< Ezekiyel 20 >

1 A shekara ta bakwai, a wata na biyar a rana ta goma, waɗansu dattawan Isra’ila suka zo don su nemi nufin Ubangiji, suka kuwa zauna a ƙasa a gabana.
II arriva, dans la septième année, le dixième jour du cinquième mois, que certains d’entre les anciens d’Israël vinrent consulter le Seigneur, et ils s’assirent en face de moi.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée en ces termes:
3 “Ɗan mutum, ka yi magana da dattawan Isra’ila ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kun zo ne ku nemi shawarata? Muddin ina raye, ba zan bari ku nemi shawarata ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
"Fils de l’homme, parle aux anciens d’Israël et dis-leur: Ainsi parle le Seigneur Dieu: C’Est pour me consulter que vous venez? Par ma vie, je ne me laisserai pas consulter par vous, dit le Seigneur Dieu.
4 “Za ka hukunta su? Za ka hukunta su, ɗan mutum? To, sai ka kalubalance su da ayyukan banƙyamar kakanninsu
Veux-tu les juger, fils de l’homme, veux-tu les juger? Fais-leur connaître les abominations de leurs pères.
5 ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na zaɓi Isra’ila, na ɗaga hannuna, na rantse wa zuriyar gidan Yaƙub na kuma bayyana kaina gare su a Masar da hannun da na ɗaga na ce musu, “Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Tu leur diras donc: Ainsi parle le Seigneur Dieu: Le jour où j’ai fait choix d’Israël, où j’ai levé la main pour la postérité de la maison de Jacob, où je me suis révélé à eux au pays d’Egypte, où j’ai levé la main pour eux en disant: Je suis l’Eternel votre Dieu,
6 A ranar na yi musu rantsuwa cewa zan fitar da su daga Masar zuwa ƙasar da na samo musu, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe.
ce jour-là, je leur ai juré de leur faire quitter le pays d’Egypte pour une contrée que j’avais explorée à leur intention, où ruissellent le lait et le miel, et qui est un joyau entre tous les pays.
7 Na kuma ce musu, “Kowannenku ya zubar da mugayen siffofin da kuka kafa idanunku a kai, kuma kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Et je leur ai dit: "Que chacun de vous rejette au loin les abominations qui sont sous ses yeux! Ne vous souillez pas avec les idoles infâmes de l’Egypte, je suis l’Eternel votre Dieu."
8 “‘Amma sai suka yi tawaye a kaina ba su kuwa saurare ni ba; ba su zubar da mugayen siffofin da suka kafa idanunsu a kai ba, balle su ƙi gumakan Masar. Saboda haka zan zubo hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a Masar.
Mais ils se sont mutinés contre moi, ils n’ont pas consenti à m’écouter; ils n’ont pas rejeté les abjections dont ils étaient témoins, ils n’ont pas abandonné les idoles de l’Egypte, et je songeais à épancher mon courroux sur eux, à assouvir sur eux ma colère au milieu du pays d’Egypte.
9 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da suka zauna a ciki da kuma a idanun al’ummai da na bayyana kaina ga Isra’ilawa ta wurin fitar da su daga Masar.
Mais j’agis en considération de mon nom, pour ne pas le profaner aux yeux des nations au milieu desquelles ils se trouvaient et à la vue desquelles je m’étais révélé à eux pour les faire sortir du pays d’Egypte.
10 Saboda haka na fisshe su daga Masar na kawo su cikin hamada.
Je les tirai donc du pays d’Egypte et je les amenai au désert.
11 Na ba su ƙa’idodina na kuma sanar musu da dokokina, gama mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu.
Je leur donnai mes lois et leur fis connaître mes règlements, que l’homme doit accomplir pour assurer sa vie.
12 Na kuma ba su Asabbataina kamar alama tsakaninmu, domin su san cewa Ni Ubangiji ne yake tsarkake su.
Je leur donnai aussi mes sabbats, qui devaient être un symbole entre moi et eux, pour qu’on sût que c’est moi, l’Eternel, qui les sanctifie.
