< Ezekiyel 20 >
1 A shekara ta bakwai, a wata na biyar a rana ta goma, waɗansu dattawan Isra’ila suka zo don su nemi nufin Ubangiji, suka kuwa zauna a ƙasa a gabana.
Un notikās septītā gadā, piektā mēnesī, desmitā mēneša dienā, tad nāca vīri no Israēla vecajiem, To Kungu vaicāt, un apsēdās manā priekšā.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Tad Tā Kunga vārds uz mani notika sacīdams:
3 “Ɗan mutum, ka yi magana da dattawan Isra’ila ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kun zo ne ku nemi shawarata? Muddin ina raye, ba zan bari ku nemi shawarata ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
Cilvēka bērns, runā uz Israēla vecajiem un saki uz tiem: tā saka Tas Kungs Dievs: vai jūs esat nākuši, Mani vaicāt? Tik tiešām kā Es dzīvoju, saka Tas Kungs Dievs: Es negribu, ka jūs Mani vaicājiet.
4 “Za ka hukunta su? Za ka hukunta su, ɗan mutum? To, sai ka kalubalance su da ayyukan banƙyamar kakanninsu
Vai tu tos gribi tiesāt? Vai tu gribi tiesāt, cilvēka bērns? Tad stāsti tiem viņu tēvu negantības!
5 ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na zaɓi Isra’ila, na ɗaga hannuna, na rantse wa zuriyar gidan Yaƙub na kuma bayyana kaina gare su a Masar da hannun da na ɗaga na ce musu, “Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Un saki uz tiem: tā saka Tas Kungs Dievs: tai dienā, kad Es Israēli izredzēju, tad Es pacēlu Savu roku pār Jēkaba nama dzimumu un tiem parādījos Ēģiptes zemē; Es pacēlu Savu roku pār tiem un sacīju: Es esmu Tas Kungs, jūsu Dievs.
6 A ranar na yi musu rantsuwa cewa zan fitar da su daga Masar zuwa ƙasar da na samo musu, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe.
Tai dienā Es pacēlu Savu roku pār tiem un tos izvedu no Ēģiptes zemes uz zemi, ko Es priekš viņiem biju izlūkojis, kur piens un medus tek, kas ir jaukāka pār visām zemēm.
7 Na kuma ce musu, “Kowannenku ya zubar da mugayen siffofin da kuka kafa idanunku a kai, kuma kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Un Es uz tiem sacīju: atmetiet ikviens savu acu gānekļus no sevis nost un neapgānāties ar Ēģiptes elkiem; Es esmu Tas Kungs, jūsu Dievs.
8 “‘Amma sai suka yi tawaye a kaina ba su kuwa saurare ni ba; ba su zubar da mugayen siffofin da suka kafa idanunsu a kai ba, balle su ƙi gumakan Masar. Saboda haka zan zubo hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a Masar.
Bet tie bija stūrgalvīgi pret Mani un negribēja Mani klausīt; neviens neatmeta savu acu gānekļus un neatstājās no Ēģiptes elkiem. Tāpēc Es sacīju: Es pār tiem izgāzīšu Savu bardzību un izdarīšu pie tiem Savu dusmību pašā Ēģiptes zemē.
9 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da suka zauna a ciki da kuma a idanun al’ummai da na bayyana kaina ga Isra’ilawa ta wurin fitar da su daga Masar.
Bet es darīju sava vārda dēļ, ka tas netaptu sagānīts priekš pagānu acīm, kuru vidū tie bija, priekš kuru acīm Es tiem biju parādījies, tos izvest no Ēģiptes zemes.
10 Saboda haka na fisshe su daga Masar na kawo su cikin hamada.
Un Es tos izvedu no Ēģiptes zemes un tos vadīju tuksnesī.
11 Na ba su ƙa’idodina na kuma sanar musu da dokokina, gama mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu.
Un Es tiem devu Savus likumus un tiem darīju zināmas tiesas, ko cilvēkam būs darīt, lai caur tām dzīvo.
12 Na kuma ba su Asabbataina kamar alama tsakaninmu, domin su san cewa Ni Ubangiji ne yake tsarkake su.
Es tiem arī devu Savas svētās dienas, ka tās būtu par zīmi starp Mani un viņiem, lai tie atzītu, ka Es esmu Tas Kungs, kas tos svētī.
13 “‘Duk da haka mutanen Isra’ila suka yi mini tawaye a cikin hamada. Ba su bi ƙa’idodina ba amma suka ki dokokina, ko da yake mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu, suka ɓata Asabbataina ƙwarai. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma hallaka su a hamada.
