< Ezekiyel 20 >
1 A shekara ta bakwai, a wata na biyar a rana ta goma, waɗansu dattawan Isra’ila suka zo don su nemi nufin Ubangiji, suka kuwa zauna a ƙasa a gabana.
No sétimo ano, no quinto mês, no décimo dia do mês, alguns dos anciãos de Israel vieram perguntar a Iavé, e sentaram-se diante de mim.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
A palavra de Javé veio a mim, dizendo:
3 “Ɗan mutum, ka yi magana da dattawan Isra’ila ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kun zo ne ku nemi shawarata? Muddin ina raye, ba zan bari ku nemi shawarata ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
“Filho do homem, fala aos anciãos de Israel, e diz-lhes: 'O Senhor Javé diz: “É para me inquirir que você veio? Como eu vivo”, diz o Senhor Javé, “não serei perguntado por você”.
4 “Za ka hukunta su? Za ka hukunta su, ɗan mutum? To, sai ka kalubalance su da ayyukan banƙyamar kakanninsu
“Você vai julgá-los, filho do homem? Você vai julgá-los? Fazê-los conhecer as abominações de seus pais.
5 ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na zaɓi Isra’ila, na ɗaga hannuna, na rantse wa zuriyar gidan Yaƙub na kuma bayyana kaina gare su a Masar da hannun da na ɗaga na ce musu, “Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Diz-lhes: 'O Senhor Javé diz: “No dia em que escolhi Israel, e jurei à descendência da casa de Jacó, e me dei a conhecer a eles na terra do Egito, quando lhes jurei, dizendo: 'Eu sou Javé, vosso Deus';
6 A ranar na yi musu rantsuwa cewa zan fitar da su daga Masar zuwa ƙasar da na samo musu, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe.
naquele dia jurei-lhes que os tiraria da terra do Egito para uma terra que eu havia procurado, fluindo com leite e mel, que é a glória de todas as terras.
7 Na kuma ce musu, “Kowannenku ya zubar da mugayen siffofin da kuka kafa idanunku a kai, kuma kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Eu lhes disse: 'Cada um de vocês jogue fora as abominações de seus olhos'. Não se contaminem com os ídolos do Egito”. Eu sou Yahweh, vosso Deus”.
8 “‘Amma sai suka yi tawaye a kaina ba su kuwa saurare ni ba; ba su zubar da mugayen siffofin da suka kafa idanunsu a kai ba, balle su ƙi gumakan Masar. Saboda haka zan zubo hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a Masar.
“““Mas eles se rebelaram contra mim e não me quiseram ouvir. Nem todos jogaram fora as abominações de seus olhos. Eles também não abandonaram os ídolos do Egito. Então eu disse que derramaria minha ira sobre eles, para cumprir minha ira contra eles no meio da terra do Egito.
9 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da suka zauna a ciki da kuma a idanun al’ummai da na bayyana kaina ga Isra’ilawa ta wurin fitar da su daga Masar.
Mas trabalhei por meu nome, para que não fosse profanado aos olhos das nações entre as quais se encontravam, a cujos olhos me fiz conhecer ao trazê-los para fora da terra do Egito.
10 Saboda haka na fisshe su daga Masar na kawo su cikin hamada.
Assim, fiz com que saíssem da terra do Egito e os levei para o deserto.
11 Na ba su ƙa’idodina na kuma sanar musu da dokokina, gama mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu.
Dei-lhes meus estatutos e mostrei-lhes minhas ordenanças, que se um homem o fizer, viverá nelas.
12 Na kuma ba su Asabbataina kamar alama tsakaninmu, domin su san cewa Ni Ubangiji ne yake tsarkake su.
Além disso, também lhes dei meus sábados, para serem um sinal entre mim e eles, para que soubessem que eu sou Yahweh que os santifica.
13 “‘Duk da haka mutanen Isra’ila suka yi mini tawaye a cikin hamada. Ba su bi ƙa’idodina ba amma suka ki dokokina, ko da yake mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu, suka ɓata Asabbataina ƙwarai. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma hallaka su a hamada.
