< Ezekiyel 20 >

1 A shekara ta bakwai, a wata na biyar a rana ta goma, waɗansu dattawan Isra’ila suka zo don su nemi nufin Ubangiji, suka kuwa zauna a ƙasa a gabana.
Or il arriva en la septième année, au cinquième mois, au dixième jour du mois, que des hommes d’entre les anciens d’Israël vinrent pour consulter le Seigneur, et qu’ils s’assirent devant moi.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
3 “Ɗan mutum, ka yi magana da dattawan Isra’ila ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kun zo ne ku nemi shawarata? Muddin ina raye, ba zan bari ku nemi shawarata ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
Fils d’un homme, parle aux anciens d’Israël, et tu leur diras: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Est-ce pour me consulter que vous êtes venus, vous? Je vis, moi, je ne vous répondrai point, dit le Seigneur Dieu.
4 “Za ka hukunta su? Za ka hukunta su, ɗan mutum? To, sai ka kalubalance su da ayyukan banƙyamar kakanninsu
Si tu les juges, fils d’un homme, si tu les juges, montre leur les abominations de leurs pères.
5 ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na zaɓi Isra’ila, na ɗaga hannuna, na rantse wa zuriyar gidan Yaƙub na kuma bayyana kaina gare su a Masar da hannun da na ɗaga na ce musu, “Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Et tu leur diras: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Au jour où je choisis Israël, et où je levai ma main pour la race de la maison de Jacob, et où je leur apparus dans la terre de l’Egypte, et où je levai ma main pour eux, disant: Je suis le Seigneur votre Dieu;
6 A ranar na yi musu rantsuwa cewa zan fitar da su daga Masar zuwa ƙasar da na samo musu, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe.
En ce jour-là, je levai ma main pour eux, afin de les conduire de la terre d’Egypte dans une terre que je leur avais destinée, où coulent du lait et du miel, et qui est excellente entre toutes les terres.
7 Na kuma ce musu, “Kowannenku ya zubar da mugayen siffofin da kuka kafa idanunku a kai, kuma kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Et je leur dis: Que chacun éloigne les scandales de ses yeux, et ne vous souillez point par les idoles de l’Egypte; je suis le Seigneur votre Dieu.
8 “‘Amma sai suka yi tawaye a kaina ba su kuwa saurare ni ba; ba su zubar da mugayen siffofin da suka kafa idanunsu a kai ba, balle su ƙi gumakan Masar. Saboda haka zan zubo hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a Masar.
Mais ils m’ont irrité, et n’ont pas voulu m’écouler, aucun d’eux n’a rejeté les abominations de leurs yeux, et ils n’ont pas quitté les idoles de l’Egypte; et j’ai dit que je répandrais mon indignation sur eux, et que j’assouvirais ma colère sur eux, au milieu de la terre d’Egypte.
9 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da suka zauna a ciki da kuma a idanun al’ummai da na bayyana kaina ga Isra’ilawa ta wurin fitar da su daga Masar.
Mais j’ai agi à cause de mon nom, afin qu’il ne fût pas violé devant les nations au milieu desquelles ils étaient, et parmi lesquelles je leur ai apparu, afin de les retirer de la terre d’Egypte.
10 Saboda haka na fisshe su daga Masar na kawo su cikin hamada.
Je les ai donc fait sortir de la terre d’Egypte, et je les ai conduits dans le désert.
11 Na ba su ƙa’idodina na kuma sanar musu da dokokina, gama mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu.
Et je leur ai donné mes préceptes, je leur ai fait connaître mes ordonnances, dans lesquelles l’homme qui les accomplira trouvera la vie.
12 Na kuma ba su Asabbataina kamar alama tsakaninmu, domin su san cewa Ni Ubangiji ne yake tsarkake su.
De plus je leur donnai aussi mes sabbats, afin qu’ils fussent un signe entre moi et eux, et qu’ils sussent que je suis le Seigneur qui les sanctifie.
13 “‘Duk da haka mutanen Isra’ila suka yi mini tawaye a cikin hamada. Ba su bi ƙa’idodina ba amma suka ki dokokina, ko da yake mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu, suka ɓata Asabbataina ƙwarai. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma hallaka su a hamada.