Bet Israēla nams bija stūrgalvīgs pret Mani tuksnesī; tie nestaigāja Manos likumos un atmeta Manas tiesas, ko cilvēkam būs darīt, lai caur tām dzīvo; un tie ļoti sagānīja Manas svētās dienas, tā ka Es sacīju: Es Savu bardzību pār tiem gribu izgāzt tuksnesī un tiem darīt galu.
14 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
Bet Es darīju Sava vārda dēļ, ka tas netaptu sagānīts priekš to pagānu acīm, priekš kuru acīm Es tos biju izvedis.
15 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu a hamada cewa ba zan kawo su ƙasar da na ba su ba, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe,
Un tomēr Es Savu roku pacēlu pret tiem tuksnesī, tos nevest tai zemē, ko Es tiem biju devis, kur piens un medus tek, kas ir jaukāka pār visām zemēm:
16 domin sun ƙi dokokina ba su kuwa bi ƙa’idodina ba suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Gama zukatansu sun fi so su bauta wa gumakansu.
Tādēļ ka tie atmeta Manas tiesas un nestaigāja Manos likumos un sagānīja Manas svētās dienas; jo viņu sirds dzinās pakaļ viņu elkiem.
17 Duk da haka na dube su ta tausayi ba zan hallaka su ko in kawo ƙarshensu a hamada ba.
Bet Mana acs tos žēloja, ka Es tos nenomaitāju un tiem galu nedarīju tuksnesī.
18 Na faɗa wa’ya’yansu a hamada, “Kada ku bi farillai kakanninku ko ku kiyaye dokokinsu ko ku ƙazantar da kanku da gumakansu.
Un Es sacīju uz viņu bērniem tuksnesī: nestaigājiet savu tēvu likumos un nesargājiet viņu tiesas un neapgānāties ar viņu elkiem,
19 Ni ne Ubangiji Allahnku; ku bi ƙa’idodina ku kuma kula ku kiyaye dokokina.
Es esmu Tas Kungs, jūsu Dievs; staigājiet manos likumos un sargājiet manas tiesas un dariet tās.
20 Ku kiyaye Asabbataina da tsarki, don su zama alama tsakaninmu. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Allahnku.”
Un svētījiet manas svētās dienas, lai tās ir par zīmi starp mani un jums, un jūs samanāt, ka Es esmu Tas Kungs, jūsu Dievs.
21 “‘Amma’ya’yan suka yi mini tawaye. Ba su bi ƙa’idodina ba, ba su kula su kiyaye dokokina ba, ko da yake mutumin da ya kiyaye su zai rayu ta wurinsu, suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a hamada.
Bet arī tie bērni bija stūrgalvīgi pret Mani, tie nestaigāja Manos likumos un nesargāja Manas tiesas, tās nedarīdami, ko cilvēkam būs darīt, lai caur tām dzīvo; tie sagānīja Manas svētās dienas, tā ka Es sacīju: Es Savu bardzību pār tiem gribu izgāzt un Savu dusmību pret tiem izdarīt tuksnesī.
22 Amma na janye hannuna, kuma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
Bet Es atturēju Savu roku Sava vārda dēļ, ka tas netaptu sagānīts priekš to pagānu acīm, priekš kuru acīm Es tos biju izvedis.
23 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu cewa zan watsar da su cikin al’ummai in kuma warwatsa su cikin ƙasashe,
Un taču Es pacēlu Savu roku pret tiem tuksnesī, tos izkaisīt starp tiem pagāniem un tos izputināt pa tām valstīm,
24 domin ba su kiyaye dokokina ba amma suka ƙi ƙa’idodina suka kuma ƙazantar da Asabbataina, idanunsu suka yi sha’awar gumakan kakanninsu.
Tādēļ ka tie Manas tiesas nebija darījuši, bet bija atmetuši Manus likumus un sagānījuši Manas svētās dienas un viņu acis dzinās pakaļ viņu tēvu elkiem.
25 Na kuma ba da su ga farillan da ba su da kyau da dokokin da ba za su rayu ta wurinsu ba;
Tāpēc Es tiem arī devu likumus, kas nebija labi, un tiesas, caur ko tie nevarēja dzīvot.
26 na bari suka ƙazantu ta wurin kyautai, hadayar kowane ɗan fari don in cika su da abin tsoro domin su san cewa ni ne Ubangiji.’