“““Mas a casa de Israel se rebelou contra mim no deserto. Eles não entraram em meus estatutos e rejeitaram minhas ordenanças, as quais, se um homem as cumprir, viverá nelas. Eles profanaram muito os meus sábados. Então eu disse que derramaria minha ira sobre eles no deserto, para consumi-los.
14 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
Mas trabalhei por meu nome, para que não fosse profanado aos olhos das nações, a cujos olhos os fiz sair.
15 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu a hamada cewa ba zan kawo su ƙasar da na ba su ba, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe,
Além disso, também lhes jurei no deserto que não os traria para a terra que lhes havia dado, que mana leite e mel, que é a glória de todas as terras,
16 domin sun ƙi dokokina ba su kuwa bi ƙa’idodina ba suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Gama zukatansu sun fi so su bauta wa gumakansu.
porque rejeitaram minhas ordenanças, não andaram em meus estatutos e profanaram meus sábados; pois seu coração foi atrás de seus ídolos.
17 Duk da haka na dube su ta tausayi ba zan hallaka su ko in kawo ƙarshensu a hamada ba.
Nevertheless meu olho os poupou, e eu não os destruí. Eu não fiz um fim completo deles no deserto.
18 Na faɗa wa’ya’yansu a hamada, “Kada ku bi farillai kakanninku ko ku kiyaye dokokinsu ko ku ƙazantar da kanku da gumakansu.
Eu disse a seus filhos no deserto: 'Não andem nos estatutos de seus pais'. Não observem as ordenanças deles nem se sujem com os ídolos deles.
19 Ni ne Ubangiji Allahnku; ku bi ƙa’idodina ku kuma kula ku kiyaye dokokina.
Eu sou Yahweh, vosso Deus. Caminhe em meus estatutos, cumpra minhas ordenanças e faça-as.
20 Ku kiyaye Asabbataina da tsarki, don su zama alama tsakaninmu. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Allahnku.”
Santificai meus sábados. Eles serão um sinal entre mim e vocês, para que saibam que eu sou Yahweh, vosso Deus”.
21 “‘Amma’ya’yan suka yi mini tawaye. Ba su bi ƙa’idodina ba, ba su kula su kiyaye dokokina ba, ko da yake mutumin da ya kiyaye su zai rayu ta wurinsu, suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a hamada.
“““Mas as crianças se rebelaram contra mim. Eles não entraram em meus estatutos e não cumpriram minhas ordenanças para fazê-los, o que se um homem o fizer, ele viverá neles. Eles profanaram meus sábados. Então eu disse que derramaria minha ira sobre eles, para cumprir minha ira contra eles no deserto.
22 Amma na janye hannuna, kuma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
Nevertheless Retirei minha mão e trabalhei em nome do meu nome, para que não fosse profanada aos olhos das nações, aos olhos de quem os trouxe para fora.
23 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu cewa zan watsar da su cikin al’ummai in kuma warwatsa su cikin ƙasashe,
Além disso, jurei-lhes no deserto, que os dispersaria entre as nações e os dispersaria pelos países,
24 domin ba su kiyaye dokokina ba amma suka ƙi ƙa’idodina suka kuma ƙazantar da Asabbataina, idanunsu suka yi sha’awar gumakan kakanninsu.
porque eles não haviam executado minhas ordenanças, mas haviam rejeitado meus estatutos, e haviam profanado meus sábados, e seus olhos estavam atrás dos ídolos de seus pais.
25 Na kuma ba da su ga farillan da ba su da kyau da dokokin da ba za su rayu ta wurinsu ba;
Além disso, também lhes dei estatutos que não eram bons, e ordenanças nas quais eles não podiam viver.
26 na bari suka ƙazantu ta wurin kyautai, hadayar kowane ɗan fari don in cika su da abin tsoro domin su san cewa ni ne Ubangiji.’
