< Ezekiyel 20 >

1 A shekara ta bakwai, a wata na biyar a rana ta goma, waɗansu dattawan Isra’ila suka zo don su nemi nufin Ubangiji, suka kuwa zauna a ƙasa a gabana.
La septième année, le dixième jour du cinquième mois, quelques-uns des anciens d'Israël vinrent pour consulter l'Éternel, et ils s'assirent devant moi.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l'Éternel me fut adressée en ces termes:
3 “Ɗan mutum, ka yi magana da dattawan Isra’ila ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kun zo ne ku nemi shawarata? Muddin ina raye, ba zan bari ku nemi shawarata ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
Fils de l'homme, parle aux anciens d'Israël, et dis-leur: Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: C'est pour me consulter que vous êtes venus! Je suis vivant! je ne me laisserai point consulter par vous, dit le Seigneur, l'Éternel.
4 “Za ka hukunta su? Za ka hukunta su, ɗan mutum? To, sai ka kalubalance su da ayyukan banƙyamar kakanninsu
Ne les jugeras-tu pas, fils de l'homme, ne les jugeras-tu pas? Fais-leur connaître les abominations de leurs pères.
5 ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na zaɓi Isra’ila, na ɗaga hannuna, na rantse wa zuriyar gidan Yaƙub na kuma bayyana kaina gare su a Masar da hannun da na ɗaga na ce musu, “Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Et dis-leur: Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Le jour où j'élus Israël, où je levai ma main en faveur de la postérité de la maison de Jacob, où je me fis connaître à eux dans le pays d'Égypte, où je levai ma main pour eux, en disant: Je suis l'Éternel votre Dieu;
6 A ranar na yi musu rantsuwa cewa zan fitar da su daga Masar zuwa ƙasar da na samo musu, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe.
En ce jour-là, je leur promis en levant ma main, que je les ferais sortir du pays d'Égypte, pour les faire entrer dans un pays que j'avais cherché pour eux, pays où coulent le lait et le miel, le plus beau de tous les pays.
7 Na kuma ce musu, “Kowannenku ya zubar da mugayen siffofin da kuka kafa idanunku a kai, kuma kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Et je leur dis: Rejetez, chacun de vous, les abominations objets de vos regards, ne vous souillez pas avec les idoles de l'Égypte; je suis l'Éternel, votre Dieu.
8 “‘Amma sai suka yi tawaye a kaina ba su kuwa saurare ni ba; ba su zubar da mugayen siffofin da suka kafa idanunsu a kai ba, balle su ƙi gumakan Masar. Saboda haka zan zubo hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a Masar.
Mais ils se révoltèrent contre moi, et ne voulurent pas m'écouter; aucun d'eux ne rejeta les abominations qui attiraient ses regards, et n'abandonna les idoles de l'Égypte. Alors je songeai à répandre ma fureur sur eux, et à assouvir contre eux ma colère au milieu du pays d'Égypte.
9 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da suka zauna a ciki da kuma a idanun al’ummai da na bayyana kaina ga Isra’ilawa ta wurin fitar da su daga Masar.
Néanmoins j'ai agi pour l'amour de mon nom, afin qu'il ne fût point profané aux yeux des nations parmi lesquelles ils se trouvaient, et en présence desquelles je m'étais fait connaître à eux, pour les faire sortir du pays d'Égypte.
10 Saboda haka na fisshe su daga Masar na kawo su cikin hamada.
Je les fis donc sortir du pays d'Égypte, et les amenai au désert.
11 Na ba su ƙa’idodina na kuma sanar musu da dokokina, gama mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu.
Je leur donnai mes statuts et leur fis connaître mes lois, que l'homme doit accomplir afin de vivre par elles.
12 Na kuma ba su Asabbataina kamar alama tsakaninmu, domin su san cewa Ni Ubangiji ne yake tsarkake su.
Je leur donnai aussi mes sabbats pour servir de signe entre moi et eux, afin qu'ils connussent que je suis l'Éternel, qui les sanctifie.
13 “‘Duk da haka mutanen Isra’ila suka yi mini tawaye a cikin hamada. Ba su bi ƙa’idodina ba amma suka ki dokokina, ko da yake mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu, suka ɓata Asabbataina ƙwarai. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma hallaka su a hamada.