Un Es tos sagānīju ar viņu dāvanām, caur to, ka tie ikvienai pirmdzimtībai lika caur uguni iet, lai Es tos nopostītu, lai tie samanītu, ka Es esmu Tas Kungs.
27 “Saboda haka, ɗan mutum, ka yi magana da mutanen Isra’ila ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a wannan kuma kakanninku suka saɓe ni ta wurin yashe ni.
Tādēļ cilvēka bērns, runā uz Israēla namu un saki uz tiem: tā saka Tas Kungs Dievs: jūsu tēvi Mani vēl ir zaimojuši, atkāpdamies no Manis.
28 Sa’ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su suka kuma ga tudu mai tsawo ko itace mai ganye, a can suka miƙa hadayunsu, suka yi sadakokin da suka tsokane ni na yi fushi, suka miƙa turaren ƙanshinsu suka kuma zuba sadakokinsu na sha.
Kad Es tos biju novedis uz to zemi, par ko Savu roku biju pacēlis, viņiem to dot, tad tie izraudzījās ikkatru augstu pakalnu un ikkatru kuplu koku, un upurēja tur savus upurus un nonesa tur savas riebīgās dāvanas un kvēpināja tur savu saldo smaržu un upurēja turpat savus dzeramos upurus.
29 Sai na ce musu, Wane ɗakin tsafi kuke tafiya?’” (Ana ce da shi Bama har wa yau.)
Un Es uz tiem sacīju: kas tas par kalnu, kurp jūs ejat? Bet šī vārds līdz šai dienai ir nosaukts elka kalns.
30 “Domin haka ka faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa za ku ƙazantar da kanku yadda kakanninku suka yi ne ku yi sha’awar mugayen siffofinsu?
Tādēļ saki uz Israēla namu: tā saka Tas Kungs Dievs: jūs esat sagānījušies pa savu tēvu ceļiem un maukojušies viņu gānekļiem pakaļ.
31 Sa’ad da kuka miƙa kyautai naku, hadayar’ya’yanku maza a wuta, kuna cin gaba da ƙazantar da kanku da duka gumakanku har wa yau. Zan bari ku nemi shawarata, ya gidan Isra’ila? Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba zan bari ku nemi shawarata ba.
Tiešām, savas dāvanas upurēdami, saviem bērniem likdami caur uguni iet, jūs esat apgānījušies pie visiem saviem elkiem līdz šai dienai; vai Es no jums ļautos vaicāties, ak Israēla nams! Tik tiešām kā Es dzīvoju, saka Tas Kungs Dievs, Es negribu, ka jūs Mani vaicājiet.
32 “‘Kukan ce, “Kuna so ku zama kamar sauran al’ummai, kamar sauran mutanen duniya, waɗanda suke bauta wa itace da dutse.” Amma abin da kuke tunani ba zai taɓa faruwa ba.
Un kas jums prātā nācis, tas mūžam nenotiks, ka jūs sakāt: mēs turēsimies kā tās (pagānu) tautas un kā tās ciltis visās zemēs kalposim kokam un akmenim.
33 Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan yi mulki a kanku da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
Tik tiešām kā Es dzīvoju, saka Tas Kungs Dievs, ar stipru roku un izstieptu elkoni un ar izgāztu bardzību Es pār jums gribu valdīt.
34 Zan fitar da ku daga al’ummai in tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
Es jūs izvedīšu no tām tautām un jūs sapulcināšu no tām valstīm, kurp esat izkaisīti, ar stipru roku un izstieptu elkoni un ar izgāztu bardzību.
35 Zan kawo ku cikin hamadar al’ummai a can kuwa, fuska da fuska, zan hukunta ku.
Un Es jūs vedīšu uz tautu tuksnesi, un tur es ar jums tiesāšos vaigu vaigā.
36 Yadda na hukunta kakanninku a hamadar ƙasar Masar, haka zan hukunta ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Tā kā Es ar jūsu tēviem esmu tiesājies Ēģiptes zemes tuksnesī, tāpat Es ar jums tiesāšos, saka Tas Kungs Dievs.
37 Zan lura da ku yayinda kuke wucewa ƙarƙashin sanda, zan kuma kawo ku cikin daurin alkawari.
Un Es jums likšu staigāt apakš rīkstes un jūs vedīšu derības saitēs.
