< Ezekiyel 20 >

1 A shekara ta bakwai, a wata na biyar a rana ta goma, waɗansu dattawan Isra’ila suka zo don su nemi nufin Ubangiji, suka kuwa zauna a ƙasa a gabana.
Almost seven years [King Jehoiachin and the rest of us had been captured and taken to Babylonia], on the tenth day of the fifth [of that year], some Israeli elders came to me to [if I had a message for them] from Yahweh.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then Yahweh gave me a message. [He said, ]
3 “Ɗan mutum, ka yi magana da dattawan Isra’ila ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kun zo ne ku nemi shawarata? Muddin ina raye, ba zan bari ku nemi shawarata ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
“You human, speak to the Israeli elders and say to them, ‘This is what Yahweh the Lord says: [say that] you have come to ask if there is any message from me [RHQ], but [as surely] as I am alive, I will [answer you if] you ask [to tell you] anything.’
4 “Za ka hukunta su? Za ka hukunta su, ɗan mutum? To, sai ka kalubalance su da ayyukan banƙyamar kakanninsu
If you are [RHQ] willing to warn them, remind them of the detestable things that their ancestors did.
5 ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na zaɓi Isra’ila, na ɗaga hannuna, na rantse wa zuriyar gidan Yaƙub na kuma bayyana kaina gare su a Masar da hannun da na ɗaga na ce musu, “Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Then say to them, ‘On the day that I chose [you] Israeli [to belong to me], with my hand lifted up, I made a solemn promise to your [while they were still] in Egypt. I said to them, “I am Yahweh, your God.
6 A ranar na yi musu rantsuwa cewa zan fitar da su daga Masar zuwa ƙasar da na samo musu, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe.
I will bring you out of Egypt and lead you to a land that I have chosen for you. It is a very fertile [IDM] and (very beautiful/more beautiful than any other) land.
7 Na kuma ce musu, “Kowannenku ya zubar da mugayen siffofin da kuka kafa idanunku a kai, kuma kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Each of you must get rid of the disgusting idols that you loved [IDM], and do not defile yourselves [worshiping] those [that you saw] in Egypt. I, Yahweh your God, [am saying this to you].”’
8 “‘Amma sai suka yi tawaye a kaina ba su kuwa saurare ni ba; ba su zubar da mugayen siffofin da suka kafa idanunsu a kai ba, balle su ƙi gumakan Masar. Saboda haka zan zubo hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a Masar.
But they rebelled against me. They would not pay attention to me. They did not get rid of the disgusting idols they loved, and they did not reject those [that they saw] in Egypt. So because I was angry with them, I said that I would punish [MTY] them in Egypt.
9 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da suka zauna a ciki da kuma a idanun al’ummai da na bayyana kaina ga Isra’ilawa ta wurin fitar da su daga Masar.
But for the sake of my own reputation, I decided to do something in order that I would not be dishonored by the people of the nations who would see it when I brought my people out of Egypt.
10 Saboda haka na fisshe su daga Masar na kawo su cikin hamada.
Therefore I led them out of Egypt and brought them into the desert.
11 Na ba su ƙa’idodina na kuma sanar musu da dokokina, gama mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu.
I gave them [all] my laws and decrees [DOU], in order that they would obey them, and as a result they would live [for a long time].
12 Na kuma ba su Asabbataina kamar alama tsakaninmu, domin su san cewa Ni Ubangiji ne yake tsarkake su.
Also, I established the Sabbath/rest days to be a symbol between us to show that I, Yahweh, had caused them to be set [from the other nations].
13 “‘Duk da haka mutanen Isra’ila suka yi mini tawaye a cikin hamada. Ba su bi ƙa’idodina ba amma suka ki dokokina, ko da yake mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu, suka ɓata Asabbataina ƙwarai. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma hallaka su a hamada.
But the Israeli people rebelled against me in the desert. They did not obey my commands [DOU]; they rejected them, even though they tell people who obey them that they will live [for a long time], and they profaned the Sabbath days. So I said that I would get rid of them in the desert, and that would show that I was very angry with them.
14 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
But [again], for the sake of my own reputation, I decided to do something else in order that I would not be dishonored/despised by [the people of] the nations who had seen me bring my people out of Egypt.
15 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu a hamada cewa ba zan kawo su ƙasar da na ba su ba, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe,
I lifted up my hand and solemnly declared to them in the desert that I would not take them into the land that [had promised to] give them, a land that was very fertile [IDM] and (very beautiful/more beautiful than any other) land.
16 domin sun ƙi dokokina ba su kuwa bi ƙa’idodina ba suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Gama zukatansu sun fi so su bauta wa gumakansu.
The reason that I promised that was because they rejected and disobeyed all my laws [DOU] and (desecrated/refused to rest on) the Sabbath days. [They did that] because they [SYN] were devoted [worshiping] their idols.
17 Duk da haka na dube su ta tausayi ba zan hallaka su ko in kawo ƙarshensu a hamada ba.
But, I still pitied them and did not get rid of [all of] them in the desert.