Mais ceux de la maison d'Israël se révoltèrent contre moi dans le désert; ils ne marchèrent point selon mes statuts et rejetèrent mes lois, que l'homme doit accomplir afin de vivre par elles, et ils profanèrent indignement mes sabbats. C'est pourquoi je songeai à répandre sur eux ma fureur au désert, pour les anéantir.
14 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
Néanmoins j'ai agi pour l'amour de mon nom, afin qu'il ne fût point profané aux yeux des nations, en présence desquelles je les avais fait sortir d'Égypte.
15 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu a hamada cewa ba zan kawo su ƙasar da na ba su ba, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe,
Et même je leur avais promis, en levant ma main dans le désert, que je ne les amènerais point au pays que je leur avais donné, - pays où coulent le lait et le miel, le plus beau de tous les pays, -
16 domin sun ƙi dokokina ba su kuwa bi ƙa’idodina ba suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Gama zukatansu sun fi so su bauta wa gumakansu.
Parce qu'ils avaient rejeté mes lois, qu'ils n'avaient point marché selon mes statuts, et qu'ils avaient profané mes sabbats, car leur cœur marchait après leurs idoles.
17 Duk da haka na dube su ta tausayi ba zan hallaka su ko in kawo ƙarshensu a hamada ba.
Toutefois mon œil les épargna pour ne point les détruire; je ne les exterminai pas entièrement au désert.
18 Na faɗa wa’ya’yansu a hamada, “Kada ku bi farillai kakanninku ko ku kiyaye dokokinsu ko ku ƙazantar da kanku da gumakansu.
Je dis à leurs enfants au désert: Ne marchez pas selon les préceptes de vos pères, n'observez pas leurs mœurs, et ne vous souillez pas avec leurs idoles.
19 Ni ne Ubangiji Allahnku; ku bi ƙa’idodina ku kuma kula ku kiyaye dokokina.
Je suis l'Éternel votre Dieu; marchez selon mes statuts, gardez mes commandements, et mettez-les en pratique.
20 Ku kiyaye Asabbataina da tsarki, don su zama alama tsakaninmu. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Allahnku.”
Sanctifiez mes sabbats, afin qu'ils servent de signe entre moi et vous, et que vous connaissiez que je suis l'Éternel votre Dieu.
21 “‘Amma’ya’yan suka yi mini tawaye. Ba su bi ƙa’idodina ba, ba su kula su kiyaye dokokina ba, ko da yake mutumin da ya kiyaye su zai rayu ta wurinsu, suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a hamada.
Mais les enfants se révoltèrent contre moi; ils ne marchèrent point selon mes statuts; ils n'observèrent pas mes ordonnances et ne mirent point en pratique ces lois, que l'homme doit accomplir afin de vivre par elles, et ils profanèrent mes sabbats. C'est pourquoi je songeai à répandre sur eux ma fureur, et à assouvir contre eux ma colère au désert.
22 Amma na janye hannuna, kuma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
Néanmoins j'ai retiré ma main, et je l'ai fait pour l'amour de mon nom, afin qu'il ne fût point profané aux yeux des nations en présence desquelles je les avais fait sortir.
23 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu cewa zan watsar da su cikin al’ummai in kuma warwatsa su cikin ƙasashe,
Toutefois je leur avais promis, en levant ma main au désert, que je les disperserais parmi les nations et que je les répandrais en divers pays,
24 domin ba su kiyaye dokokina ba amma suka ƙi ƙa’idodina suka kuma ƙazantar da Asabbataina, idanunsu suka yi sha’awar gumakan kakanninsu.
Parce qu'ils n'avaient point observé mes statuts, qu'ils avaient rejeté mes lois, qu'ils avaient profané mes sabbats et que leurs yeux étaient attachés aux idoles de leurs pères.
25 Na kuma ba da su ga farillan da ba su da kyau da dokokin da ba za su rayu ta wurinsu ba;
Aussi leur ai-je donné des statuts qui n'étaient pas bons, et des lois par lesquelles ils ne devaient pas vivre.