Eu os poluí em seus próprios dons, na medida em que fizeram com que tudo o que abre o ventre passasse pelo fogo, para que eu pudesse deixá-los desolados, até o fim, para que eles soubessem que eu sou Yahweh”.
27 “Saboda haka, ɗan mutum, ka yi magana da mutanen Isra’ila ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a wannan kuma kakanninku suka saɓe ni ta wurin yashe ni.
“Portanto, filho do homem, fale com a casa de Israel e lhes diga: 'O Senhor Javé diz: “Além disso, nisto seus pais me blasfemaram, pois cometeram uma transgressão contra mim.
28 Sa’ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su suka kuma ga tudu mai tsawo ko itace mai ganye, a can suka miƙa hadayunsu, suka yi sadakokin da suka tsokane ni na yi fushi, suka miƙa turaren ƙanshinsu suka kuma zuba sadakokinsu na sha.
Pois quando os trouxe para a terra que jurei dar-lhes, então eles viram cada colina alta e cada árvore grossa, e ali ofereceram seus sacrifícios, e ali apresentaram a provocação de sua oferta. Ali também fizeram seu aroma agradável, e ali derramaram suas ofertas de bebida.
29 Sai na ce musu, Wane ɗakin tsafi kuke tafiya?’” (Ana ce da shi Bama har wa yau.)
Então eu lhes disse: “O que significa o lugar alto onde você vai?”. Então seu nome é chamado Bamah até hoje”.
30 “Domin haka ka faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa za ku ƙazantar da kanku yadda kakanninku suka yi ne ku yi sha’awar mugayen siffofinsu?
“Portanto, diga à casa de Israel: 'O Senhor Javé diz: “Vocês se poluem no caminho de seus pais? Vocês se fazem de prostitutas depois de suas abominações?
31 Sa’ad da kuka miƙa kyautai naku, hadayar’ya’yanku maza a wuta, kuna cin gaba da ƙazantar da kanku da duka gumakanku har wa yau. Zan bari ku nemi shawarata, ya gidan Isra’ila? Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba zan bari ku nemi shawarata ba.
Quando vocês oferecem seus dons, quando fazem seus filhos passar pelo fogo, vocês se poluem com todos os seus ídolos até os dias de hoje? Devo ser consultado por vocês, casa de Israel? Como eu vivo, diz o Senhor Javé, não serei consultado por vocês!
32 “‘Kukan ce, “Kuna so ku zama kamar sauran al’ummai, kamar sauran mutanen duniya, waɗanda suke bauta wa itace da dutse.” Amma abin da kuke tunani ba zai taɓa faruwa ba.
“” “O que lhe vem à mente não será de forma alguma, no sentido de que você diz: “Seremos como as nações, como as famílias dos países, para servir madeira e pedra”.
33 Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan yi mulki a kanku da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
Enquanto eu viver”, diz o Senhor Javé, “certamente com uma mão poderosa, com um braço estendido e com a ira derramada, eu serei rei sobre vós”.
34 Zan fitar da ku daga al’ummai in tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
Eu vos tirarei dos povos, e vos congregarei dos países onde estais espalhados com uma mão poderosa, com um braço estendido, e com a ira derramada”.
35 Zan kawo ku cikin hamadar al’ummai a can kuwa, fuska da fuska, zan hukunta ku.
Eu os levarei ao deserto dos povos, e lá entrarei em juízo com vocês face a face.
36 Yadda na hukunta kakanninku a hamadar ƙasar Masar, haka zan hukunta ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Assim como entrei em juízo com seus pais no deserto da terra do Egito, também eu entrarei em juízo com você”, diz o Senhor Javé.
37 Zan lura da ku yayinda kuke wucewa ƙarƙashin sanda, zan kuma kawo ku cikin daurin alkawari.
“Farei com que você passe debaixo da vara, e o levarei ao vínculo do pacto”.
