuma goge, shiryayye don a yi kisa da shi.
And I have sent it to be made smooth, so that it may be handled. This sword has been sharpened, and it has been polished, so that it may be in the hand of the one who kills.
12 Ka yi kuka ka yi makoki, ɗan mutum, gama yana gāba da dukan sarakunan Isra’ila. An jefa su ga takobi tare da jama’ata. Saboda haka ku buga ƙirjinku.
Cry out and wail, O son of man! For this has been done among my people, this is among all the leaders of Israel, who have fled. They have been handed over to the sword, with my people. Therefore, slap your thigh,
13 “‘Gwaji tabbatacce zai zo. Kuma a ce sandan Yahuda, wanda takobi ya ƙi, ya ci gaba? In ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
for it has been tested. And this one, when he will have overthrown the scepter, will not be, says the Lord God.
14 “Saboda haka fa, ɗan mutum ka yi annabci ka kuma tafa hannuwanka. Bari takobi ya yi sara sau biyu, har sau uku ma. Takobin kisa ne, takobi ne don kisa mai girma, zai kewaye su a kowane gefe.
You therefore, O son of man, prophesy, and strike hand against hand, and let the sword be doubled, and let the sword of the slain be tripled. This is the sword of the great slaughter, which causes them to be utterly stupefied,
15 Domin zukata su narke da yawa kuma su fāɗi, na tsai da takobin kisa a dukan ƙofofinsu. Kash! A sa ya haska kamar walƙiya, ana riƙe da shi don kisa.
and to waste away in heart, and which multiplies ruin. At all their gates, I have presented the consternation of the sword, which has been sharpened and polished so as to shine, which has been dressed for the slaughter.
16 Ya takobi, yi sara zuwa dama ka yi kuma zuwa hagu, duk inda aka juya ka.
Be sharpened! Go to the right or to the left, whichever way is the desire of your face.
17 Zan tafa hannuwana, fushina kuwa zai sauka. Ni Ubangiji na faɗa.”
And then I will clap hand against hand, and I will fulfill my indignation. I, the Lord, have spoken.”
18 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying:
19 “Ɗan mutum, ka nuna hanyoyi biyu inda takobin sarkin Babilon zai bi, duka biyun su fara daga ƙasa guda. Ka kafa shaida inda hanyar za tă rabu zuwa cikin birni.
“And as for you, son of man, set for yourself two ways, so that the sword of the king of Babylon may approach. Both shall go forth from one land. And with a hand, he will grasp and cast lots; he will cast at the head of the way of the community.
20 Ka nuna hanya guda wadda takobi zai fāɗo wa Rabba ta Ammonawa ɗayan kuma da zai fāɗo a kan Yahuda da kuma Urushalima mai katanga.
You shall appoint a way, so that the sword may approach to Rabbah of the sons of Ammon, or to Judah, into Jerusalem, greatly fortified.
21 Gama sarkin Babilon zai tsaya a mararrabar hanya, a inda hanyar ta rabu biyu, don yă yi duba. Zai jefa ƙuri’a da kibiyoyinsa, zai nemi shawarar gumakansa, zai bincike hanta.
For the king of Babylon stood at the fork, at the head of the two ways, seeking divination, shuffling arrows; he inquired of idols, and he consulted entrails.
22 A hannunsa na dama ƙuri’a don Urushalima za tă fito, inda zai kafa dundurusai, ya ba da umarni kisa, a yi kururuwar yaƙi, a kafa dundurusai a kan ƙofofi, a gina mahaurai a kuma yi ƙawanya.
To his right was set the divination over Jerusalem, to place battering rams so as to open a mouth for the slaughter, to lift up the voice of wailing, to place battering rams opposite the gates, to cast up a rampart, to build fortifications.
23 Zai zama kamar duban ƙarya ne ga waɗanda suka yi rantsuwar yin masa biyayya, amma zai tunashe su game da laifinsu ya kuma kama su.
And he shall be, in their eyes, like someone consulting an oracle in vain, or imitating the leisure of Sabbaths. But he will call to mind iniquities, so that it will be captured.
24 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku mutanen nan kun tuna da laifinku ta wurin tawaye, kun kuma bayyana zunubanku cikin dukan abin da kuke yi, domin kun yi haka, za a kama ku.
Therefore, thus says the Lord God: Because you have been remembered in your iniquities, and you have revealed your betrayals, and your sins have appeared within all your plans, because, I say, you have been remembered, you will be captured by a hand.
25 “‘Ya kai ƙazantaccen mugu, yerima Isra’ila, wanda kwanansa ta zo, wanda lokacin hukuncinsa ya cika fal,
But as for you, O impious leader of Israel, whose day has arrived that was predetermined at the time of iniquity:
26 ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka kunce rawanin, ka ɗauke rawanin nan. Ba zai zama kamar yadda yake ba. Za a ɗaukaka ƙasƙantacce, amma a ƙasƙantar da mai girma.
Thus says the Lord God: Take away the diadem, remove the crown. Is this not what has exalted the lowly one, and brought low the sublime one?
27 Hallaka! Hallaka! Zan hallaka shi! Ba za a maido da shi ba sai ya ga ainihin mai shi; gare shi zan bayar da shi.’
Iniquity, iniquity, iniquity I will make it. And this was not done until the one arrived to whom judgment belongs, and I will hand it over to him.
28 “Kai kuma, ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da Ammonawa da kuma zarginsu. “‘Takobi, takobi, an ja don kisa, an goge don cinyewa yana haske kamar walƙiya!
And as for you, son of man, prophesy, and say: Thus says the Lord God to the sons of Ammon, and to their disgrace, and you shall say: O sword, O sword, unsheathe yourself so as to slay; polish yourself so as to kill and to shine,
29 Duk da wahayin ƙarya game da kai, duban ƙarya game da kai, za a sa shi a wuyan mugaye waɗanda za a kashe, waɗanda kwanansu ta zo, waɗanda lokacin hukuncinsu ya cika fal.
while they look upon you in vain, and they divine lies, so that you may be given over to the necks of the wounded impious, whose day has arrived that was predetermined at the time of iniquity.
30 “‘Ka mai da takobi a kubensa. A inda aka halicce ka, a ƙasar kakanninka, zan hukunta ka.
Be returned to your sheath! I will judge you in the place where you were created, in the land of your nativity.
31 Zan zub da hasalata a kanka in hura maka wutar fushina; Zan ba da kai a hannun mugayen mutanen da suka gwanince a hallakarwa.
And I will pour out upon you my indignation. In the fire of my fury, I will fan you, and I will give you over to the hands of cruel men, who have devised destruction.
32 Za ka zama itacen wuta, za a zub da jininka a ƙasarka, ba za a ƙara tuna da kai ba; gama Ni Ubangiji na faɗa.’”
You will be food for the fire; your blood will be in the midst of the land; you will be delivered to oblivion. For I, the Lord, have spoken.”