13 “‘Duk da haka mutanen Isra’ila suka yi mini tawaye a cikin hamada. Ba su bi ƙa’idodina ba amma suka ki dokokina, ko da yake mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu, suka ɓata Asabbataina ƙwarai. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma hallaka su a hamada.
Mais la maison d’Israël s’est révoltée contre moi dans le désert; ils n’ont pas suivi mes lois, ils ont méprisé mes règlements, que l’homme doit accomplir pour vivre, ils ont profané à l’excès mes sabbats, et je songeai à épancher mon courroux sur eux dans le désert pour les anéantir.
14 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
Mais j’agis en considération de mon nom, pour ne pas le profaner aux yeux des nations à la vue desquelles je les avais fait sortir.
15 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu a hamada cewa ba zan kawo su ƙasar da na ba su ba, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe,
Aussi bien, je jurai contre eux au désert, de ne pas les amener au pays que je leur destinais, ruisselant de lait et de miel, qui est un joyau entre tous les pays,
16 domin sun ƙi dokokina ba su kuwa bi ƙa’idodina ba suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Gama zukatansu sun fi so su bauta wa gumakansu.
parce qu’ils avaient méprisé mes règlements, refusé de suivre mes lois et profané mes sabbats, leur coeur n’étant épris que de leurs viles idoles.
17 Duk da haka na dube su ta tausayi ba zan hallaka su ko in kawo ƙarshensu a hamada ba.
Mais mon oeil eut trop pitié d’eux pour les détruire et je ne les ai pas réduits à néant dans le désert.
18 Na faɗa wa’ya’yansu a hamada, “Kada ku bi farillai kakanninku ko ku kiyaye dokokinsu ko ku ƙazantar da kanku da gumakansu.
Et je dis à leurs enfants dans le désert: "Ne suivez point les errements de vos pères, n’observez pas leurs coutumes et ne vous souillez point par leurs idoles.
19 Ni ne Ubangiji Allahnku; ku bi ƙa’idodina ku kuma kula ku kiyaye dokokina.
Je suis l’Eternel, votre Dieu, suivez mes lois, observez mes règlements et exécutez-les.
20 Ku kiyaye Asabbataina da tsarki, don su zama alama tsakaninmu. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Allahnku.”
Sanctifiez mes sabbats; qu’ils soient un symbole entre moi et vous, pour qu’on sache que je suis l’Eternel, votre Dieu.
21 “‘Amma’ya’yan suka yi mini tawaye. Ba su bi ƙa’idodina ba, ba su kula su kiyaye dokokina ba, ko da yake mutumin da ya kiyaye su zai rayu ta wurinsu, suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a hamada.
Et les enfants se sont révoltés contre moi ils n’ont pas suivi mes lois, ils n’ont pas respecté, pour les accomplir, mes règlements que l’homme doit accomplir pour vivre; ils ont profané mes sabbats, et je songeai à épancher mon courroux sur eux, à assouvir sur eux ma colère dans le désert.
22 Amma na janye hannuna, kuma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
Mais je retins ma main et j’agis en considération de mon nom, pour ne pas le profaner aux yeux des nations à la vue desquelles je les avais fait sortir.
23 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu cewa zan watsar da su cikin al’ummai in kuma warwatsa su cikin ƙasashe,
Mais j’ai aussi juré contre eux dans le désert, de les disperser parmi les nations et de les disséminer dans les pays,
24 domin ba su kiyaye dokokina ba amma suka ƙi ƙa’idodina suka kuma ƙazantar da Asabbataina, idanunsu suka yi sha’awar gumakan kakanninsu.
parce qu’ils n’ont pas accompli mes règlements, et qu’ils ont méprisé mes lois, profané mes sabbats, et que leurs yeux ont été épris des idoles de leurs pères.
25 Na kuma ba da su ga farillan da ba su da kyau da dokokin da ba za su rayu ta wurinsu ba;
Mais en revanche, moi je leur ai donné des lois malheureuses et des règlements non susceptibles de les faire vivre.
26 na bari suka ƙazantu ta wurin kyautai, hadayar kowane ɗan fari don in cika su da abin tsoro domin su san cewa ni ne Ubangiji.’