38 Zan fitar da waɗanda suke mini tayarwa da kuma’yan tawaye. Ko da yake zan fitar da su daga ƙasar da suke zama, duk da haka ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
“Expurgarei dentre vós os rebeldes e aqueles que me desobedecerem”. Eu os tirarei da terra onde vivem, mas eles não entrarão na terra de Israel. Então vocês saberão que eu sou Yahweh”.
39 “‘Game da ku, ya gidan Isra’ila, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tafi ku bauta wa gumakanku, kowannenku! Amma daga baya tabbatacce za ku saurare ni ba kuwa za ku ƙara ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku ba.
“'Quanto a você, casa de Israel, o Senhor Javé diz: “Vá, todos servem a seus ídolos, e daqui em diante também, se não me ouvirdes; mas não profanareis mais meu santo nome com vossos dons e com vossos ídolos.
40 Gama a kan dutsena mai tsarki, dutse mai tsayi na Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, a can a ƙasar gidan Isra’ila gaba ɗaya za su bauta mini, a can kuwa zan karɓe su. A can zan bukaci hadayunku da sadake sadakenku mafi kyau, tare da dukan tsarkakan hadayunku.
Pois em minha montanha santa, na montanha do alto de Israel”, diz o Senhor Javé, “ali toda a casa de Israel, todos eles, me servirão na terra”. Ali as aceitarei, e ali requererei suas ofertas e as primícias de suas ofertas, com todas as suas coisas santas”.
41 Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa’ad da na fitar da ku daga al’ummai na kuma tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, zan kuma nuna kaina mai tsarki a cikinku a idon al’ummai.
Eu os aceitarei como um aroma agradável quando os tirar dos povos e os recolher dos países nos quais foram dispersos. Serei santificado em vocês, aos olhos das nações.
42 Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na kawo ku cikin ƙasar Isra’ila, ƙasar da na ɗaga hannu na rantse zan ba wa kakanninku.
Saberão que eu sou Iavé quando os levar para a terra de Israel, para o país que jurei dar a seus pais.
43 A can za ku tuna da halinku da kuma dukan ayyukanku waɗanda kuka ɓata kanku da su, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda mugayen abubuwan da kuka aikata.
Lá vocês se lembrarão de seus caminhos, e de todos os seus atos nos quais vocês se poluíram. Então, odiar-vos-eis a vós mesmos por todos os vossos males que cometestes.
44 Za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na yi muku haka saboda sunana ba bisa ga mugayen hanyoyinku da ayyukanku marasa kyau ba, ya gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Sabereis que eu sou Yahweh, quando eu tiver tratado convosco em meu nome, não de acordo com vossos maus caminhos, nem de acordo com vossos atos corruptos, vossa casa de Israel”, diz o Senhor Yahweh”. A palavra de
45 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Yahweh veio até mim, dizendo:
46 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka wajen kudu; ka yi wa’azi a kan kudu ka kuma yi annabci a kan kurmin ƙasar kudu.
“Filho do homem, ponha seu rosto para o sul, pregue para o sul e profetize contra a floresta do campo no sul”.
47 Ka faɗa wa kurmin kudanci, ‘Ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da sa maka wuta, za tă kuwa cinye dukan itatuwanki sarai, da ɗanye da busasshe. Ba za a kashe wutar da take ci ba, kuma kowace fuska a kudu zuwa arewa za tă ƙone.
Tell a floresta do sul, 'Ouve a palavra de Javé: O Senhor Javé diz: “Eis que eu acenderei um fogo em ti, e ele devorará toda árvore verde em ti, e toda árvore seca”. A chama ardente não se apagará, e todas as faces do sul para o norte serão queimadas por ela.
48 Kowa zai san cewa Ni Ubangiji ne ya ƙuna ta; ba za a kashe ta ba.’”
All a carne verá que eu, Yahweh, a acendi. Ela não se apagará””.
49 Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Suna zance a kaina cewa, ‘Ba misalai kawai yake yi ba?’”
Then Eu disse: “Ah Senhor Yahweh! Dizem de mim: 'Ele não é um orador de parábolas?'”