< Ezekiyel 20 >

1 A shekara ta bakwai, a wata na biyar a rana ta goma, waɗansu dattawan Isra’ila suka zo don su nemi nufin Ubangiji, suka kuwa zauna a ƙasa a gabana.
هفت سال و پنج ماه و ده روز از تبعید ما می‌گذشت، که عده‌ای از رهبران اسرائیل آمدند تا از خداوند هدایت بطلبند. ایشان مقابل من نشستند و منتظر جواب ماندند.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
آنگاه خداوند این پیغام را به من داد:
3 “Ɗan mutum, ka yi magana da dattawan Isra’ila ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kun zo ne ku nemi shawarata? Muddin ina raye, ba zan bari ku nemi shawarata ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
«ای پسر انسان، به رهبران اسرائیل بگو که خداوند یهوه چنین می‌فرماید: «چگونه جرأت کرده‌اید که بیایید و از من هدایت بطلبید؟ به حیات خود قسم که هدایتی از من نخواهید یافت!
4 “Za ka hukunta su? Za ka hukunta su, ɗan mutum? To, sai ka kalubalance su da ayyukan banƙyamar kakanninsu
«ای پسر انسان، ایشان را محکوم کن. گناهان این قوم را، از زمان پدرانشان تاکنون، به یادشان بیاور.
5 ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na zaɓi Isra’ila, na ɗaga hannuna, na rantse wa zuriyar gidan Yaƙub na kuma bayyana kaina gare su a Masar da hannun da na ɗaga na ce musu, “Ni ne Ubangiji Allahnku.”
به ایشان بگو خداوند یهوه چنین می‌گوید: «وقتی قوم اسرائیل را انتخاب کردم و خود را در مصر بر ایشان آشکار ساختم، برای آنان قسم خوردم که ایشان را از مصر بیرون آورده، به سرزمینی بیاورم که برای ایشان در نظر گرفته بودم، یعنی به سرزمینی که شیر و عسل در آن جاریست و بهترین جای دنیاست.
6 A ranar na yi musu rantsuwa cewa zan fitar da su daga Masar zuwa ƙasar da na samo musu, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe.
7 Na kuma ce musu, “Kowannenku ya zubar da mugayen siffofin da kuka kafa idanunku a kai, kuma kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
«پس به ایشان گفتم که بتهای نفرت‌انگیز و مورد علاقه‌شان را از خود دور کنند و خود را با پرستش خدایان مصری نجس نسازند، زیرا من یهوه خدای ایشان هستم.
8 “‘Amma sai suka yi tawaye a kaina ba su kuwa saurare ni ba; ba su zubar da mugayen siffofin da suka kafa idanunsu a kai ba, balle su ƙi gumakan Masar. Saboda haka zan zubo hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a Masar.
اما آنان یاغی شده، نخواستند به من گوش فرا دهند و از پرستش بتهای خود و خدایان مصر دست بکشند. پس خواستم که خشم و غضب خود را همان جا در مصر بر ایشان نازل کنم.
9 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da suka zauna a ciki da kuma a idanun al’ummai da na bayyana kaina ga Isra’ilawa ta wurin fitar da su daga Masar.
اما برای حفظ حرمت نام خود، این کار را نکردم، مبادا مصری‌ها خدای اسرائیل را تمسخر کرده، بگویند که نتوانست ایشان را از آسیب و بلا دور نگاه دارد. پس در برابر چشمان مصری‌ها، قوم خود اسرائیل را از مصر بیرون آوردم و به بیابان هدایت کردم.
10 Saboda haka na fisshe su daga Masar na kawo su cikin hamada.
11 Na ba su ƙa’idodina na kuma sanar musu da dokokina, gama mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu.
در آنجا احکام و قوانین خود را به ایشان اعطا نمودم تا مطابق آنها رفتار کنند و زنده بمانند؛
12 Na kuma ba su Asabbataina kamar alama tsakaninmu, domin su san cewa Ni Ubangiji ne yake tsarkake su.
و روز شَبّات را به ایشان دادم تا در هفته یک روز استراحت کنند. این علامتی بود بین من و ایشان، تا به یاد آورند که این من یهوه هستم که ایشان را تقدیس و جدا کرده، قوم خود ساخته‌ام.
13 “‘Duk da haka mutanen Isra’ila suka yi mini tawaye a cikin hamada. Ba su bi ƙa’idodina ba amma suka ki dokokina, ko da yake mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu, suka ɓata Asabbataina ƙwarai. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma hallaka su a hamada.