Mais la maison d’Israël m’a irrité dans le désert; ils n’ont pas marché dans mes préceptes; ils ont rejeté mes ordonnances dans lesquelles l’homme qui les accomplira trouvera la vie, et mes sabbats, ils les ont violés grièvement: j’ai dit donc que je répandrais ma fureur sur eux dans le désert, et que je les exterminerais.
14 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
Mais j’ai fait autrement à cause de mon nom, afin qu’il ne fût pas violé devant les nations, d’où je les ai retirés en leur propre présence.
15 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu a hamada cewa ba zan kawo su ƙasar da na ba su ba, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe,
Moi donc j’ai levé ma main sur eux dans le désert, pour ne les pas faire entrer dans la terre que je leur avais donnée, où coulent du lait et du miel, la principale de toutes les terres;
16 domin sun ƙi dokokina ba su kuwa bi ƙa’idodina ba suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Gama zukatansu sun fi so su bauta wa gumakansu.
Parce qu’ils ont rejeté mes ordonnances, et qu’ils n’ont pas marché dans mes préceptes, et qu’ils ont violé mes sabbats; car c’est à la suite des idoles que leur cœur allait.
17 Duk da haka na dube su ta tausayi ba zan hallaka su ko in kawo ƙarshensu a hamada ba.
Et mon œil les a épargnés pour ne pas leur ôter la vie, et je ne les ai pas exterminés dans le désert.
18 Na faɗa wa’ya’yansu a hamada, “Kada ku bi farillai kakanninku ko ku kiyaye dokokinsu ko ku ƙazantar da kanku da gumakansu.
Mais j’ai dit à leurs enfants dans la solitude: Ne marchez point dans les préceptes de vos pères, ne gardez point leurs coutumes, et ne vous souillez point par leurs idoles.
19 Ni ne Ubangiji Allahnku; ku bi ƙa’idodina ku kuma kula ku kiyaye dokokina.
Je suis le Seigneur votre Dieu; marchez dans mes préceptes, gardez mes ordonnances et pratiquez-les;
20 Ku kiyaye Asabbataina da tsarki, don su zama alama tsakaninmu. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Allahnku.”
Et mes sabbats, sanctifiez-les, afin qu’ils soient un signe entre moi et vous, et que vous sachiez que moi, je suis le Seigneur votre Dieu.
21 “‘Amma’ya’yan suka yi mini tawaye. Ba su bi ƙa’idodina ba, ba su kula su kiyaye dokokina ba, ko da yake mutumin da ya kiyaye su zai rayu ta wurinsu, suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a hamada.
Mais les enfants m’ont aigri, ils n’ont pas marché dans mes préceptes, et ils n’ont pas gardé mes ordonnances, de manière à accomplir les choses par lesquelles l’homme qui les aura accomplies vivra; et mes sabbats, ils les ont violés; et j’ai menacé de répandre ma fureur sur eux, et d’assouvir ma colère sur eux dans le désert.
22 Amma na janye hannuna, kuma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
Mais j’ai détourné ma main, et j’ai agi à cause de mon nom, afin qu’il ne fût pas violé devant les nations, d’où je les ai retirés sous leurs propres yeux.
23 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu cewa zan watsar da su cikin al’ummai in kuma warwatsa su cikin ƙasashe,
De nouveau j’ai levé ma main sur eux dans la solitude, afin de les disperser parmi les nations et de les jeter au vent dans les divers pays;
24 domin ba su kiyaye dokokina ba amma suka ƙi ƙa’idodina suka kuma ƙazantar da Asabbataina, idanunsu suka yi sha’awar gumakan kakanninsu.
Parce qu’ils n’avaient pas observé mes ordonnances, et qu’ils avaient rejeté mes préceptes, et violé mes sabbats, et que leurs yeux s’étaient portés sur les idoles de leurs pères.
25 Na kuma ba da su ga farillan da ba su da kyau da dokokin da ba za su rayu ta wurinsu ba;
Moi donc aussi je leur ai donné des préceptes qui n’étaient pas bons, et des ordonnances dans lesquelles ils ne trouveront pas la vie.
26 na bari suka ƙazantu ta wurin kyautai, hadayar kowane ɗan fari don in cika su da abin tsoro domin su san cewa ni ne Ubangiji.’