Je les ai rendus impurs par leurs offrandes, en ce qu’ils faisaient passer par le feu tout premier-né, de manière à les terroriser, afin qu’ils connussent que je suis l’Eternel.
27 “Saboda haka, ɗan mutum, ka yi magana da mutanen Isra’ila ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a wannan kuma kakanninku suka saɓe ni ta wurin yashe ni.
C’Est pourquoi, parle à la maison d’Israël, fils de l’homme, et dis-leur: Ainsi parle le Seigneur Dieu: Encore en cela vos pères m’ont outragé, en commettant une infidélité à mon égard.
28 Sa’ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su suka kuma ga tudu mai tsawo ko itace mai ganye, a can suka miƙa hadayunsu, suka yi sadakokin da suka tsokane ni na yi fushi, suka miƙa turaren ƙanshinsu suka kuma zuba sadakokinsu na sha.
Je les avais amenés au pays que j’avais juré de leur donner; et eux, dès qu’ils aperçurent toute colline élevée et tout arbre touffu, ils y ont immolé leurs sacrifices, déposé leurs odieuses offrandes, apporté leurs parfums voluptueux et répandu leurs libations.
29 Sai na ce musu, Wane ɗakin tsafi kuke tafiya?’” (Ana ce da shi Bama har wa yau.)
Et je leur ai dit: Qu’est-ce que ce haut lieu où vous venez vous réunir? (Et on l’a désigné du nom de Bama, jusqu’à ce jour.)
30 “Domin haka ka faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa za ku ƙazantar da kanku yadda kakanninku suka yi ne ku yi sha’awar mugayen siffofinsu?
C’Est pourquoi dis à la maison d’Israël: Ainsi parle le Seigneur Dieu: Quoi! Vous vous rendriez impurs comme ont fait vos pères et vous vous prostitueriez à leurs idoles abjectes!
31 Sa’ad da kuka miƙa kyautai naku, hadayar’ya’yanku maza a wuta, kuna cin gaba da ƙazantar da kanku da duka gumakanku har wa yau. Zan bari ku nemi shawarata, ya gidan Isra’ila? Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba zan bari ku nemi shawarata ba.
Oui, en apportant vos offrandes, en faisant passer vos enfants par le feu, vous vous souillez par toutes vos idoles jusqu’à ce jour, et moi, je me laisserais consulter par vous, maison d’Israël! Par ma vie, dit le Seigneur Dieu, je ne me laisserai pas consulter par vous!
32 “‘Kukan ce, “Kuna so ku zama kamar sauran al’ummai, kamar sauran mutanen duniya, waɗanda suke bauta wa itace da dutse.” Amma abin da kuke tunani ba zai taɓa faruwa ba.
Ce qui vous monte en l’esprit ne se réalisera pas, lorsque vous dites: "Devenons comme les nations, comme les familles des autres pays pour adorer le bois et la pierre!"
33 Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan yi mulki a kanku da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
Par ma vie, dit le Seigneur Dieu, je jure que d’une main puissante et d’un bras étendu et d’un courroux débordant, je me comporterai en roi à votre égard!
34 Zan fitar da ku daga al’ummai in tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
Je vous ferai sortir d’entre les peuples et je vous rassemblerai des pays où vous avez été dispersés, avec une main puissante, avec un bras étendu et avec un courroux déchaîné.
35 Zan kawo ku cikin hamadar al’ummai a can kuwa, fuska da fuska, zan hukunta ku.
Et je vous amènerai au désert des peuples, et je vous demanderai des comptes, là, face à face.
36 Yadda na hukunta kakanninku a hamadar ƙasar Masar, haka zan hukunta ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Comme j’ai demandé des comptes à vos pères dans le désert du pays d’Egypte, ainsi je vous demanderai des comptes à vous, dit le Seigneur Dieu.
37 Zan lura da ku yayinda kuke wucewa ƙarƙashin sanda, zan kuma kawo ku cikin daurin alkawari.
Et je vous ferai passer sous la verge, et je vous engagerai dans les liens de l’alliance.