«اما بنی‌اسرائیل در بیابان نیز از من اطاعت نکردند. آنان قوانین مرا زیر پا گذاشتند و از احکام حیات‌بخش من سرپیچی کردند، و حرمت روز شَبّات را نگاه نداشتند. پس خواستم که خشم و غضب خود را همان جا در بیابان بر ایشان نازل کنم و نابودشان سازم.
14 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
اما باز برای حفظ حرمت نام خود، از هلاک کردن ایشان صرف‌نظر نمودم، مبادا اقوامی که دیدند من چگونه بنی‌اسرائیل را از مصر بیرون آوردم، بگویند:”چون خدا نتوانست از ایشان محافظت کند، ایشان را از بین برد.“
15 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu a hamada cewa ba zan kawo su ƙasar da na ba su ba, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe,
اما در بیابان قسم خوردم که ایشان را به سرزمینی که به آنان داده بودم، نیاورم به سرزمینی که شیر و عسل در آن جاریست و بهترین جای دنیاست.
16 domin sun ƙi dokokina ba su kuwa bi ƙa’idodina ba suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Gama zukatansu sun fi so su bauta wa gumakansu.
زیرا از احکام من سرپیچی کرده، قوانین مرا شکستند و روز شَبّات را بی‌حرمت کرده، به سوی بتها کشیده شدند.
17 Duk da haka na dube su ta tausayi ba zan hallaka su ko in kawo ƙarshensu a hamada ba.
با وجود این، بر آنان ترحم نمودم و ایشان را در بیابان به طور کامل هلاک نکردم و از بین نبردم.
18 Na faɗa wa’ya’yansu a hamada, “Kada ku bi farillai kakanninku ko ku kiyaye dokokinsu ko ku ƙazantar da kanku da gumakansu.
«بنابراین، در بیابان به فرزندان ایشان گفتم:”به راه پدران خود نروید و به سنت آنها عمل نکنید و خود را با پرستش بتهای ایشان نجس نسازید،
19 Ni ne Ubangiji Allahnku; ku bi ƙa’idodina ku kuma kula ku kiyaye dokokina.
چون یهوه خدای شما، من هستم؛ پس فقط از قوانین من پیروی کنید و احکام مرا بجا آورید؛
20 Ku kiyaye Asabbataina da tsarki, don su zama alama tsakaninmu. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Allahnku.”
و حرمت روزهای شَبّات را نگاه دارید، زیرا روز شبّات، نشان عهد بین ماست تا به یادتان آورد که من یهوه، خدای شما هستم.“
21 “‘Amma’ya’yan suka yi mini tawaye. Ba su bi ƙa’idodina ba, ba su kula su kiyaye dokokina ba, ko da yake mutumin da ya kiyaye su zai rayu ta wurinsu, suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a hamada.
«اما فرزندان ایشان هم نافرمانی کردند. آنان قوانین مرا شکستند و از احکام حیات‌بخش من سرپیچی کردند و حرمت روز شَبّات را نیز نگاه نداشتند. پس خواستم که خشم و غضب خود را همان جا در بیابان بر ایشان نازل کنم و همه را از بین ببرم.
22 Amma na janye hannuna, kuma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
اما باز هم برای حفظ حرمت نام خود در میان اقوامی که قدرت مرا به هنگام بیرون آوردن بنی‌اسرائیل از مصر دیده بودند، ایشان را از بین نبردم.
23 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu cewa zan watsar da su cikin al’ummai in kuma warwatsa su cikin ƙasashe,
اما همان زمان که در بیابان بودند، قسم خوردم که ایشان را در سراسر جهان پراکنده سازم،
24 domin ba su kiyaye dokokina ba amma suka ƙi ƙa’idodina suka kuma ƙazantar da Asabbataina, idanunsu suka yi sha’awar gumakan kakanninsu.
زیرا احکام مرا بجا نیاوردند و قوانین مرا شکستند و روز شَبّات را بی‌حرمت کرده، به سوی بتهای پدرانشان بازگشتند.
25 Na kuma ba da su ga farillan da ba su da kyau da dokokin da ba za su rayu ta wurinsu ba;
پس من نیز اجازه دادم قوانین و احکامی را پیروی کنند که حیات در آنها نبود.
