< Ezekiyel 21 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka gāba da Urushalima ka kuma yi wa’azi a kan wuri mai tsarki. Ka yi annabci gāba da ƙasar Isra’ila
Son of man, let your face be turned to Jerusalem, let your words be dropped in the direction of her holy place, and be a prophet against the land of Israel;
3 ka faɗa mata, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina gāba da ke. Zan ja takobina daga kubensa in karkashe adalai da mugaye daga cikinki.
And say to the land of Israel, These are the words of the Lord: See, I am against you, and I will take my sword out of its cover, cutting off from you the upright and the evil.
4 Domin zan karkashe adalai da kuma mugaye, ba zan rufe takobina a kan kowa daga kudu zuwa arewa ba.
Because I am going to have the upright and the evil cut off from you, for this cause my sword will go out from its cover against all flesh from the south to the north:
5 Sa’an nan duka mutane za su san cewa Ni Ubangiji na ja takobina daga kubensa; ba zai sāke koma kuma ba.’
And all flesh will see that I the Lord have taken my sword out of its cover: and it will never go back.
6 “Saboda ka yi nishi, ɗan mutum! Yi nishi a gabansu da ajiyar zuciya da ɓacin rai.
Make sounds of grief, son of man; with body bent and a bitter heart make sounds of grief before their eyes.
7 Kuma sa’ad da suka tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Domin labarun da suke fitowa. Kowace zuciya za tă narke kowane hannu kuma ya gurgunta; kowane ruhu zai sume kowane gwiwa kuma ta rasa ƙarfi kamar ruwa.’ Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
And when they say to you, Why are you making sounds of grief? then say, Because of the news, for it is coming: and every heart will become soft, and all hands will be feeble, and every spirit will be burning low, and all knees will be turned to water: see, it is coming and it will be done, says the Lord.
8 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying,
9 “Ɗan mutum, yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Takobi, takobi, wasasshe da kuma gogagge,
Son of man, say as a prophet, These are the words of the Lord: Say, A sword, a sword which has been made sharp and polished:
10 wasasshe don kisa, gogagge har yana walwal kamar walƙiya! “‘Kada ku yi farin ciki, hukunci yana zuwa, domin kowa ya ƙi jin abin da na yi gargaɗi a kai.
It has been made sharp to give death; it is polished so that it may be like a thunder-flame: ...
11 “‘An ba da wannan takobi don a goge, don a kama da hannu; an washe shi aka kuma goge, shiryayye don a yi kisa da shi.
And I have given it to the polisher so that it may be taken in the hand: he has made the sword sharp, he has had it polished, to put it into the hand of him who gives death.
12 Ka yi kuka ka yi makoki, ɗan mutum, gama yana gāba da dukan sarakunan Isra’ila. An jefa su ga takobi tare da jama’ata. Saboda haka ku buga ƙirjinku.
Give loud cries and make sounds of grief, O son of man: for it has come on my people, it has come on all the rulers of Israel: fear of the sword has come on my people: for this cause give signs of grief.
13 “‘Gwaji tabbatacce zai zo. Kuma a ce sandan Yahuda, wanda takobi ya ƙi, ya ci gaba? In ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
14 “Saboda haka fa, ɗan mutum ka yi annabci ka kuma tafa hannuwanka. Bari takobi ya yi sara sau biyu, har sau uku ma. Takobin kisa ne, takobi ne don kisa mai girma, zai kewaye su a kowane gefe.
So then, son of man, be a prophet, and put your hands together with a loud sound, and give two blows with the sword, and even three; it is the sword of those who are wounded, even the sword of the wounded; the great sword which goes round about them.
15 Domin zukata su narke da yawa kuma su fāɗi, na tsai da takobin kisa a dukan ƙofofinsu. Kash! A sa ya haska kamar walƙiya, ana riƙe da shi don kisa.
In order that hearts may become soft, and the number of those who are falling may be increased, I have sent death by the sword against all their doors: you are made like a flame, you are polished for death.
16 Ya takobi, yi sara zuwa dama ka yi kuma zuwa hagu, duk inda aka juya ka.
Be pointed to the right, to the left, wherever your edge is ordered.
17 Zan tafa hannuwana, fushina kuwa zai sauka. Ni Ubangiji na faɗa.”
And I will put my hands together with a loud sound, and I will let my wrath have rest: I the Lord have said it.
18 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me again, saying,
19 “Ɗan mutum, ka nuna hanyoyi biyu inda takobin sarkin Babilon zai bi, duka biyun su fara daga ƙasa guda. Ka kafa shaida inda hanyar za tă rabu zuwa cikin birni.