18 Na faɗa wa’ya’yansu a hamada, “Kada ku bi farillai kakanninku ko ku kiyaye dokokinsu ko ku ƙazantar da kanku da gumakansu.
I said to their children, ‘Do not do the things that your parents continually did, or defile yourselves [worshiping] their idols.
19 Ni ne Ubangiji Allahnku; ku bi ƙa’idodina ku kuma kula ku kiyaye dokokina.
I am Yahweh your God. Carefully obey [DOU] my laws and commands.
20 Ku kiyaye Asabbataina da tsarki, don su zama alama tsakaninmu. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Allahnku.”
Respect my Sabbath days, in order that by doing that [PRS], it will remind you that you belong to me, Yahweh your God.’
21 “‘Amma’ya’yan suka yi mini tawaye. Ba su bi ƙa’idodina ba, ba su kula su kiyaye dokokina ba, ko da yake mutumin da ya kiyaye su zai rayu ta wurinsu, suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a hamada.
But their children [also] rebelled against me. They did not carefully obey my laws [DOU], [even though] the people who obey them will live [for a long time]; and they profaned the Sabbath days. So again I said that by getting rid of them in the desert, I would show that I was very angry with them.
22 Amma na janye hannuna, kuma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
But I did not do that [IDM]. [Again, ] for the sake of my own reputation, I [decided to] do something in order that I would not be dishonored/despised by [the people of] the nations who had seen it when I brought my people out [of Egypt].
23 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu cewa zan watsar da su cikin al’ummai in kuma warwatsa su cikin ƙasashe,
I lifted up my hand and solemnly declared to them in the desert that I would cause them to be scattered among [many] nations [DOU],
24 domin ba su kiyaye dokokina ba amma suka ƙi ƙa’idodina suka kuma ƙazantar da Asabbataina, idanunsu suka yi sha’awar gumakan kakanninsu.
because they had rejected and disobeyed all my laws [DOU] and desecrated the Sabbath days, and they had eagerly [to worship] the idols that their [had worshiped].
25 Na kuma ba da su ga farillan da ba su da kyau da dokokin da ba za su rayu ta wurinsu ba;
I also allowed them to obey laws that were not good, and laws that would not enable them to live [a long time if they obeyed them].
26 na bari suka ƙazantu ta wurin kyautai, hadayar kowane ɗan fari don in cika su da abin tsoro domin su san cewa ni ne Ubangiji.’
I allowed them to become unacceptable to me by their sacrificing their firstborn children in the fire. I did that in order that they would be horrified, and in order that they would know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].
27 “Saboda haka, ɗan mutum, ka yi magana da mutanen Isra’ila ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a wannan kuma kakanninku suka saɓe ni ta wurin yashe ni.
Therefore, you human, speak to the Israeli people. Say this to them, ‘This is what Yahweh the Lord says [to you]: This is one way that your ancestors dishonored me by turning away from me.
28 Sa’ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su suka kuma ga tudu mai tsawo ko itace mai ganye, a can suka miƙa hadayunsu, suka yi sadakokin da suka tsokane ni na yi fushi, suka miƙa turaren ƙanshinsu suka kuma zuba sadakokinsu na sha.
After I brought them into the land that I had solemnly promised to give to them, every time that they saw a high hill or a [big] green tree, they offered [to idols] there. They made offerings to them, and that caused me to become angry. They presented to those idols their fragrant burning incense, and poured out wine offerings to them.
29 Sai na ce musu, Wane ɗakin tsafi kuke tafiya?’” (Ana ce da shi Bama har wa yau.)
[Then] I asked them, “Who [RHQ] [told you to worship at] a shrine like this, here on this hilltop?” So they are still called “hilltop shrines”.’
30 “Domin haka ka faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa za ku ƙazantar da kanku yadda kakanninku suka yi ne ku yi sha’awar mugayen siffofinsu?
Therefore, say this to the Israeli people [MTY]: 'This is what Yahweh the Lord says: “You are going to [RHQ] defile yourselves like your ancestors did by strongly [to worship] their disgusting [statues of idols].
31 Sa’ad da kuka miƙa kyautai naku, hadayar’ya’yanku maza a wuta, kuna cin gaba da ƙazantar da kanku da duka gumakanku har wa yau. Zan bari ku nemi shawarata, ya gidan Isra’ila? Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba zan bari ku nemi shawarata ba.
When you sacrifice your children in the fire, you are still continuing to make yourselves unacceptable to me [worshiping] your many idols. You Israeli people, should I allow you to [what I want you to do]? I, Yahweh the Lord, say that [as surely] as I am alive, [I will not answer] if you inquire.'
32 “‘Kukan ce, “Kuna so ku zama kamar sauran al’ummai, kamar sauran mutanen duniya, waɗanda suke bauta wa itace da dutse.” Amma abin da kuke tunani ba zai taɓa faruwa ba.