38 Zan fitar da waɗanda suke mini tayarwa da kuma’yan tawaye. Ko da yake zan fitar da su daga ƙasar da suke zama, duk da haka ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Un Es izmēzīšu no jums tos atkāpējus un atkritējus no Manis, un Es tos gan izvedīšu no tās zemes, kur piemita, bet uz Israēla zemi tie vairs nenāks, un jūs samanīsiet, ka Es esmu Tas Kungs.
39 “‘Game da ku, ya gidan Isra’ila, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tafi ku bauta wa gumakanku, kowannenku! Amma daga baya tabbatacce za ku saurare ni ba kuwa za ku ƙara ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku ba.
Bet jūs no Israēla nama, tā saka Tas Kungs Dievs: noejat, kalpojiet ikviens saviem elkiem! Bet pēclaikā, tad tiešām jūs Mani klausīsiet un vairs neapgānīsiet Manu svēto vārdu ar savām dāvanām un ar saviem elkiem.
40 Gama a kan dutsena mai tsarki, dutse mai tsayi na Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, a can a ƙasar gidan Isra’ila gaba ɗaya za su bauta mini, a can kuwa zan karɓe su. A can zan bukaci hadayunku da sadake sadakenku mafi kyau, tare da dukan tsarkakan hadayunku.
Jo uz Mana svētā kalna, uz Israēla augstā kalna, saka Tas Kungs Dievs, tur Man kalpos viss Israēla nams, visi, kas tanī zemē; tur man pie tiem būs labs prāts, un tur Es prasīšu jūsu cilājamos upurus un jūsu upuru pirmajus, ar visu, ko jūs Man svētījat.
41 Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa’ad da na fitar da ku daga al’ummai na kuma tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, zan kuma nuna kaina mai tsarki a cikinku a idon al’ummai.
Man būs labs prāts pie jums kā pie saldas smaržas, kad Es jūs no tām tautām izvedīšu un jūs sapulcināšu no tām valstīm, kur bijāt izkaisīti, un Es caur jums pagodināšos priekš pagānu acīm.
42 Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na kawo ku cikin ƙasar Isra’ila, ƙasar da na ɗaga hannu na rantse zan ba wa kakanninku.
Un jūs samanīsiet, ka Es esmu Tas Kungs, kad Es jūs ievedīšu Israēla zemē, tai zemē, par ko Es Savu roku esmu pacēlis, to dot jūsu tēviem.
43 A can za ku tuna da halinku da kuma dukan ayyukanku waɗanda kuka ɓata kanku da su, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda mugayen abubuwan da kuka aikata.
Tad jūs tur pieminēsiet savus ceļus un visus savus darbus, ar ko jūs esat apgānījušies, un jums pašiem riebs visa jūsu bezdievība, ko esat darījuši.
44 Za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na yi muku haka saboda sunana ba bisa ga mugayen hanyoyinku da ayyukanku marasa kyau ba, ya gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Tā jūs samanīsiet, ka Es esmu Tas Kungs, kad Es ar jums būšu darījis Sava vārda dēļ, ne pēc jūsu nikniem ceļiem un netikliem darbiem, ak Israēla nams, saka Tas Kungs Dievs.
45 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Un Tā Kunga vārds notika uz mani sacīdams:
46 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka wajen kudu; ka yi wa’azi a kan kudu ka kuma yi annabci a kan kurmin ƙasar kudu.
Cilvēka bērns, griez savu vaigu pret dienvidiem, un lai (tava valoda) pil pret dienvidiem, un sludini pret to mežu dienvidu klajumā.
47 Ka faɗa wa kurmin kudanci, ‘Ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da sa maka wuta, za tă kuwa cinye dukan itatuwanki sarai, da ɗanye da busasshe. Ba za a kashe wutar da take ci ba, kuma kowace fuska a kudu zuwa arewa za tă ƙone.
Un saki uz to mežu dienvidos: klausi Tā Kunga vārdu! Tā saka Tas Kungs Dievs: redzi Es iededzināšu uguni iekš tevis, un tas iekš tevis aprīs visus zaļos kokus un visus sausos kokus; tās varenās liesmas nevarēs izdzēst, un tā sadegs viss, kas ir no dienvidiem līdz ziemeļiem.
48 Kowa zai san cewa Ni Ubangiji ne ya ƙuna ta; ba za a kashe ta ba.’”
Un visa miesa redzēs, ka Es Tas Kungs to esmu iededzinājis; tas netaps izdzēsts.
49 Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Suna zance a kaina cewa, ‘Ba misalai kawai yake yi ba?’”
Un es sacīju: ak Kungs Dievs! Tie par mani saka: vai tas nav līdzības stāstītājs?