38 Zan fitar da waɗanda suke mini tayarwa da kuma’yan tawaye. Ko da yake zan fitar da su daga ƙasar da suke zama, duk da haka ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Et je trierai parmi vous ceux qui se révoltent et pèchent contre moi, je les ferai sortir du pays où ils séjournent, et ils ne viendront pas au pays d’Israël, et vous saurez que je suis l’Eternel.
39 “‘Game da ku, ya gidan Isra’ila, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tafi ku bauta wa gumakanku, kowannenku! Amma daga baya tabbatacce za ku saurare ni ba kuwa za ku ƙara ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku ba.
Pour vous, maison d’Israël, ainsi parle le Seigneur Dieu, que chacun aille donc adorer ses idoles, et après cela on verra si vous ne m’écoutez pas; vous ne profanerez plus mon saint nom par vos offrandes et vos idoles.
40 Gama a kan dutsena mai tsarki, dutse mai tsayi na Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, a can a ƙasar gidan Isra’ila gaba ɗaya za su bauta mini, a can kuwa zan karɓe su. A can zan bukaci hadayunku da sadake sadakenku mafi kyau, tare da dukan tsarkakan hadayunku.
Car c’est sur ma montagne sainte, sur la montagne élevée d’Israël, dit le Seigneur Dieu, c’est là que m’adorera la maison d’Israël tout entière, dans le pays. Là je les agréerai, et là je rechercherai vos prélèvements et les prémices de vos dons, avec toutes vos choses saintes.
41 Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa’ad da na fitar da ku daga al’ummai na kuma tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, zan kuma nuna kaina mai tsarki a cikinku a idon al’ummai.
Grâce à un parfum agréable, je vous accueillerai avec bienveillance, quand je vous aurai fait sortir du sein des peuples, rassemblés des pays où vous avez été dispersés, et je me sanctifierai par vous aux yeux des nations.
42 Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na kawo ku cikin ƙasar Isra’ila, ƙasar da na ɗaga hannu na rantse zan ba wa kakanninku.
Et vous saurez que je suis l’Eternel, quand je vous aurai menés au pays d’Israël, sur la terre que j’ai juré de donner à vos pères.
43 A can za ku tuna da halinku da kuma dukan ayyukanku waɗanda kuka ɓata kanku da su, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda mugayen abubuwan da kuka aikata.
Là, vous vous souviendrez de vos voies et de vos actes par lesquels vous vous êtes souillés, et vous aurez du dégoût pour vous-mêmes à cause de tous les forfaits que vous avez commis.
44 Za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na yi muku haka saboda sunana ba bisa ga mugayen hanyoyinku da ayyukanku marasa kyau ba, ya gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Et vous saurez que je suis l’Eternel, lorsque j’en userai avec vous par égard pour mon nom, non selon vos voies, qui sont mauvaises et selon vos actes dépravés, maison d’Israël, dit le Seigneur Dieu."
45 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
46 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka wajen kudu; ka yi wa’azi a kan kudu ka kuma yi annabci a kan kurmin ƙasar kudu.
"Fils de l’homme, tourne ta face dans la direction méridionale, prêche contre le Sud et prophétise contre la forêt de la campagne du Midi.
47 Ka faɗa wa kurmin kudanci, ‘Ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da sa maka wuta, za tă kuwa cinye dukan itatuwanki sarai, da ɗanye da busasshe. Ba za a kashe wutar da take ci ba, kuma kowace fuska a kudu zuwa arewa za tă ƙone.
Tu diras à la forêt du Sud: "Ecoute la parole du Seigneur: Ainsi parle le Seigneur Dieu: Je vais allumer en toi un feu qui te dévorera tous tes arbres verts et tous tes arbres secs; elle ne s’éteindra pas, la flamme flambante, tous les visages s’y brûleront du Sud jusqu’au Nord.
48 Kowa zai san cewa Ni Ubangiji ne ya ƙuna ta; ba za a kashe ta ba.’”
Et toute chair verra que moi, l’Eternel, je l’ai allumée; elle ne s’éteindra pas.
49 Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Suna zance a kaina cewa, ‘Ba misalai kawai yake yi ba?’”
Et je dis: "Ah! Seigneur Dieu, ils me disent, eux: Oh! C’Est un conteur d’allégories!"

< Ezekiyel 20 >