26 na bari suka ƙazantu ta wurin kyautai, hadayar kowane ɗan fari don in cika su da abin tsoro domin su san cewa ni ne Ubangiji.’
بله، گذاشتم فرزندان خود را به عنوان قربانی برای بتهایشان بسوزانند و با این کار، خود را نجس سازند. بدین ترتیب ایشان را مجازات کردم تا بدانند که من یهوه هستم.
27 “Saboda haka, ɗan mutum, ka yi magana da mutanen Isra’ila ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a wannan kuma kakanninku suka saɓe ni ta wurin yashe ni.
«ای پسر انسان، به قوم اسرائیل بگو که وقتی پدرانشان را به سرزمین موعود آوردم، در آنجا نیز به من خیانت ورزیدند، چون روی هر تپهٔ بلند و زیر هر درخت سبز، برای بتها قربانی می‌کردند و بخور می‌سوزاندند؛ عطر و بخور خوشبو و هدایای نوشیدنی خود را می‌آوردند و به آنها تقدیم می‌کردند، و با این کارها، خشم مرا برمی‌انگیختند.
28 Sa’ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su suka kuma ga tudu mai tsawo ko itace mai ganye, a can suka miƙa hadayunsu, suka yi sadakokin da suka tsokane ni na yi fushi, suka miƙa turaren ƙanshinsu suka kuma zuba sadakokinsu na sha.
29 Sai na ce musu, Wane ɗakin tsafi kuke tafiya?’” (Ana ce da shi Bama har wa yau.)
به ایشان گفتم:”این مکان بلند که برای قربانی به آنجا می‌روید، چیست؟“به همین جهت تا به حال آن محل را مکان بلند می‌نامند.»
30 “Domin haka ka faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa za ku ƙazantar da kanku yadda kakanninku suka yi ne ku yi sha’awar mugayen siffofinsu?
آنگاه خداوند یهوه فرمود که به آنانی که نزد من آمده بودند، از جانب او چنین بگویم: «آیا شما نیز می‌خواهید مانند پدرانتان، با بت‌پرستی، خود را نجس سازید؟
31 Sa’ad da kuka miƙa kyautai naku, hadayar’ya’yanku maza a wuta, kuna cin gaba da ƙazantar da kanku da duka gumakanku har wa yau. Zan bari ku nemi shawarata, ya gidan Isra’ila? Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba zan bari ku nemi shawarata ba.
شما هنوز هم برای بتها هدیه می‌آورید و پسران کوچک خود را برای آنها قربانی کرده، می‌سوزانید؛ پس چگونه انتظار دارید که به دعاهای شما گوش دهم و شما را هدایت نمایم؟ به حیات خود قسم که هیچ هدایت و پیغامی به شما نخواهم داد.
32 “‘Kukan ce, “Kuna so ku zama kamar sauran al’ummai, kamar sauran mutanen duniya, waɗanda suke bauta wa itace da dutse.” Amma abin da kuke tunani ba zai taɓa faruwa ba.
«آنچه در فکرتان هست، هرگز عملی نخواهد شد. شما می‌خواهید مثل قومهای مجاور شوید و مانند آنها، بتهای چوبی و سنگی را بپرستید.
33 Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan yi mulki a kanku da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
به حیات خود سوگند که من خود، با مشتی آهنین و قدرتی عظیم و با خشمی برافروخته، بر شما سلطنت خواهم نمود!
34 Zan fitar da ku daga al’ummai in tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
با قدرت و قهری عظیم، شما را از سرزمینهایی که در آنجا پراکنده هستید، بیرون خواهم آورد.
35 Zan kawo ku cikin hamadar al’ummai a can kuwa, fuska da fuska, zan hukunta ku.
شما را به بیابان امتها آورده، در آنجا شما را داوری و محکوم خواهم نمود، همان‌گونه که پدرانتان را پس از بیرون آوردن از مصر، در بیابان داوری و محکوم کردم.
36 Yadda na hukunta kakanninku a hamadar ƙasar Masar, haka zan hukunta ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
37 Zan lura da ku yayinda kuke wucewa ƙarƙashin sanda, zan kuma kawo ku cikin daurin alkawari.
شما را به دقت خواهم شمرد تا فقط عده کمی از شما بازگردند،
38 Zan fitar da waɗanda suke mini tayarwa da kuma’yan tawaye. Ko da yake zan fitar da su daga ƙasar da suke zama, duk da haka ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
و بقیه را که سرکش بوده، به من گناه می‌کنند، از میان شما جدا خواهم نمود. ایشان را از سرزمینهایی که به آنجا تبعید شده‌اند بیرون خواهم آورد، ولی نخواهم گذاشت وارد سرزمین اسرائیل گردند. وقتی اینها اتفاق افتاد، خواهید دانست که من یهوه هستم.