Je les ai souillés dans leurs présents, lorsqu’ils offraient tout ce qui ouvre un sein, pour leurs péchés; et ils sauront que je suis le Seigneur.
27 “Saboda haka, ɗan mutum, ka yi magana da mutanen Isra’ila ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a wannan kuma kakanninku suka saɓe ni ta wurin yashe ni.
C’est pourquoi parle à la maison d’Israël, fils d’un homme, et tu leur diras: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Vos pères m’ont encore outragé en cela, qu’après qu’ils m’avaient dédaigné par leur mépris,
28 Sa’ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su suka kuma ga tudu mai tsawo ko itace mai ganye, a can suka miƙa hadayunsu, suka yi sadakokin da suka tsokane ni na yi fushi, suka miƙa turaren ƙanshinsu suka kuma zuba sadakokinsu na sha.
Et que je les avais fait entrer dans la terre que j’avais juré de leur donner, ils ont vu toute colline élevée et tout arbre touffu, et là ils ont immolé leurs victimes, et là ils m’ont donné un sujet d’irritation par leurs oblations, là ils ont consumé leurs parfums de suavité, et ils ont fait leurs nombreuses libations.
29 Sai na ce musu, Wane ɗakin tsafi kuke tafiya?’” (Ana ce da shi Bama har wa yau.)
Et je leur ai dit: Quel est ce haut lieu où vous allez? et on a appelé son nom Haut lieu jusqu’à ce jour.
30 “Domin haka ka faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa za ku ƙazantar da kanku yadda kakanninku suka yi ne ku yi sha’awar mugayen siffofinsu?
À cause de cela, dis à la maison d’Israël: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Certainement vous vous souillez vous-mêmes dans la voie de vos pères, et vous forniquez à la suite de leurs pierres d’achoppement;
31 Sa’ad da kuka miƙa kyautai naku, hadayar’ya’yanku maza a wuta, kuna cin gaba da ƙazantar da kanku da duka gumakanku har wa yau. Zan bari ku nemi shawarata, ya gidan Isra’ila? Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba zan bari ku nemi shawarata ba.
Et par l’oblation de vos dons, vous vous souillez, lorsque vous faites passer vos enfants au feu, et par toutes vos idoles jusqu’à ce jour; et moi je vous répondrai, maison d’Israël? Je vis, moi, dit le Seigneur Dieu, je ne vous répondrai point.
32 “‘Kukan ce, “Kuna so ku zama kamar sauran al’ummai, kamar sauran mutanen duniya, waɗanda suke bauta wa itace da dutse.” Amma abin da kuke tunani ba zai taɓa faruwa ba.
Et la pensée de votre esprit ne s’accomplira pas, lorsque vous dites: Nous serons comme les nations et comme les familles de la terre, nous adorerons comme eux du bois et de la pierre.
33 Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan yi mulki a kanku da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
Je vis, moi, dit le Seigneur Dieu, avec une main forte, et avec un bras étendu, et dans ma fureur épanchée je régnerai sur vous.
34 Zan fitar da ku daga al’ummai in tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
Et je vous ferai sortir du milieu des peuples, et je vous rassemblerai des pays dans lesquels vous avez été dispersés, avec une main forte, et avec un bras étendu, et dans ma fureur épanchée je régnerai sur vous.
35 Zan kawo ku cikin hamadar al’ummai a can kuwa, fuska da fuska, zan hukunta ku.
Et je vous amènerai dans le désert des peuples, et là j’entrerai en jugement avec vous, face à face.
36 Yadda na hukunta kakanninku a hamadar ƙasar Masar, haka zan hukunta ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Comme j’ai disputé en jugement contre vos pères dans le désert de l’Egypte, ainsi je vous jugerai, dit le Seigneur Dieu.
37 Zan lura da ku yayinda kuke wucewa ƙarƙashin sanda, zan kuma kawo ku cikin daurin alkawari.
Et je vous assujettirai à mon sceptre, et je vous ferai entrer dans les liens de mon alliance.
38 Zan fitar da waɗanda suke mini tayarwa da kuma’yan tawaye. Ko da yake zan fitar da su daga ƙasar da suke zama, duk da haka ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Et je séparerai de vous les transgresseurs et les impies; et je les ferai sortir du pays où ils demeuraient comme étrangers; mais dans la terre d’Israël ils n’entreront pas, et vous saurez que je suis le Seigneur.