And you, son of man, have two ways marked out, so that the sword of the king of Babylon may come; let the two of them come out of one land: and let there be a pillar at the top of the road:
20 Ka nuna hanya guda wadda takobi zai fāɗo wa Rabba ta Ammonawa ɗayan kuma da zai fāɗo a kan Yahuda da kuma Urushalima mai katanga.
Put a pillar at the top of the road for the sword to come to Rabbah in the land of the children of Ammon, and to Judah and to Jerusalem in the middle of her.
21 Gama sarkin Babilon zai tsaya a mararrabar hanya, a inda hanyar ta rabu biyu, don yă yi duba. Zai jefa ƙuri’a da kibiyoyinsa, zai nemi shawarar gumakansa, zai bincike hanta.
For the king of Babylon took his place at the parting of the ways, at the top of the two roads, to make use of secret arts: shaking the arrows this way and that, he put questions to the images of his gods, he took note of the inner parts of dead beasts.
22 A hannunsa na dama ƙuri’a don Urushalima za tă fito, inda zai kafa dundurusai, ya ba da umarni kisa, a yi kururuwar yaƙi, a kafa dundurusai a kan ƙofofi, a gina mahaurai a kuma yi ƙawanya.
At his right hand was the fate of Jerusalem, to give orders for destruction, to send up the war-cry, to put engines of war against the doors, lifting up earthworks, building walls.
23 Zai zama kamar duban ƙarya ne ga waɗanda suka yi rantsuwar yin masa biyayya, amma zai tunashe su game da laifinsu ya kuma kama su.
And this answer given by secret arts will seem false to those who have given their oaths and have let them be broken: but he will keep the memory of evil-doing so that they may be taken.
24 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku mutanen nan kun tuna da laifinku ta wurin tawaye, kun kuma bayyana zunubanku cikin dukan abin da kuke yi, domin kun yi haka, za a kama ku.
For this cause the Lord has said: Because you have made your evil-doing come to mind by the uncovering of your wrongdoing, causing your sins to be seen in all your evil-doings; because you have come to mind, you will be taken in them.
25 “‘Ya kai ƙazantaccen mugu, yerima Isra’ila, wanda kwanansa ta zo, wanda lokacin hukuncinsa ya cika fal,
And you, O evil one, wounded to death, O ruler of Israel, whose day has come in the time of the last punishment;
26 ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka kunce rawanin, ka ɗauke rawanin nan. Ba zai zama kamar yadda yake ba. Za a ɗaukaka ƙasƙantacce, amma a ƙasƙantar da mai girma.
This is what the Lord has said: Take away the holy head-dress, take off the crown: this will not be again: let that which is low be lifted up, and that which is high be made low.
27 Hallaka! Hallaka! Zan hallaka shi! Ba za a maido da shi ba sai ya ga ainihin mai shi; gare shi zan bayar da shi.’
I will let it be overturned, overturned, overturned: this will not be again till he comes whose right it is; and I will give it to him.
28 “Kai kuma, ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da Ammonawa da kuma zarginsu. “‘Takobi, takobi, an ja don kisa, an goge don cinyewa yana haske kamar walƙiya!
And you, son of man, say as a prophet, This is what the Lord has said about the children of Ammon and about their shame: Say, A sword, even a sword let loose, polished for death, to make it shining so that it may be like a flame:
29 Duk da wahayin ƙarya game da kai, duban ƙarya game da kai, za a sa shi a wuyan mugaye waɗanda za a kashe, waɗanda kwanansu ta zo, waɗanda lokacin hukuncinsu ya cika fal.
Your vision is to no purpose, your use of secret arts gives a false answer, to put it on the necks of evil-doers who are wounded to death, whose day has come, in the time of the last punishment.
30 “‘Ka mai da takobi a kubensa. A inda aka halicce ka, a ƙasar kakanninka, zan hukunta ka.
Go back into your cover. In the place where you were made, in the land from which you were taken, I will be your judge.
31 Zan zub da hasalata a kanka in hura maka wutar fushina; Zan ba da kai a hannun mugayen mutanen da suka gwanince a hallakarwa.
And I will let loose my burning passion on you, breathing out on you the fire of my wrath: and I will give you up into the hands of men like beasts, trained to destruction.
32 Za ka zama itacen wuta, za a zub da jininka a ƙasarka, ba za a ƙara tuna da kai ba; gama Ni Ubangiji na faɗa.’”
You will be food for the fire; your blood will be drained out in the land; there will be no more memory of you: for I the Lord have said it.