39 “‘Game da ku, ya gidan Isra’ila, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tafi ku bauta wa gumakanku, kowannenku! Amma daga baya tabbatacce za ku saurare ni ba kuwa za ku ƙara ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku ba.
«اما اگر اصرار دارید که به بت‌پرستی خود ادامه دهید، من مانع شما نمی‌شوم! ولی بدانید که پس از آن، مرا اطاعت خواهید نمود و دیگر نام مقدّس مرا با تقدیم هدایا و قربانی به بتها، بی‌حرمت نخواهید ساخت.
40 Gama a kan dutsena mai tsarki, dutse mai tsayi na Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, a can a ƙasar gidan Isra’ila gaba ɗaya za su bauta mini, a can kuwa zan karɓe su. A can zan bukaci hadayunku da sadake sadakenku mafi kyau, tare da dukan tsarkakan hadayunku.
زیرا در اورشلیم، روی کوه مقدّس من، همه اسرائیلی‌ها مرا پرستش خواهند نمود. در آنجا از شما خشنود خواهم شد و قربانیها و بهترین هدایا و نذرهای مقدّس شما را خواهم پذیرفت.
41 Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa’ad da na fitar da ku daga al’ummai na kuma tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, zan kuma nuna kaina mai tsarki a cikinku a idon al’ummai.
وقتی شما را از تبعید بازگردانم، برایم همچون هدایای خوشبو خواهید بود و قومها خواهند دید که در دل و رفتار شما چه تغییر بزرگی ایجاد شده است.
42 Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na kawo ku cikin ƙasar Isra’ila, ƙasar da na ɗaga hannu na rantse zan ba wa kakanninku.
زمانی که شما را به وطن خودتان بازگردانم، یعنی به سرزمینی که وعده آن را به پدرانتان دادم، خواهید دانست که من خداوند هستم.
43 A can za ku tuna da halinku da kuma dukan ayyukanku waɗanda kuka ɓata kanku da su, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda mugayen abubuwan da kuka aikata.
آنگاه تمام گناهان گذشتهٔ خود را به یاد آورده، به سبب همهٔ کارهای زشتی که کرده‌اید، از خود متنفر خواهید شد.
44 Za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na yi muku haka saboda sunana ba bisa ga mugayen hanyoyinku da ayyukanku marasa kyau ba, ya gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
ای قوم اسرائیل، وقتی با وجود تمام بدیها و شرارتهایتان، به خاطر حرمت نام خود، شما را برکت دهم، آنگاه خواهید دانست که من یهوه هستم.»
45 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
سپس این پیغام از جانب خداوند به من رسید:
46 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka wajen kudu; ka yi wa’azi a kan kudu ka kuma yi annabci a kan kurmin ƙasar kudu.
«ای پسر انسان، به سوی اورشلیم نگاه کن و کلام مرا بر ضد آن، و بر ضد دشتهای پوشیده از جنگل جنوب، اعلام نما.
47 Ka faɗa wa kurmin kudanci, ‘Ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da sa maka wuta, za tă kuwa cinye dukan itatuwanki sarai, da ɗanye da busasshe. Ba za a kashe wutar da take ci ba, kuma kowace fuska a kudu zuwa arewa za tă ƙone.
درباره آن نبوّت نما و بگو که ای جنگل انبوه، به کلام خداوند گوش بده! خداوند می‌فرماید: من در تو آتشی می‌افروزم که تمام درختان سبز و خشک تو را بسوزاند. شعله‌های مهیب آن خاموش نخواهد شد و همه مردم حرارت آن را احساس خواهند کرد.
48 Kowa zai san cewa Ni Ubangiji ne ya ƙuna ta; ba za a kashe ta ba.’”
آنگاه همه خواهند دانست که من، خداوند، آن را افروخته‌ام و خاموش نخواهد شد.»
49 Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Suna zance a kaina cewa, ‘Ba misalai kawai yake yi ba?’”
گفتم: «ای خداوند یهوه، آنها به من می‌گویند که چرا با معما با ایشان سخن می‌گویم!»

< Ezekiyel 20 >