39 “‘Game da ku, ya gidan Isra’ila, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tafi ku bauta wa gumakanku, kowannenku! Amma daga baya tabbatacce za ku saurare ni ba kuwa za ku ƙara ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku ba.
Et vous, maison d’Israël, voici ce que dit le Seigneur Dieu: Suivez chacun vos idoles et les servez. Que si en cela même vous ne m’écoutez pas, et que vous souilliez encore mon nom saint par vos présents et par vos idoles,
40 Gama a kan dutsena mai tsarki, dutse mai tsayi na Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, a can a ƙasar gidan Isra’ila gaba ɗaya za su bauta mini, a can kuwa zan karɓe su. A can zan bukaci hadayunku da sadake sadakenku mafi kyau, tare da dukan tsarkakan hadayunku.
Sur ma montagne sainte, sur la montagne élevée d’Israël, dit le Seigneur Dieu, là me servira toute la maison d’Israël; tous, dis-je, me serviront dans la terre en laquelle ils me seront agréables; et là je demanderai vos prémices et vos premières dîmes, dans tout ce que vous me consacrerez.
41 Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa’ad da na fitar da ku daga al’ummai na kuma tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, zan kuma nuna kaina mai tsarki a cikinku a idon al’ummai.
Comme une odeur de suavité je vous recevrai, lorsque je vous aurai retirés d’entre les peuples, et que je vous aurai rassemblés des pays où vous avez été dispersés, et je serai sanctifié parmi vous aux yeux des nations.
42 Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na kawo ku cikin ƙasar Isra’ila, ƙasar da na ɗaga hannu na rantse zan ba wa kakanninku.
Et vous saurez que je suis le Seigneur, lorsque je vous aurai fait rentrer dans la terre d’Israël, dans la terre pour laquelle j’ai levé ma main que je la donnerais à vos pères.
43 A can za ku tuna da halinku da kuma dukan ayyukanku waɗanda kuka ɓata kanku da su, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda mugayen abubuwan da kuka aikata.
Et là vous vous souviendrez de vos voies, et de tous vos crimes dont vous vous êtes souillés; et vous vous déplairez à vous-mêmes à vos propres yeux, à cause de toutes les méchancetés que vous avez commises.
44 Za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na yi muku haka saboda sunana ba bisa ga mugayen hanyoyinku da ayyukanku marasa kyau ba, ya gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Et vous saurez que je suis le Seigneur, lorsque je vous aurai fait du bien à cause de mon nom, et non point selon vos voies mauvaises, ni selon vos crimes détestables, ô maison d’Israël, dit le Seigneur Dieu.
45 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
46 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka wajen kudu; ka yi wa’azi a kan kudu ka kuma yi annabci a kan kurmin ƙasar kudu.
Fils d’un homme, tourne la face contre la voie du midi; et répands tes paroles vers l’Africus, et prophétise à la forêt du champ du midi.
47 Ka faɗa wa kurmin kudanci, ‘Ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da sa maka wuta, za tă kuwa cinye dukan itatuwanki sarai, da ɗanye da busasshe. Ba za a kashe wutar da take ci ba, kuma kowace fuska a kudu zuwa arewa za tă ƙone.
Et tu diras à la forêt du midi: Ecoute la parole du Seigneur; voici ce que dit le Seigneur: Voici que moi j’allumerai en toi un feu, et je brûlerai en toi tout arbre vert et tout arbre aride; la flamme de l’embrasement ne s’éteindra pas; et par elle toute face sera brûlée, depuis le midi jusqu’à l’aquilon.
48 Kowa zai san cewa Ni Ubangiji ne ya ƙuna ta; ba za a kashe ta ba.’”
Et toute chair verra que moi, le Seigneur, j’ai allumé la flamme, et elle ne s’éteindra pas.
49 Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Suna zance a kaina cewa, ‘Ba misalai kawai yake yi ba?’”
Et j’ai dit: Ah! ah! ah! Seigneur Dieu; eux disent de moi: Est-ce qu’il ne parle pas en paraboles, celui-ci?

< Ezekiyel 20 >