You say, ‘We want to be like the [other] nations, like the [other] people-groups in the world. We want to [idols made of] wood and [like they do].’ But what you want will never happen.
33 Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan yi mulki a kanku da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
[I], Yahweh your Lord, say that [as surely] as I am alive, I will use my great power [DOU, MTY] to rule over you, and show that I am angry with you.
34 Zan fitar da ku daga al’ummai in tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
With my great power I will gather you from the places to which you have been scattered,
35 Zan kawo ku cikin hamadar al’ummai a can kuwa, fuska da fuska, zan hukunta ku.
and I will bring you to a [that is surrounded] by [other] nations. There, while I am looking at you, I will judge you.
36 Yadda na hukunta kakanninku a hamadar ƙasar Masar, haka zan hukunta ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
I will punish you, like I punished your ancestors in the desert near Egypt.
37 Zan lura da ku yayinda kuke wucewa ƙarƙashin sanda, zan kuma kawo ku cikin daurin alkawari.
I will count you [MTY] as you walk by, and I will force you to obey the agreement that I made with you.
38 Zan fitar da waɗanda suke mini tayarwa da kuma’yan tawaye. Ko da yake zan fitar da su daga ƙasar da suke zama, duk da haka ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
I will get rid of those people among you who rebel [DOU] against me. Although I will bring them out [Babylonia], where they are now living, they will not enter Israel. Then you will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].
39 “‘Game da ku, ya gidan Isra’ila, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tafi ku bauta wa gumakanku, kowannenku! Amma daga baya tabbatacce za ku saurare ni ba kuwa za ku ƙara ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku ba.
As for you Israeli people [MTY], this is what [I], Yahweh the Lord, say: 'Go and worship your idols now [IRO], each of you. But [afterwards], you will [surely] heed me and no longer dishonor me [MTY] by taking gifts to your idols.
40 Gama a kan dutsena mai tsarki, dutse mai tsayi na Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, a can a ƙasar gidan Isra’ila gaba ɗaya za su bauta mini, a can kuwa zan karɓe su. A can zan bukaci hadayunku da sadake sadakenku mafi kyau, tare da dukan tsarkakan hadayunku.
[I], Yahweh your Lord, declare that there on my sacred hill, [Zion], that high hill in Israel, you will bring gifts to me, and I will accept them. I will require you to bring to me gifts and offerings there, and your sacrifices that are dedicated to me.
41 Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa’ad da na fitar da ku daga al’ummai na kuma tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, zan kuma nuna kaina mai tsarki a cikinku a idon al’ummai.
When I bring you out from the [other] nations [DOU] to which you have been scattered, I will accept [as though you were] fragrant incense. By doing that, I will show the people of other nations that I have set you apart to belong to me.
42 Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na kawo ku cikin ƙasar Isra’ila, ƙasar da na ɗaga hannu na rantse zan ba wa kakanninku.
Then, when I bring you into the land of Israel, the land that I solemnly promised with my hand lifted up that I would give to your ancestors, you will know that I, Yahweh, [have done it].
43 A can za ku tuna da halinku da kuma dukan ayyukanku waɗanda kuka ɓata kanku da su, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda mugayen abubuwan da kuka aikata.
And [in Israel] you will remember how you conducted your lives [previously, you will remember] the actions that caused you to become unacceptable to me, and you will hate/despise yourselves for all the evil things that you have done.
44 Za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na yi muku haka saboda sunana ba bisa ga mugayen hanyoyinku da ayyukanku marasa kyau ba, ya gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
When I act toward you Israeli people to protect my reputation, and not [just] because of your evil deeds and corrupt behavior, you Israeli people will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].' That is what Yahweh the Lord declares.”
45 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Yahweh gave me another message. He said,
46 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka wajen kudu; ka yi wa’azi a kan kudu ka kuma yi annabci a kan kurmin ƙasar kudu.
“You human, turn toward the south. Preach about what will happen to that dry land, to the forest there.
47 Ka faɗa wa kurmin kudanci, ‘Ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da sa maka wuta, za tă kuwa cinye dukan itatuwanki sarai, da ɗanye da busasshe. Ba za a kashe wutar da take ci ba, kuma kowace fuska a kudu zuwa arewa za tă ƙone.
Say to the forest in the [part of Israel]: 'Listen to this message that Yahweh the Lord is saying [about you]: “I am about to start a fire in your midst, and it will burn up all your trees, [both] the green trees and the withered/dry trees. Nothing will extinguish the blazing flames. And the fire will scorch the faces of everyone [who lives] in that area, from the south to the north.
48 Kowa zai san cewa Ni Ubangiji ne ya ƙuna ta; ba za a kashe ta ba.’”
Everyone will see that it is I, Yahweh, who have lit this fire, and no one will [be able to] put it out.” '”
49 Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Suna zance a kaina cewa, ‘Ba misalai kawai yake yi ba?’”
Then I said, “Yahweh, my Lord, [when I tell things like this to people, they do not believe me]. They say about me, ‘He is only telling parables.’”

< Ezekiyel 20 >