26 na bari suka ƙazantu ta wurin kyautai, hadayar kowane ɗan fari don in cika su da abin tsoro domin su san cewa ni ne Ubangiji.’
Je les souillai par leurs offrandes, en ce qu'ils ont fait passer par le feu tous leurs premiers-nés, afin de les mettre en désolation et de leur faire connaître que je suis l'Éternel.
27 “Saboda haka, ɗan mutum, ka yi magana da mutanen Isra’ila ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a wannan kuma kakanninku suka saɓe ni ta wurin yashe ni.
C'est pourquoi, fils de l'homme, parle à la maison d'Israël, et dis-leur: Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Vos pères m'ont outragé en agissant perfidement à mon égard.
28 Sa’ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su suka kuma ga tudu mai tsawo ko itace mai ganye, a can suka miƙa hadayunsu, suka yi sadakokin da suka tsokane ni na yi fushi, suka miƙa turaren ƙanshinsu suka kuma zuba sadakokinsu na sha.
Je les ai fait entrer dans le pays que j'avais promis, en levant la main, de leur donner; mais ils ont regardé toute colline élevée et tout arbre touffu; ils y ont fait leurs sacrifices, ils y ont présenté leurs offrandes qui m'irritaient; ils y ont déposé leurs parfums d'agréable odeur, et y ont fait leurs libations.
29 Sai na ce musu, Wane ɗakin tsafi kuke tafiya?’” (Ana ce da shi Bama har wa yau.)
Et je leur dis: Que signifient ces hauts lieux où vous vous rendez? Et le nom de hauts lieux leur a été donné jusqu'à ce jour.
30 “Domin haka ka faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa za ku ƙazantar da kanku yadda kakanninku suka yi ne ku yi sha’awar mugayen siffofinsu?
C'est pourquoi, dis à la maison d'Israël: Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Ne vous souillez-vous pas dans les voies de vos pères, et ne vous prostituez-vous pas à leurs abominations?
31 Sa’ad da kuka miƙa kyautai naku, hadayar’ya’yanku maza a wuta, kuna cin gaba da ƙazantar da kanku da duka gumakanku har wa yau. Zan bari ku nemi shawarata, ya gidan Isra’ila? Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba zan bari ku nemi shawarata ba.
Quand vous présentez vos offrandes, quand vous faites passer vos enfants par le feu, vous vous souillez avec toutes vos idoles encore aujourd'hui. Et je me laisserais consulter par vous, ô maison d'Israël! Je suis vivant! dit le Seigneur, l'Éternel, je ne me laisserai point consulter par vous!
32 “‘Kukan ce, “Kuna so ku zama kamar sauran al’ummai, kamar sauran mutanen duniya, waɗanda suke bauta wa itace da dutse.” Amma abin da kuke tunani ba zai taɓa faruwa ba.
Rien n'arrivera de ce que vous pensez quand vous dites: Nous voulons être comme les nations et les familles des autres pays, en servant le bois et la pierre.
33 Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan yi mulki a kanku da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
Je suis vivant! dit le Seigneur, l'Éternel, à main forte, à bras étendu, et avec effusion de colère, je régnerai sur vous!
34 Zan fitar da ku daga al’ummai in tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
Je vous ferai sortir d'entre les peuples; je vous rassemblerai des pays dans lesquels vous avez été dispersés, à main forte, à bras étendu et avec effusion de colère.
35 Zan kawo ku cikin hamadar al’ummai a can kuwa, fuska da fuska, zan hukunta ku.
Et je vous amènerai dans le désert des peuples, et là j'entrerai en jugement avec vous, face à face;
36 Yadda na hukunta kakanninku a hamadar ƙasar Masar, haka zan hukunta ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Comme je suis entré en jugement avec vos pères dans le désert du pays d'Égypte, ainsi j'entrerai en jugement avec vous, dit le Seigneur, l'Éternel.
37 Zan lura da ku yayinda kuke wucewa ƙarƙashin sanda, zan kuma kawo ku cikin daurin alkawari.
Puis je vous ferai passer sous la verge, et vous ferai rentrer dans les liens de l'alliance.
38 Zan fitar da waɗanda suke mini tayarwa da kuma’yan tawaye. Ko da yake zan fitar da su daga ƙasar da suke zama, duk da haka ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Je séparerai de vous les rebelles et ceux qui se sont révoltés contre moi; je les ferai sortir du pays où ils séjournent; mais ils n'entreront point sur le sol d'Israël. Ainsi vous saurez que je suis l'Éternel.
39 “‘Game da ku, ya gidan Isra’ila, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tafi ku bauta wa gumakanku, kowannenku! Amma daga baya tabbatacce za ku saurare ni ba kuwa za ku ƙara ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku ba.
Et vous, maison d'Israël, ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Allez servir chacun vos idoles! Mais, après cela, vous m'écouterez et ne profanerez plus le nom de ma sainteté par vos offrandes et par vos idoles.
40 Gama a kan dutsena mai tsarki, dutse mai tsayi na Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, a can a ƙasar gidan Isra’ila gaba ɗaya za su bauta mini, a can kuwa zan karɓe su. A can zan bukaci hadayunku da sadake sadakenku mafi kyau, tare da dukan tsarkakan hadayunku.
Mais sur ma sainte montagne, sur la haute montagne d'Israël, dit le Seigneur, l'Éternel, là toute la maison d'Israël et tout ce qui sera dans le pays me serviront. Là je prendrai plaisir à eux; là je rechercherai vos offrandes, et les prémices de vos dons, dans tout ce que vous me consacrerez.
41 Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa’ad da na fitar da ku daga al’ummai na kuma tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, zan kuma nuna kaina mai tsarki a cikinku a idon al’ummai.
Je prendrai plaisir à vous, comme à un parfum d'agréable odeur, quand je vous aurai fait sortir du milieu des peuples et rassemblés des pays où vous êtes dispersés, et je serai sanctifié par vous aux yeux des nations.
42 Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na kawo ku cikin ƙasar Isra’ila, ƙasar da na ɗaga hannu na rantse zan ba wa kakanninku.
Et vous saurez que je suis l'Éternel, quand je vous aurai fait revenir sur le sol d'Israël, dans le pays que j'avais promis, en levant la main, de donner à vos pères.
43 A can za ku tuna da halinku da kuma dukan ayyukanku waɗanda kuka ɓata kanku da su, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda mugayen abubuwan da kuka aikata.
Là, vous vous souviendrez de vos voies et de toutes vos actions par lesquelles vous vous êtes souillés; vous vous prendrez vous-mêmes en dégoût, à cause de tout ce que vous aurez fait de mal.
44 Za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na yi muku haka saboda sunana ba bisa ga mugayen hanyoyinku da ayyukanku marasa kyau ba, ya gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Et vous saurez que je suis l'Éternel, quand j'agirai avec vous pour l'amour de mon nom, et non pas selon votre conduite mauvaise et vos actions corrompues, ô maison d'Israël! dit le Seigneur, l'Éternel.
45 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l'Éternel me fut adressée en ces mots:
46 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka wajen kudu; ka yi wa’azi a kan kudu ka kuma yi annabci a kan kurmin ƙasar kudu.
Fils de l'homme, tourne ta face du côté de Théman, et prêche vers le midi, prophétise sur la forêt de la campagne du midi.
47 Ka faɗa wa kurmin kudanci, ‘Ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da sa maka wuta, za tă kuwa cinye dukan itatuwanki sarai, da ɗanye da busasshe. Ba za a kashe wutar da take ci ba, kuma kowace fuska a kudu zuwa arewa za tă ƙone.
Dis à la forêt du midi: Écoute la parole de l'Éternel! Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Voici, je vais allumer un feu au-dedans de toi; il dévorera dans ton sein tout arbre vert et tout arbre sec; la flamme embrasée ne s'éteindra point, et toute la surface en sera brûlée du midi au septentrion.
48 Kowa zai san cewa Ni Ubangiji ne ya ƙuna ta; ba za a kashe ta ba.’”
Et toute chair verra que moi, l'Éternel, je l'ai allumée; elle ne s'éteindra point.
49 Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Suna zance a kaina cewa, ‘Ba misalai kawai yake yi ba?’”
Et je dis: Ah! Seigneur, Éternel, ils disent de moi: Cet homme ne fait que parler en énigmes.

< Ezekiyel 20 >